《HASEENAH》Page 7&8
Advertisement
🌸 *HASEENAH*🌸
story nd written
by👇🏻
Aysher Abbakar (Meerah)
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
#
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-08144932303
follow me on wattpad @Aysherabbakar
*long live pml*
*7-8*
Aunty maimuna Mummy ta hango tsaye tana 'kare musu kallo, jikin Mummy ne ya hau tsuma saboda razanar da tayi, dan duk masifar Mummy to Aunty Maimuna tasha gaban ta, cikin 'karfin hali Mummy tace "ke kuma meya kawoki gidannan?"
ba tare da Aunty ta bata amsa ba ta 'karaso yanda suke ta janyo Saratu ta sharara mata mari sannan tace
" fansar marin 'yata da kikayi, kuma kikamun rashin kunya in mari uwarki"
shuru tayi ta rik'e kunci hawaye na zirara, Mummy ce ta fusata cikin tsiwa da tsawa da fara fad'in
" akanme zaki dake ta? ko kina tunanin ke kad'ai kika iya bala'i?"
dariya Aunty tayi sannan tace " ai ita Haseenar da kika sa aka bigeta baiwar uwar wani ko uban wani ce? da kike cewa ta cire kaya ta baki akwai sisin ki aciki ne? to inga uban da zai sake dukanta in k'yale"
ta duba Haseenah tace"wuce ki kama hanya ki tafi kafin in tattaka ki er banza me miskilancin tsiya da ruwan ciki, daga ke har uwarki na rasa wa kuka gado dan ba cikin danginmu ba"
sum sum Haseenah ta kama hanya ta fita, tana fita kuwa ta had'u da Haseen ya d'auketa ya ajiye ta a makaranta.
wunin ranan Mummy ta kasa sukuni tunda Aunty tazo, kai komo kawai take tsakanin palour da bedroom ta sak'a wancan ta kunce wannan duk mafita take nema wajan da zata d'au fansa akan Umma, ita yanzu burinta ta fitar da Umma a gidan ne ta salwantar da Haseenah.
Advertisement
can gefe kuwa Saratu ce take ta k'unk'uni kan marin da aka mata ita a dole Mommy taje ta rama mata.
ran Mommy ya dad'a 6aci jin k'ananan kukan da Saratu ke mata, hakan ya sanya daka matsa tsawa tace" wallahi in baki mun shuru ba senaci ubanki, shegiya da tun kafin zuwanta dakin ma Haseenah duka da ba.azo wannan fagen ba, gashi kinsa ancimun mutunci kan wa'yannan mayun mtwxxxx" taja tsuka ta barta wajan.
Aunty kuwa tana shiga wajan Umma nan ta tarar da ita zaune ta tasa abincin da Haseenah ta zuba mata ta zabga uban tagumi, nan itama ta hau ta da masifa kan shurun yayi yawa meyasa zata bari ana cutar da ita, ita dai Umma hak'uri tayita bata har ta samu ta sauko sannan suka fara tattaunawa.
'''WACECE HASEENAH'''
Haseenah 'ya ce ga Alhaji sani mai Atampa, Alhaji sani su uku ne a wajan mahaifiyarsu, maza biyu mata uku, Muhammad, sani, sai kuna autar su Hajiya Zuwaira, su 'yan asalin jihar Gombe ne, sun taso cikin wahalar rayuwa har Allah ya hore musu sukayi karatun boko cikin yardar Allah Alhaji sani ya had'u da ubangida na 'kwarai har shima ya samu ya bud'e mishi nashi shagon, haka Allah ya sanya mishi Albarka har ya fara fita kasashen k'etare yana shigo da yadika da Atampopi.
shiko Alhaji Muhammad wan shi karatu yayi na likitanci shima Alhmdlh.
Zuwaira kuwa auran wuri aka mata ta na da zama a Kano da yaranta uku.
wata rana Alhaji sani na zaune a shago wata matashiyar yarinya suka zo bara tare da wata dattijuwa, tunda ya 'daura idonshi kan yarinyar yaji ta kwanta mishi a rai, nan ya kudiri niyar taimaka musu, haka yayita bibiyarsu har ya gano gidan su da kuma asalinsu, nan ya hanasu fita bara ya ajiye musu komai wanda zasu buk'ata, nan har Allah yasa suka dai daita da wannan budurwa mai suna Hajara har Allah ya shige masa gaba aka d'aura musu aure, wannan budurwa ba wata bace kuwa illa mummy. anyi auransu da wata d'aya Allah yayiwa mahaifiyar mummy rasuwa.
