《HASEENAH》Page 3&4
Advertisement
🌸 *HASEENAH*🌸
story nd written
by👇🏻
Aysher Abbakar (Meerah)
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
#
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-08144932303
follow me on wattpad @Aysherabbakar
*long live pml*
*3-4*
cak Haseenah ta tsaya ta kasa gaba ta kasa baya, tsawar da mommy ta 'kara mata ne ya sata tsugunawa a wajan jikinta na rawa, dubanta Mommy ta sake yi tace " menene a hanunki nace?"
cikin rawar murya ta bata amsa da " kayan umma na ne na kai wajan tela aka gyara mata"
dariya mommy ta saki sannan tace"kice paci kika kai wa tsohuwarki mana, tashi kije da nayi tunanin maula kikaje ai"
wani ajiyar zuciya Haseenah ta saki sannan ta tashi da sauri ta nufa cikin gida. da sallama ta shiga nan ta tarar da ummanta zaune yanda ta barta, zama tayi a gefenta sannan ta dubi Umma tace " gashi ma yaya Haseen ya biya kud'in makarantar"
shuru tayi sannan ta dubi ledar hanunta a hankali tace " wannan fa?"
sai a lokacin ta tuna da ledar da ta shigo dashi, janyo wa tayi ta bud'e nan ta fara ciro kayan ciki, school uniform ne set biyu sai na islamiya shima biyu, sai socks dozen d'aya sai turare da sauran tarkacen kayana makeup da sabon sneakers wanda suke amfani da shi a school sai flat shoe da bathmilk, bayan tagama ciro kayan ne kuma 'karamin envelop ya fad'o, sa hannu tayi ta 'dauka ta fara bud'ewa a hankali.
kud'i ne a ciki 'yan dubu 'da'ddaya guda goma, da sauri ta duba Ummanta sannan tace" Umma harda kud'i fa aciki, a mayar mishi kawai ko Ummah?"
ta 'karasa maganar cike da damuwa.
dubanta Umma tayi sannan tace"ke kika rok'eshi?"
Advertisement
da sauri ta girgiza kai alamar a.a, gyad'a kai Umma tayi sannan tace" to shi yaga dama kuma ba a mayar da hanun kyauta baya, ki adana kud'in sekiyi hidimar makaranta dashi.
batace komai ba ta tattara kayan ta mayar leda sannan ta samu waje ta adana kud'in.
sallaman da sukaji ne ya katse shurun da sukayi, ko bata tanbaya ba tasan Abban tane, sunkuyar da kai tayi ta gaida shi, murmushi ya saki mata sannan ya k'araso ciki ya zauna bakin gadon, duban Umma yayi sannan yace " Maryama ya jikin naki?"
da 'kyar ta iya amsawa saboda yanda takeji numfashin ta na fita sama-sama, hankalinshi ne ya tashi ganin yanda take mayar da numfashi, kallon Haseenah yayi yace " Uwata me yasa baki sameni kin fad'amun ba, kina ganin yanda take wahala amma kikayi shuru?"
sunkuyar da kai tayi dan in tayi yunk'urin sanar mishi ma to a ina zata ganshi? Mommy ma bazata barta ma, sedai ta bita da tsinuwa da kuma zagi.
sanin halin Mommy yasa shi basar da maganar yace su shirya su sameshi a mota su wuce asibiti.
yana gama fad'in haka ya fice, dai dai fita daga side d'insu Haseenah sukayi kici6is da Mommy, dubanshi tayi tace" uwar me ka shiga yi wajanta?"
cikin rawar murya yace" ni ba d'akinta naje ba, warin 'kauri naji nayi tunanin metre ne sekuma naga ba nan bane"
girgiza kai tayi ta wuce wajanta ba tare da ta sake mishi magana ba.
ba 6ata lokaci suka tarar dashi a mota, suna shiga da sauri ya figesu gudun kar Mommy ta le'ko ta gansu, kai tsaye Apple Clinic suka wuce, da yake asibitin na abokin shi ne ba 6ata lokaci aka kar6esu, kwantar da ita akayi sannan aka fara duba ta, test d'in farko da aka mata aka gano tana d'auke da cikin wata biyu, sedai damuwa da zama da yunwa ya sa ulcer ya mata mummunan kamu wanda yake baraza ga cikin jikinta.
Advertisement
taimakon gaggawa aka fara bata, sannan aka d'aura mata drip, aka had'a mata da allurai da magunguna.
likita ne ya lek'o yace a taho mata da abinci mai ruwa wanda zata iya ci.
Abba ne ya dube ta yace" yanzu me zaki mata wanda baze d'au lokaci ba?"
shuru tayi kaman me tunani sannan tace" sedai gwate"
da sauri yace"to kiyi sauri nima bari naje nan bakin asibiti innemo mata abunda zataci kafin ki dawo"
dubu biyar ya ciro cikin aljihun shi ya mik'a mata sannan yace" ga wannan ki siya duk abunda babu ki hau a daidaita ki dawo, ni zan tsaya nan kafin ki dawo"
kaman zata ce mishi akwai komai to amma data tuna wataran zasu nema seta kar6a ta fice da sauri.
ba 6ata lokaci ta gama komai sannan ta dama mata kunun gyad'a ta had'a komai a flask ta zuba a basket.
d'aki ta koma ta d'au babban sallaya da hijab da kayan Mommy kala biyu sannan ta fito ta kulle 'kofar ta fito da niyan tafiya.
