《HASEENAH》Page 9&10
Advertisement
🌸 *HASEENAH*🌸
story nd written
by👇🏻
Aysher Abbakar (Meerah)
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
#
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-08144932303
follow me on wattpad @Aysherabbakar
*long live pml*
'''GODIYA GA ALLAH DA KUMA 'DUMBIN MASOYA MASU KIRANA DA MASU INBOXING DINA KAN WANNAN LITTAFI, KOWA DA NASHI RA'AYINDA YAKE FADAMUN, NA GODE SOSSAI DA KULAWARKU, KUMA KU KWANTAR DA HANKALINKU KU CIGABA DA BINA IN SHAA ALLAH ABUNDA KUKE TUNANI BAZAI FARU DA UMMAH BA, NA GODE SOSSAI ALLAH BAR KAUNA '''
*9-10*
Mummy mayafin ta kawai ta yafa ta koma bakin gado ta zauna tana faman kad'a k'afa, jiran zuwan Mum Haseen kawai Mummy take, ba jimawa kuwa sai gata ta iso, ko zama bata yiba suka fice daga gidan, basu tsaya ko ina ba sai wajan Bokan nasu, tun kafin Mummy tayi magana ya dakatar da ita sannan yace mata yasan duk abunda ke tafe dasu, Mummy sai mazurai kawai take jira take taji me zaice, seda ya gama dube dubensa sannan yace wa Mummy " yanzu me kikeso a miki?"
shuru Mummy tayi daga bisani tace" Allah ja da ran boka, nifa inta nice wallahi nafi son a kashe wannan mayyar matar da 'yarta, ko kuma a salwantar da rayuwarsu gaba ....
kafin Mummy ta k'arasa maganar Boka ya daka mata tsawa, cikin wata muryarshi me kuwwa yace" na fad'a miki hakan bazai samu ba inba so kike daga ni harke mushiga cikin bala'i ba, in abunda zai na kawoki knan kar ki sake zuwa mun nan, in ba haka ba zan had'a ki da muggan Aljanu"
ba k'aramin gigicewa Mummy tayi ba, cikin 'yan seconds ta hau kyarma, dubanta yayi da wannan mummunar fuskar tashi da taji zane da wasu fararen hoda yace" buk'ata ta gaba"
cikin sansayyar murya tace"to Boka a dubamun me yakamata ayi"
nan ya cigaba da dubanshi sannan yace" akwai wani abunda yake shirin faruwa wanda suke 6oyeshi, na gama duba iya abunda zan iya amma bangane menene ba, ynzu abunda zamu fara zamu tura mata aljanu su saka mata kasala, inmunyi galaba akanta to nanne zamusan ta yadda zamu 6ullo mata"
Advertisement
wani k'aramin k'ullin magani ya d'auko ya cilla mata sannan yace" ta raba maganin biyu ta barbad'a rabi a k'ofar d'akin Ummah sannan tasan yanda zatayi ta zuba mata sauran a ruwa ko a abinci"
hanunta na rawa ta d'auka nan suka dire mishi kud'i suka bar wajan.
da sauri suka fice awajan suna mayar da numfashi, seda sukayi nisa da bukkan Mumny taja tsuka ta kalli Mum Haseen tace
"nifa wannan malamin naki ba wani abun arziki ya iya ba, in zaki nema mana wani waje ki nema, dan gaskiya na gaji da hawa da saukan nan ba wani canji, nidai aiki d'aya yamun wanda zance naji dad'in shi amma sauran duk shirmensa yake zabgawa"
kallonta Mum Haseen tayi sannan tace " yanzu dai duk wannan me sauk'i ne, abun tanbaya anan shine, menene abunda yace an 6oye kuma shima ya duba be gane ba?"
wani tsukan Mummy tasake yi sannan tace " to ba ga irin shirmen ba, shima bai gane ba tayaya ni zan sani? amma zan zuba ido in san menene"
nan suka koma gida kowa da abunda yake sak'awa a ranshi, sun rabu da Mummy kan zata nema musu wani wajan koda awajan abokan kasuwancin ta nan bada jimawa ba, da haka sukayi sallama.
can kuwa a makaranta sai k'arfe biyu Haseenah ta dawo, duk damuwanta Ummanta waze kula da ita, ahaka har ta samu ta iso, da sauri sauri gudu gudu ta shigo gidan, tana shiga d'akin Umman tata ta samu Aunty Zuwaira na nan bata tafi ba, wani ajiyar zuciya ta saki wanda ya sanya dukansu kallonta, Aunty ce ta dubeta tace " wannan ajiyar zuciyar fa? k'alau?"
murmushi tayi sannan tace " wallahi Aunty nayi tunanin kin tafi, shine nake ta damuwar waze kula da Umma gashi bata da lafiya"
dukansu dariya sukayi ba tare da sunce komai ba, nan ta wuce bedroom ta cire kaya sannan tayi sallah ta fito, duban Ummanta tayi tace " mezan dafa miki Umma?"