Advertisement
Umma kuwa 'yar abokin baban Abba ce, saboda nutsuwa da hak'urin ta Mahaifin Abba yayi sha'awar had'a zuri'a da shi, lokacin da yayi magana da Abba bai fuskanci wata matsala ba nan aka fara maganar sa rana, lokacin da ya sanar da mummy kuma ba 'karamin tashin hankali ta d'aga ba tana fad'in gaba d'aya auran su shekara d'aya amma zaice ze mata kishiya, Abba ya rasa inda zaisa rayuwar shi, har 'yar rama ya farayi, ganin haka Hajiya Zuwaira wato 'kanwar Abba tazo har gida ta mata wankin babban bargo kuma tace inta ce zata musu rashin mutunci to angulu zata koma gidanta na tsamiya, jin haka ne yasa mummy ta saduda amma ta 'kudiri aniyar seta fitar da mummy kota tsiya kota arziki.
haka akayi biki aka gama komai amma Mummy ko lek'e babu tana 'kunshe a d'aki ita da 'kawayenta, wanda suke ta faman zugata da mata pampo kan karta kuskura da 'kuruciyar ta a cuceta, nan Mummy ta cika tayi fam.
bayan an watse Mummy ta tada rashin arziki, seda Abba yayi mata barazanar saki sannan ta hak'ura, kiran 'kanwar ta tayi a waya wato Mahaifiyar Haseen, nan ta d'auketa ta kaita wajan wani malami kan a salwantar da Umma, yace hakan bazai yuwu ba dan akwai tsari ajikinta sossai, Mummy ba wani yarda tayi ba nan 'kanwarta ta bata shawarar a mayar da Abba mijin tace, hakan kuwa akayi tunda ga lokacin sai abunda Mummy tace yakeyi, tsoronta yake kamar itace mahaifiyar shi.
da haka Mummy da Umma suka samu ciki a tare, duk wata hanya sunbi dan zubar da cikin amma abu ya gagara, haka har lokacin haihuwar su tayi, Mummy ce ta fara haihuwar saratu, bayan sati d'aya Umma ta Haifi Haseenah, nan Mummy ta hana Abba yin komai sai dangin Abba ne suka mata komai.
tun daga wannan lokacin Umma da d'iyarta suke cikin tsangwama da wahala, dan kafin Haseenah ta girma Umma ce kewa Mummy komai, haka suka taso a wahale har Haseenah ta fara wayo, tun tana aiki Mummy na dukanta har ta koya na dole, haka kuma har yanxu Umma ce kawai ta samu sauk'in aiki yanzu Haseenah take fama.
da Abba yayi yunk'urin 'daukar me aiki Mummy tace sam bata yarda ba ai ga Haseenah, ba yanda ya iya haka ya hak'ura.
wannan knan..
'''CIFABAN LABARI'''
ganin kai komo bazai fishe da Mummy ba yasa ta d'au waya ta kira k'anwar tata wato Mahaifiyar Haseen ta bata labarin abunda ya faru, nan ta hauta da bala'i wai zaman me take yi da bazata d'au mataki akan ta ba, da taga wayar bazai mata ba nan ta sanar da Mummy kan ta shirya gata nan zuwa.....
for comments only 08144932303
Advertisement
- In Serial61 Chapters
Isekai Tensei no Boukensha
Ootori Tenma, who lost his parents and was raised by his grandfather’s and grandmother’s friends who are living in the countryside, loses his life at the age of 25. A god of a different world called out to the ghost Tenma. This is a story about Tenma who, is liked by multiple Gods of reincarnation, receives multiple cheats and lives a second life in another world.
8 309 - In Serial12 Chapters
A Royal Knight From Another World Got Reincarnated To Earth
Ragur, a Royal Knight from another world has passed away after defending his country against the demons. After waking up he found himself in a place where everything is white. There was a woman floating in the air who called herself a goddess. She promised Ragur that she'll reincarnate him to a place called Earth if he swears his loyalty to her. After the goddess reincarnated him to Earth, he woke up as a baby laying under a bridge. He stayed in the cold and starved there for hours till a girl came and took him to the orphanage she was raised in. When Ragur waked up again he found himself on a bed, with a girl laying next to the bed.
8 114 - In Serial6 Chapters
Temporal Deities
In the far future, humanity has spread to new worlds. While spaceships are used to travel to these different worlds, they aren't new planets, but different versions of Earth. Bifrostal vessels are able to travel through space and reality itself. In this new era, several super-corporations emerge and expand rapidly in power and reach. Named after deities of old, they are the true rulers of the three temporal galaxies. Haloke Shanendoah is a lone warrior who has dedicated herself to the increasingly vain quest of finding her lost brother. Her journey brings her to the planet Tefnut where she encounters a corporate spy, Naak. Naak is a secret agent who operates in the perpetual war between the corporations. He thrives in the arena of secrets and craves power and control. Together, they'll try to discover what they stand for in a universe that seems to grow ever bleaker.
8 152 - In Serial34 Chapters
Room 1997 | J. Jungkook ✔
"Would you dare to go inside?"JEON JEONGGUK+ contains gore, profanities, and violence+ suggested to read during daylightREVIEWED BY @TheBTSWriters AND @regan4life THANK YOU VERY MUCH!!!cover created by @suwubins
8 249 - In Serial11 Chapters
It's Just A Prank
Gray and natsu decide to pretend date to prank the guild. But what happens when real feeling began to emerge.
8 152 - In Serial17 Chapters
Familiar
This is the tale of Jordan. A socially awkward high school teenage boy. Sometimes life is unfair, and this is one of those times. Jordan didn't quite anticipate that not doing homework would end up with him being dead. This is my first novel. Please don't hold me at gunpoint... actually, please do. Just take a few steps back so I can see the face of the person that brought my demise upon this earth.
8 72