'Kwalla mata kira Mommy tayi, ganinta d'auke da kaya yasa ta fad'in " sai ina kuma a yawo?"
a tak'aice tace" Ummata ce batada lafiya an kwantar ta a asibiti"
ta6e baki tayi tace" Allah kyauta"
da sauri itama ta fita dan komawa asibitin, Haseen ta hango yana k'ok'arin shigowa cikin gidan da motarshi, ganinta da kaya yasashi fasa shiga ya fito ya dubeta sannan yace" ya na ganki da kaya a hannu, waye ba lafiya?
" umma ce take asibiti"
da sauri ya dubeta sannan yace" dama bata da lafiya amma jiya baki fad'amun ba?"
shuru tayi bata ce komai ba.
sanin halinta ya sashi cewa"shigo muje wani asibiti take?"
ba musu ta shiga nan ta fad'a mishi sunan asibitin.
cikin 'kan'kanin lokaci suka iso, Abba suka hango zaune a reception, da gani kasan ita dama yake jira, yana ganin Haseen ya washe baki yace" tare kuke tafe knan?"
nan suka gaisa ya musu jagora zuwa inda Umma take, har lokacin drip ke hanunta, amma ta farka daga baccin, gefen side bed d'in kuwa kayan tea ne da su maltina da fruits da Abba ya siyo mata.
murmushi Haseenah ta saki wa Umma ganin ta dawo dai-dai, nan ta zuba mata abincin ta zauna gefenta tana bata ahankali tasha sossai.
nan Haseen ma ya gaidata suka zauna suna hira, Doctor ne ya shigo suka gaisa da Abba ya d'an dubata sannan yace yana son ganin Abba.
fita yayi ya barsu shikuma ya nufi Office d'in Abokin nashi.
Abunda Dr ya fad'awa Abba shine ya firgitashi ya sashi mik'ewa tsaye ba shiri had'eda zaro ido waje.......
for comments 08144932303
Advertisement
- In Serial25 Chapters
MERTICORE
Meet Ian. Ian is an IT consultant who accepted a supposedly impossible job for an incredible amount of money. However, he quickly learns why his colleagues avoided that gig like the plague. Ian now hates his job, and wants to be fired to get severance pay. However, things don’t go as planned when he downloads MERTICORE, a mysterious program that popped out of nowhere. After that, the life of Ian has changed drastically. Gone are the days of drinking bad coffee while staring at a screen. His days are now filled with magic, fighting weird creatures and even weirder people. Let’s not even mention the comrades he collects along the way, which are more often than not worse than the (numerous) enemies he makes as he bumbles through alternate dimensions. There’s also a disturbing number of laundromats for some reason. Release Schedule: One or two long(2.5k+ words) chapters per week, maybe more depending on real life.
8 148 - In Serial50 Chapters
Age of Legends
Age of Legends takes place in the world of Noctra a decade after a man known as Lord White coveted power for himself by wiping out the two eldest races of Noctra; Ta' and Nomads. Two survivors of this horror reunite and begin a journey to unravel Lord White's world while uncovering the truth to Noctra's history. A man who is initially only known as "Silent One" seeks vengeance for his people while a lively, wild Amberosin simply fights to survive in a world that wishes her dead. As the last two of the elder races, these two wrestle with destiny in their quest for lasting peace.
8 72 - In Serial99 Chapters
BENDING (GXG) (GIRLXGIRL) (GL)
Don't Be Jealous, I Will Bend MyselfBending herself to fall in love with the female lead. The straight pipe, writer Ke is bound to the romance system, the task is to love the female masters from each novel she'd written.In order to complete the task, she dresses as a vicious female supporting character. At the expense of her sexuality, she approaches the female lord.However, the female lead just reached out her hand...Ke Li: Don't be jealous, I will bend myself!The female host silently retracted her hand, which was ready to beat someone.After bending herself....Ke: The male lead can scram.Male Lead: ......[Task] Fall in love with female lead, abuse slag male lead.[Tip] Women have not been able to stand straight since the first world.---Author : 兮木蕭蕭Translator: Novice Translations--This is only posted for offline purposes. I do not own the story, characters and the translations. Those rightfully belong to the content creators.
8 245 - In Serial54 Chapters
NCT -Imagines, Scenarios, Reactions, etc.-
Just as the title says :DNCT OT21 -Please Enjoy! 👻-Started: 6/25/2017
8 187 - In Serial14 Chapters
Demon Contractor Unknowingly Becomes Less Of A Jerk
Alright so I guess the basic summary would be. A demon with the ability to make contracts with the gods themselves, after working for his king for several years decides to hunt his original prey, the humans as the war between humans and demons has ended. He goes to the human land aiming to create pure chaos using his abilities but has to stop as he encounters some strange humans. He pauses his journey is joined by a beast man and a little mage to figure what is going on. (Alright dis is a newbies work and all so I just hope that this is good enough)
8 99 - In Serial22 Chapters
Curse of Muzan
Family burned at the stake, Izuku Midoriya runs away from the sight of the assailants he had lived with to find somewhere to hide. His crime in their eyes, his half demon blood lineage with his family paying the punishment of hiding him. Now trained in the art of the Demon Slayer Corps, Izuku fights the endless hoards of demons to one day face off against the man responsible for so much misery in the world. His father, Muzan Kibutsuji.MHA is rightfully owned by Kohei Horikoshi and Demon Slayer is owned by Kyoharu Gotouge. All art is rightfully owned by their respected owners. Please support the official release.
8 93