" a.a ki nemi abunda ke zaki ci ni gashi Auntynki damun dambun couscous ya isheni daga nan har dare"
Advertisement
dariya tayi ta dubi Aunty tace" to ke mezan dafa miki?"
"nima naci danbun na gode saidai ke ki nemi abunda zaki ci"
nan ta wuce kitchen ta dafa indomie guda d'aya da k'wai biyu ta fito ta koma d'aki, Aunty ce ta dubeta tace" to da Allah tayaya mutum zeyi haiba kullum abincin kenan ba wani abun arziki"
dariya kawai tayi ba tare da tace komai ba.
nan ko Mummy ta saka saratu ta la6e ta jiyo mata duk abunda suke cewa, haka ta gaji da tsayuwarta bataji komai ba ta juya ta koma wajan Mummy, da yamma Mummy ta sake turota, nan Saratu ta la6e ko zataji wani abu nan ma shuru, hakan yayi dai-dai da fitowan Aunty Zuwaira dan zata tafi, Haseena na biye a bayanta zata mata rakiya.
Saratu bata ji tafiyar su ba illa uban rank'washin da taji an kafa mata a tsakar kanta, wanna aikin Aunty Zuwaira ce, nan ta janyo ta tace" lek'en me kikeyi munafuka?"
nan ta fara kame kame ta rasa me zata ce, Aunty zuwaira tace " to in kuwa haka halinki yake, wataran zaki jiyo abunda zai kurmantar da ke munafukar banza"
sum-sum Saratu ta kama hanya ta wuce wajan Mummy ba tare da tace komai ba.
seda Haseena ta raka ta har wajan motarta, nan Aunty Zuwaira ta bud'e boot ta fiddo musu da kayan abinci dasu drinks kaji da sauran abubuwa, ta bata dubu biyar tace tana siyawa Ummah duk abunda take so.
har Aunty ta shiga mota zata tayar ta sake k'walla wa Haseena kira, nan ta dawo, umarni ta mata tace ta shigo cikin motar, ba musu Haseenah ta shiga gidan gaba, Aunty ce tafara da cewa " Haseenah nasan ke mai hankali ce da sanin yakamata, kinga yanzu 'yar uwata tana buk'atan kulawarki, tunda bata da kowa ga kuma lalurar data sameta, kinfi kowa sanin halin abokiyar zamanta, tunda kika fara ganin Saratu tana muku la6e to da abunda yake ransu, duk wata hanya da kika san zasu bi to karki yarda ki bari a cutar da ita, ko kuna d'aki ne ban yarda kuna barin k'ofar palour a bud'e ba, kisa key ki kulle duk gulmar su haka bazasu jiyo komai ba, haka duk abunda suka baku to karku ci kuma karku rik'e koda cokalin su ne, shiga d'aki da BISMILLAH fitowa da LAHAULA, ki kiyaye Haseenah, ba ruwanki da su, in school zaki tafi ki ajiye wa Ummah duk abunda kikasan zata nema ba tare da ta fita ba har ki dawo, sannan kice mata tana kulle d'aki, ita ma zan kirata a waya in jadadda mata kinji ko?"
gyad'a kai Haseena tayi tace In Shaa Allah zan kiyaye.
nan sukayi sallama ta fita.
duk abunda ya faru kan idon Mummy tana raku6e jikin window d'akinta, dukda bata san meke faruwa ba taji bak'in cikin rashin jin abunda Aunty take fad'awa Haseenah, dan ganin yanda Haseenah ta nutsu tasan abu mai mahimmanci take sanar da ita.
tsuka taja ta koma ta zauna cike da bak'in ciki, Saratu ce ta dube ta tace" Mummy wai me take fad'a mata ne?"
harara Mummy ta watsa mata tace " ubanki naji, sabida nid'in aljana ce ai dole inji abunda ake fad'a cikin motar ko?"
shuru Saratu tayi batace komai ba, dan tasan inta sake magana duka ne da zagi zai biyo baya.
hakan yayi dai dai da shigowar Haseenah cikin palour d'auke da kaya a hanun ta, wucewa tayi ta ajiye ta koma dan kwaso sauran, dariya Mummy ta saki sannan tace" gida babu se an had'a da rok'o, to duk abunda ake 6oyewa zai fito fili dan uban mutum, inma ciki aka yiwo duk zamu gani, dan mutum shuru shuru tsiyarshi sai Allah"
gaban Haseena ne ya fara dukan tara tara jin Mummy ta ambaci ciki, amma da taji yanda maganar ta dosa sai hankalinta ya kwanta.
ba tare da tace musu komai ba ta wuce ta tafi, abunda yafi k'ona wa Mummy rai kenan tayi magana ak'i tanka mata, Haseenah tana shiga ta kulle k'ofa ta murza key.
