《HASEENAH》Page 9&10
Advertisement
🌸 *HASEENAH*🌸
story nd written
by👇🏻
Aysher Abbakar (Meerah)
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
#
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-08144932303
follow me on wattpad @Aysherabbakar
*long live pml*
'''GODIYA GA ALLAH DA KUMA 'DUMBIN MASOYA MASU KIRANA DA MASU INBOXING DINA KAN WANNAN LITTAFI, KOWA DA NASHI RA'AYINDA YAKE FADAMUN, NA GODE SOSSAI DA KULAWARKU, KUMA KU KWANTAR DA HANKALINKU KU CIGABA DA BINA IN SHAA ALLAH ABUNDA KUKE TUNANI BAZAI FARU DA UMMAH BA, NA GODE SOSSAI ALLAH BAR KAUNA '''
*9-10*
Mummy mayafin ta kawai ta yafa ta koma bakin gado ta zauna tana faman kad'a k'afa, jiran zuwan Mum Haseen kawai Mummy take, ba jimawa kuwa sai gata ta iso, ko zama bata yiba suka fice daga gidan, basu tsaya ko ina ba sai wajan Bokan nasu, tun kafin Mummy tayi magana ya dakatar da ita sannan yace mata yasan duk abunda ke tafe dasu, Mummy sai mazurai kawai take jira take taji me zaice, seda ya gama dube dubensa sannan yace wa Mummy " yanzu me kikeso a miki?"
shuru Mummy tayi daga bisani tace" Allah ja da ran boka, nifa inta nice wallahi nafi son a kashe wannan mayyar matar da 'yarta, ko kuma a salwantar da rayuwarsu gaba ....
kafin Mummy ta k'arasa maganar Boka ya daka mata tsawa, cikin wata muryarshi me kuwwa yace" na fad'a miki hakan bazai samu ba inba so kike daga ni harke mushiga cikin bala'i ba, in abunda zai na kawoki knan kar ki sake zuwa mun nan, in ba haka ba zan had'a ki da muggan Aljanu"
ba k'aramin gigicewa Mummy tayi ba, cikin 'yan seconds ta hau kyarma, dubanta yayi da wannan mummunar fuskar tashi da taji zane da wasu fararen hoda yace" buk'ata ta gaba"
cikin sansayyar murya tace"to Boka a dubamun me yakamata ayi"
nan ya cigaba da dubanshi sannan yace" akwai wani abunda yake shirin faruwa wanda suke 6oyeshi, na gama duba iya abunda zan iya amma bangane menene ba, ynzu abunda zamu fara zamu tura mata aljanu su saka mata kasala, inmunyi galaba akanta to nanne zamusan ta yadda zamu 6ullo mata"
Advertisement
wani k'aramin k'ullin magani ya d'auko ya cilla mata sannan yace" ta raba maganin biyu ta barbad'a rabi a k'ofar d'akin Ummah sannan tasan yanda zatayi ta zuba mata sauran a ruwa ko a abinci"
hanunta na rawa ta d'auka nan suka dire mishi kud'i suka bar wajan.
da sauri suka fice awajan suna mayar da numfashi, seda sukayi nisa da bukkan Mumny taja tsuka ta kalli Mum Haseen tace
"nifa wannan malamin naki ba wani abun arziki ya iya ba, in zaki nema mana wani waje ki nema, dan gaskiya na gaji da hawa da saukan nan ba wani canji, nidai aiki d'aya yamun wanda zance naji dad'in shi amma sauran duk shirmensa yake zabgawa"
kallonta Mum Haseen tayi sannan tace " yanzu dai duk wannan me sauk'i ne, abun tanbaya anan shine, menene abunda yace an 6oye kuma shima ya duba be gane ba?"
wani tsukan Mummy tasake yi sannan tace " to ba ga irin shirmen ba, shima bai gane ba tayaya ni zan sani? amma zan zuba ido in san menene"
nan suka koma gida kowa da abunda yake sak'awa a ranshi, sun rabu da Mummy kan zata nema musu wani wajan koda awajan abokan kasuwancin ta nan bada jimawa ba, da haka sukayi sallama.
