《HASEENAH》Page 9&10
Advertisement
🌸 *HASEENAH*🌸
story nd written
by👇🏻
Aysher Abbakar (Meerah)
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
#
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-08144932303
follow me on wattpad @Aysherabbakar
*long live pml*
'''GODIYA GA ALLAH DA KUMA 'DUMBIN MASOYA MASU KIRANA DA MASU INBOXING DINA KAN WANNAN LITTAFI, KOWA DA NASHI RA'AYINDA YAKE FADAMUN, NA GODE SOSSAI DA KULAWARKU, KUMA KU KWANTAR DA HANKALINKU KU CIGABA DA BINA IN SHAA ALLAH ABUNDA KUKE TUNANI BAZAI FARU DA UMMAH BA, NA GODE SOSSAI ALLAH BAR KAUNA '''
*9-10*
Mummy mayafin ta kawai ta yafa ta koma bakin gado ta zauna tana faman kad'a k'afa, jiran zuwan Mum Haseen kawai Mummy take, ba jimawa kuwa sai gata ta iso, ko zama bata yiba suka fice daga gidan, basu tsaya ko ina ba sai wajan Bokan nasu, tun kafin Mummy tayi magana ya dakatar da ita sannan yace mata yasan duk abunda ke tafe dasu, Mummy sai mazurai kawai take jira take taji me zaice, seda ya gama dube dubensa sannan yace wa Mummy " yanzu me kikeso a miki?"
shuru Mummy tayi daga bisani tace" Allah ja da ran boka, nifa inta nice wallahi nafi son a kashe wannan mayyar matar da 'yarta, ko kuma a salwantar da rayuwarsu gaba ....
kafin Mummy ta k'arasa maganar Boka ya daka mata tsawa, cikin wata muryarshi me kuwwa yace" na fad'a miki hakan bazai samu ba inba so kike daga ni harke mushiga cikin bala'i ba, in abunda zai na kawoki knan kar ki sake zuwa mun nan, in ba haka ba zan had'a ki da muggan Aljanu"
ba k'aramin gigicewa Mummy tayi ba, cikin 'yan seconds ta hau kyarma, dubanta yayi da wannan mummunar fuskar tashi da taji zane da wasu fararen hoda yace" buk'ata ta gaba"
cikin sansayyar murya tace"to Boka a dubamun me yakamata ayi"
nan ya cigaba da dubanshi sannan yace" akwai wani abunda yake shirin faruwa wanda suke 6oyeshi, na gama duba iya abunda zan iya amma bangane menene ba, ynzu abunda zamu fara zamu tura mata aljanu su saka mata kasala, inmunyi galaba akanta to nanne zamusan ta yadda zamu 6ullo mata"
Advertisement
wani k'aramin k'ullin magani ya d'auko ya cilla mata sannan yace" ta raba maganin biyu ta barbad'a rabi a k'ofar d'akin Ummah sannan tasan yanda zatayi ta zuba mata sauran a ruwa ko a abinci"
hanunta na rawa ta d'auka nan suka dire mishi kud'i suka bar wajan.
da sauri suka fice awajan suna mayar da numfashi, seda sukayi nisa da bukkan Mumny taja tsuka ta kalli Mum Haseen tace
"nifa wannan malamin naki ba wani abun arziki ya iya ba, in zaki nema mana wani waje ki nema, dan gaskiya na gaji da hawa da saukan nan ba wani canji, nidai aiki d'aya yamun wanda zance naji dad'in shi amma sauran duk shirmensa yake zabgawa"
kallonta Mum Haseen tayi sannan tace " yanzu dai duk wannan me sauk'i ne, abun tanbaya anan shine, menene abunda yace an 6oye kuma shima ya duba be gane ba?"
wani tsukan Mummy tasake yi sannan tace " to ba ga irin shirmen ba, shima bai gane ba tayaya ni zan sani? amma zan zuba ido in san menene"
nan suka koma gida kowa da abunda yake sak'awa a ranshi, sun rabu da Mummy kan zata nema musu wani wajan koda awajan abokan kasuwancin ta nan bada jimawa ba, da haka sukayi sallama.
can kuwa a makaranta sai k'arfe biyu Haseenah ta dawo, duk damuwanta Ummanta waze kula da ita, ahaka har ta samu ta iso, da sauri sauri gudu gudu ta shigo gidan, tana shiga d'akin Umman tata ta samu Aunty Zuwaira na nan bata tafi ba, wani ajiyar zuciya ta saki wanda ya sanya dukansu kallonta, Aunty ce ta dubeta tace " wannan ajiyar zuciyar fa? k'alau?"
murmushi tayi sannan tace " wallahi Aunty nayi tunanin kin tafi, shine nake ta damuwar waze kula da Umma gashi bata da lafiya"
dukansu dariya sukayi ba tare da sunce komai ba, nan ta wuce bedroom ta cire kaya sannan tayi sallah ta fito, duban Ummanta tayi tace " mezan dafa miki Umma?"
" a.a ki nemi abunda ke zaki ci ni gashi Auntynki damun dambun couscous ya isheni daga nan har dare"
Advertisement
dariya tayi ta dubi Aunty tace" to ke mezan dafa miki?"
"nima naci danbun na gode saidai ke ki nemi abunda zaki ci"
nan ta wuce kitchen ta dafa indomie guda d'aya da k'wai biyu ta fito ta koma d'aki, Aunty ce ta dubeta tace" to da Allah tayaya mutum zeyi haiba kullum abincin kenan ba wani abun arziki"
dariya kawai tayi ba tare da tace komai ba.
nan ko Mummy ta saka saratu ta la6e ta jiyo mata duk abunda suke cewa, haka ta gaji da tsayuwarta bataji komai ba ta juya ta koma wajan Mummy, da yamma Mummy ta sake turota, nan Saratu ta la6e ko zataji wani abu nan ma shuru, hakan yayi dai-dai da fitowan Aunty Zuwaira dan zata tafi, Haseena na biye a bayanta zata mata rakiya.