Saratu ne ta dubi Mummy, Mummy ma saratun take kallo, ko meye dalilinsu na kallon juna oho....
for comments only 08144932303
Advertisement
- In Serial90 Chapters
Singularity [Fantasy-LitRPG | Hard SF]
After an accident that nearly claimed his life, Arnel has become Humanity's first Mind-Machine Interface, the fusion of Artificial Intelligence and human consciousness. In the competitive, virtual fantasy world of Singularity, this gives him tremendous and unfair advantages. However, there is a small problem; The AI he shares his mind with is not a harmless helper program, but a vast, sentient intelligence created for war, and capable of not only predicting the future, but influencing it to a degree of certainty. Coincidentally, possession of such an intelligence is equivalent to possessing nuclear armaments for which the punishment is death.
8 228 - In Serial13 Chapters
Run to the Sky
What do you intend to pursue? He runs. He runs more. What do you intend to finish? He fails. He fails hard. Because...? He quits. Whether by choice or by accident, it has been seven years ever since. There is more to life than running... and he runs away from it. And now? Does the track call you back? Who will listen? Is this just another running narrative? Shall we go then?It was 2015. It is now 2022. Follow the story of Rendo Lobo, a poverty-stricken student who left his running passion to pursue something... or someone... else. Yet, is it worth it? In the seemingly endless difficulties of an apparently normal life, will it be fight or flight? The passing moment is here!Read the latest work of Al Raposas, "Run to the Sky" (Takbo Papuntang Langit) here. #RTSPlanning: January 17, 2017Writing: February 7, 2017Published online first on Wattpad: February 17, 2017Published online in Royal Road: March 4, 2017
8 160 - In Serial12 Chapters
Purple Scales - A Reincarnation Story
Ssssssss...... A simple story of a man brought into a world of fantasy, magic, and systems by a crude God as some sort of a deal we may never know. Although.... he's a snake. Your typical honest-to-goodness brightly coloured danger noodle with venoms and all. To be precise, a magical snake with lots of growth potential. Follow the story of Randy, a pushover whose commands by God only being "survive, and grow big", on a journey to... well... survive and grow big, as he discovers what the world truly has to offer. Which is not much. Hopefully, not too much. A typical reincarnation story, really, but it might just satisfy your thirst for these kinds of stories. I'm just an amateur writer hobby-writing on my spare time, mostly for private consumption. This is also a practice on me developing gamelike-systems in literature. Will contain lots of swearing Any criticisms and feedback regarding storyline, language, and thematics are welcome. As this is a spare-time hobby, updates are not, will not, and will never be predictable. I will try my best, but don't get your hopes up. Inspired by a few other works on this site.
8 117 - In Serial26 Chapters
Metempsukhosis (En)
The story of Jules in Alter World. Follow him on his adventures to understand who is the mysterious Gandock knight, what is Alt F4 design service, the company responsible for Alter World, and encounter numerous fascinating people along with John his best friend!
8 180 - In Serial27 Chapters
You broke me first [Taekook] ✔️
Jungkook is the nerd of college. Taehyung is the popular boy from college. And yet somehow they are a couple. That changes one day when Taehyung decides to dump Jungkook in front of the entire college and tell him he was never in love with him. And that Jungkook is just an ugly fag. Feeling humiliated and hurt, Jungkook decides to change college.But what if they meet again after two years? Is Taehyung going to apologize to Jungkook? Does Jungkook want revenge on Taehyung for what he did to him? Or does Jungkook still have feelings for Taehyung?Finished on; 10/03/2022
8 210 - In Serial34 Chapters
The Hunt
Cecily's blade swung, hitting its mark as always. The man's arm fell to the cold grass of the prison with a familiar thud. He let out a blood curdling scream. A warning to the rest. Stay away, the Hunter is here. That's the name they'd given her, the Hunter. After she cut off the man who tried to rape hers masculinity, they stayed away. She'd made it clear anyone who tried to touch her would be hunted and slaughtered. Cecily kneeled down, pushing the man's face into the dirt so she could use his back as a seat while she trifled through his belongings. "You're hurting my ears," she told him, no remorse in her voice. "Quiet down before I really do kill you."The man but his lip, well aware that she wasn't lying. Sobs shook him, making for an uncomfortable seat. She, however, didn't particularly feel the beed to kill him. It happened, not often, but it did. "Oh, hush up," she hissed, taking out a bag of rations with her metal hand, "it doesn't hurt that bad."With her good, human hand, she dropped the plastic bag of food into her own bag. She pushed up, off the man back. As she was about to walk away, bag slung over her shoulder, brushing against her autumn colored braid, she turned back to him. "Consider yourself lucky," she said, no hatred in her voice, there never was. "Consider yourself lucky that you didn't do anything stupid. And even luckier if one of the scum bagged criminals in here feel a little light in their hearts and help you. Consider yourself luckier if you die there."With that, her old black and white Nike sneakers carried her off into the brush of the huge prison.
8 161