can kuwa a makaranta sai k'arfe biyu Haseenah ta dawo, duk damuwanta Ummanta waze kula da ita, ahaka har ta samu ta iso, da sauri sauri gudu gudu ta shigo gidan, tana shiga d'akin Umman tata ta samu Aunty Zuwaira na nan bata tafi ba, wani ajiyar zuciya ta saki wanda ya sanya dukansu kallonta, Aunty ce ta dubeta tace " wannan ajiyar zuciyar fa? k'alau?"
murmushi tayi sannan tace " wallahi Aunty nayi tunanin kin tafi, shine nake ta damuwar waze kula da Umma gashi bata da lafiya"
dukansu dariya sukayi ba tare da sunce komai ba, nan ta wuce bedroom ta cire kaya sannan tayi sallah ta fito, duban Ummanta tayi tace " mezan dafa miki Umma?"
" a.a ki nemi abunda ke zaki ci ni gashi Auntynki damun dambun couscous ya isheni daga nan har dare"
Advertisement
dariya tayi ta dubi Aunty tace" to ke mezan dafa miki?"
"nima naci danbun na gode saidai ke ki nemi abunda zaki ci"
nan ta wuce kitchen ta dafa indomie guda d'aya da k'wai biyu ta fito ta koma d'aki, Aunty ce ta dubeta tace" to da Allah tayaya mutum zeyi haiba kullum abincin kenan ba wani abun arziki"
dariya kawai tayi ba tare da tace komai ba.
nan ko Mummy ta saka saratu ta la6e ta jiyo mata duk abunda suke cewa, haka ta gaji da tsayuwarta bataji komai ba ta juya ta koma wajan Mummy, da yamma Mummy ta sake turota, nan Saratu ta la6e ko zataji wani abu nan ma shuru, hakan yayi dai-dai da fitowan Aunty Zuwaira dan zata tafi, Haseena na biye a bayanta zata mata rakiya.
Saratu bata ji tafiyar su ba illa uban rank'washin da taji an kafa mata a tsakar kanta, wanna aikin Aunty Zuwaira ce, nan ta janyo ta tace" lek'en me kikeyi munafuka?"
nan ta fara kame kame ta rasa me zata ce, Aunty zuwaira tace " to in kuwa haka halinki yake, wataran zaki jiyo abunda zai kurmantar da ke munafukar banza"
sum-sum Saratu ta kama hanya ta wuce wajan Mummy ba tare da tace komai ba.
seda Haseena ta raka ta har wajan motarta, nan Aunty Zuwaira ta bud'e boot ta fiddo musu da kayan abinci dasu drinks kaji da sauran abubuwa, ta bata dubu biyar tace tana siyawa Ummah duk abunda take so.
har Aunty ta shiga mota zata tayar ta sake k'walla wa Haseena kira, nan ta dawo, umarni ta mata tace ta shigo cikin motar, ba musu Haseenah ta shiga gidan gaba, Aunty ce tafara da cewa " Haseenah nasan ke mai hankali ce da sanin yakamata, kinga yanzu 'yar uwata tana buk'atan kulawarki, tunda bata da kowa ga kuma lalurar data sameta, kinfi kowa sanin halin abokiyar zamanta, tunda kika fara ganin Saratu tana muku la6e to da abunda yake ransu, duk wata hanya da kika san zasu bi to karki yarda ki bari a cutar da ita, ko kuna d'aki ne ban yarda kuna barin k'ofar palour a bud'e ba, kisa key ki kulle duk gulmar su haka bazasu jiyo komai ba, haka duk abunda suka baku to karku ci kuma karku rik'e koda cokalin su ne, shiga d'aki da BISMILLAH fitowa da LAHAULA, ki kiyaye Haseenah, ba ruwanki da su, in school zaki tafi ki ajiye wa Ummah duk abunda kikasan zata nema ba tare da ta fita ba har ki dawo, sannan kice mata tana kulle d'aki, ita ma zan kirata a waya in jadadda mata kinji ko?"
gyad'a kai Haseena tayi tace In Shaa Allah zan kiyaye.
nan sukayi sallama ta fita.
duk abunda ya faru kan idon Mummy tana raku6e jikin window d'akinta, dukda bata san meke faruwa ba taji bak'in cikin rashin jin abunda Aunty take fad'awa Haseenah, dan ganin yanda Haseenah ta nutsu tasan abu mai mahimmanci take sanar da ita.
tsuka taja ta koma ta zauna cike da bak'in ciki, Saratu ce ta dube ta tace" Mummy wai me take fad'a mata ne?"
harara Mummy ta watsa mata tace " ubanki naji, sabida nid'in aljana ce ai dole inji abunda ake fad'a cikin motar ko?"
shuru Saratu tayi batace komai ba, dan tasan inta sake magana duka ne da zagi zai biyo baya.
hakan yayi dai dai da shigowar Haseenah cikin palour d'auke da kaya a hanun ta, wucewa tayi ta ajiye ta koma dan kwaso sauran, dariya Mummy ta saki sannan tace" gida babu se an had'a da rok'o, to duk abunda ake 6oyewa zai fito fili dan uban mutum, inma ciki aka yiwo duk zamu gani, dan mutum shuru shuru tsiyarshi sai Allah"
gaban Haseena ne ya fara dukan tara tara jin Mummy ta ambaci ciki, amma da taji yanda maganar ta dosa sai hankalinta ya kwanta.
ba tare da tace musu komai ba ta wuce ta tafi, abunda yafi k'ona wa Mummy rai kenan tayi magana ak'i tanka mata, Haseenah tana shiga ta kulle k'ofa ta murza key.
Saratu ne ta dubi Mummy, Mummy ma saratun take kallo, ko meye dalilinsu na kallon juna oho....
for comments only 08144932303
Advertisement
- In Serial36 Chapters
Old Version - The First Magician
INDEFINITE HIATUS I always seem to make these too long when I ask for peoples opinions so I’m not gonna try an exciting description anymore but instead just give you an idea of what to expect. First off, this is my 2nd attempt at a story but my foundation for this one is much better than the 1st already and I see this going much further and so far its coming together much faster and easier. So please excuse me if things are not up to publishing standards. Also I tend to confuse your, you’re and so on so sorry to people that triggers ahead of time. The First Magician follows the story of 15 year old Alex in a post apocalyptic rpg-ish world in the near future. Earth was transformed, monsters appeared and people began being able to use Ki but could not figure out how to use magic. Alex ends up becoming the first human able to use magic through a series of events and sets in motion events that will change the very future of the human race. He will be somewhat OP simply because he is the only human (at least to start, who knows about later?) who is able to use mana. Many classic RPG elements have been removed. I didn’t want the story to be like all of the other lit rpg stories on RRL but it also makes the writing easier for me hence the watering down of rpg elements. UPDATES: I am doing this to relieve stress and for fun so I will release chapters when I can. So far though ive managed to keep up with 2 most days. CONTENT WARNINGS: There will be some light language but it won't be insane. I might have some gore later on but am unsure and the same for the sexual content. Sexual content isn't super likely as I doubt I can write it well but I put the tag so people cant yell about it if I add some in the future but forgot to add the tag. COVER ART: Yes it is from the anime Log Horizon. It is a good representation of what earth looks like despite it not being many years in the future. DISCORD: https://discord.gg/s6V3hGV
8 129 - In Serial40 Chapters
Observation of a Demon Tortoise
An animal as ordinary as a tortoise holds the potential to become a powerful demon. This is the observation of one such tortoise that lived a long life of hardship and desire, falling to the dark side and becoming a creature that nothing could oppose. However, no matter how powerful it was in its later days, in its early life, it was a vulnerable animal that risked its life nearly every day. This is a record from birth to demonification to death. A full biography of this magnificent creature in all its glory. Credits to EpicKiller11 for the cover.
8 72 - In Serial7 Chapters
Armor Corps
The Nek'var Empire marches across the stars. Their ruthless campaign to purge all life from the galaxy has crushed a thousand years of peace. Fires rage in cities all across the Galactic Union. Their grand armies have been crushed, cities conquered. Nothing stands between a sweeping Nek'var victory but the battered remnants of a mauled fleet. If they fall, the galaxy falls with them. Meanwhile, humanity is an unknown power emerging from their little speck of space when they are inexplicably attacked by a powerful alien fleet, forcing the ever squabbling nations of Sol to form a grudging alliance in the face of annihilation. Corporal Erik Shields finds himself far from home, embroiled in a life or death struggle on the surface of a colony world known as MX-01, battling for humanity's future against a seemingly unstoppable force. But there is a glimmer of hope when Fleet engineers develop a miniaturized reactor core capable of fully realizing the power armor program's vast potential and a desperate mission is cobbled together to deploy the newly formed Armor Corps to the surface in hopes of defeating the enemy invasion. This is a tale of defiance in the face of annihilation, the soul-crushing horror of interstellar war, and the death of dreams.
8 91 - In Serial19 Chapters
Just Another Isekai
Two friends are at school, two friends are killed at school, two friends are reincarnated into another world. Do they become leechers who try to build a harem? Do they become mob charecters that control everything from the shadows? Do they end up dying and getting reincarnated again? I don't know, I'm not a psychic. *Warning* This is mostly being written for fun but any and all critisms are welcomed. Even if I am doing it for fun, I still wanna get better because I know I have plenty of room to improve. I do plan on having the readers direct which way the story goes. I have a somewhat busy schedule but I'll try to update as frequently as I can.
8 163 - In Serial8 Chapters
(Suddenly a) Dungeon Master
Quint was helping his master Woggins the Wise with something only the most powerful wizards attempt : Binding a dungeon core and becoming a dungeon master. Unfortunately, an accident causes it to go terribly wrong and Quint suddenly finds himself the youngest dungeon master in history, thrown into a position of great power, responsibility, and enemies that come with it. With occasional advice from the ghost of his master, now bound to the dungeon core, Quint attempts to ‘do the right thing’ as a budding dungeon master. Wait… are there mice in his dungeon?
8 161 - In Serial44 Chapters
ᴅᴇꜱɪɢɴᴇʀ||ᴋ.ᴋᴏᴢᴜᴍᴇ †
*pretty crap and cringe ngl*(Credits to @spriscillart for cover art)❛❛𝐁𝐞𝐢𝐧𝐠 𝐚 𝐛𝐢𝐭 𝐛𝐨𝐥𝐝𝐞𝐫 𝐭𝐨𝐝𝐚𝐲 𝐡𝐮𝐡?❜❜❛❛𝐖𝐡𝐞𝐧 𝐲𝐨𝐮 𝐭𝐞𝐚𝐬𝐞 𝐦𝐞 𝐥𝐢𝐤𝐞 𝐭𝐡𝐚𝐭, 𝐨𝐟𝐜𝐨𝐮𝐫𝐬𝐞.❜❜「ᴀ ꜱᴛᴏʀʏ ᴡʜᴇʀᴇ ᴛᴡᴏ ɴᴇᴡ ʀᴏᴏᴍᴀᴛᴇꜱ ᴍᴇᴇᴛ, ʙᴜᴛ ᴡɪʟʟ ᴛʜᴇʏ ʜɪᴛ ɪᴛ ᴏꜰꜰ?」-ꜱᴇɴꜱɪᴛɪᴠᴇ ᴛᴏᴘɪᴄꜱ-ꜱᴍᴜᴛᴛ-ꜰʟᴜꜰꜰ-ᴀɴɢꜱᴛ-ɪ ᴅᴏ ɴᴏᴛ ᴏᴡɴ ʜᴀɪᴋʏᴜᴜ ᴊᴜꜱᴛ ᴛʜᴇ ᴘʟᴏᴛ ᴀɴᴅ ᴛʜᴇ ᴛʜᴇᴍᴇ ♡Haikyuu© Haruichi furudateDesigner© WeekndHigh
8 97