Saratu bata ji tafiyar su ba illa uban rank'washin da taji an kafa mata a tsakar kanta, wanna aikin Aunty Zuwaira ce, nan ta janyo ta tace" lek'en me kikeyi munafuka?"
nan ta fara kame kame ta rasa me zata ce, Aunty zuwaira tace " to in kuwa haka halinki yake, wataran zaki jiyo abunda zai kurmantar da ke munafukar banza"
sum-sum Saratu ta kama hanya ta wuce wajan Mummy ba tare da tace komai ba.
seda Haseena ta raka ta har wajan motarta, nan Aunty Zuwaira ta bud'e boot ta fiddo musu da kayan abinci dasu drinks kaji da sauran abubuwa, ta bata dubu biyar tace tana siyawa Ummah duk abunda take so.
har Aunty ta shiga mota zata tayar ta sake k'walla wa Haseena kira, nan ta dawo, umarni ta mata tace ta shigo cikin motar, ba musu Haseenah ta shiga gidan gaba, Aunty ce tafara da cewa " Haseenah nasan ke mai hankali ce da sanin yakamata, kinga yanzu 'yar uwata tana buk'atan kulawarki, tunda bata da kowa ga kuma lalurar data sameta, kinfi kowa sanin halin abokiyar zamanta, tunda kika fara ganin Saratu tana muku la6e to da abunda yake ransu, duk wata hanya da kika san zasu bi to karki yarda ki bari a cutar da ita, ko kuna d'aki ne ban yarda kuna barin k'ofar palour a bud'e ba, kisa key ki kulle duk gulmar su haka bazasu jiyo komai ba, haka duk abunda suka baku to karku ci kuma karku rik'e koda cokalin su ne, shiga d'aki da BISMILLAH fitowa da LAHAULA, ki kiyaye Haseenah, ba ruwanki da su, in school zaki tafi ki ajiye wa Ummah duk abunda kikasan zata nema ba tare da ta fita ba har ki dawo, sannan kice mata tana kulle d'aki, ita ma zan kirata a waya in jadadda mata kinji ko?"
gyad'a kai Haseena tayi tace In Shaa Allah zan kiyaye.
nan sukayi sallama ta fita.
duk abunda ya faru kan idon Mummy tana raku6e jikin window d'akinta, dukda bata san meke faruwa ba taji bak'in cikin rashin jin abunda Aunty take fad'awa Haseenah, dan ganin yanda Haseenah ta nutsu tasan abu mai mahimmanci take sanar da ita.
tsuka taja ta koma ta zauna cike da bak'in ciki, Saratu ce ta dube ta tace" Mummy wai me take fad'a mata ne?"
harara Mummy ta watsa mata tace " ubanki naji, sabida nid'in aljana ce ai dole inji abunda ake fad'a cikin motar ko?"
shuru Saratu tayi batace komai ba, dan tasan inta sake magana duka ne da zagi zai biyo baya.
hakan yayi dai dai da shigowar Haseenah cikin palour d'auke da kaya a hanun ta, wucewa tayi ta ajiye ta koma dan kwaso sauran, dariya Mummy ta saki sannan tace" gida babu se an had'a da rok'o, to duk abunda ake 6oyewa zai fito fili dan uban mutum, inma ciki aka yiwo duk zamu gani, dan mutum shuru shuru tsiyarshi sai Allah"
gaban Haseena ne ya fara dukan tara tara jin Mummy ta ambaci ciki, amma da taji yanda maganar ta dosa sai hankalinta ya kwanta.
ba tare da tace musu komai ba ta wuce ta tafi, abunda yafi k'ona wa Mummy rai kenan tayi magana ak'i tanka mata, Haseenah tana shiga ta kulle k'ofa ta murza key.
Saratu ne ta dubi Mummy, Mummy ma saratun take kallo, ko meye dalilinsu na kallon juna oho....
for comments only 08144932303
Advertisement
- In Serial79 Chapters
The Forest Spirit who sought the Gods
After the Gods of Time, Nature and the Elements created this world, they took a rest under the shade of a tree they created. Thanking their creation for helping them back with its shade, they gave the tree sentience, blessed him and called him a friend. Now the Gods are half-asleep, content with only watching. The world has breathed for millenia, and the blessed tree still watches over the forest around himself. The world has changed and his life comes to an end, surrounded by loneliness. Gathering what's left of his strength, he passes his torch on, in the hope of giving a last goodbye to his friends, wherever they may be and whenever they would see. Meet and follow his first and last creation he passes his will to, a one of a kind forest spirit with... abilities (wouldn't want to spoil too much here now, would I?). Curious and cute, he will travel and meet new people, discovering the world he's in, to try and give a last goodbye to the three creation gods in his dad-tree's place.------It's my first time writing a novel! Or anything of the kind, in fact. So bash me as much as you like (within reason, of course).------This will be a world of humans, humanoïds, beasts, magic, and a heartwarming tale of travels across it. It won't always be butterflies, roses and friendship though, heavy moments are there too. Also : depictions of violence, blood and gore, nudity, strong language, alcohol and other classic +17 stuff. To the reader's discretion.
8 119 - In Serial42 Chapters
Humanity? HELL YEAH!!
After the second rebranding of the entire world, the foreshadowing demands the world may end.But what happens afterwards?Of course everyone goes to hell. The story deals with happenings before, during and after the end of the world after the second rebranding.Mostly it will be about nerds and jocks tho and in a different tone than the Viable 2.
8 1241 - In Serial18 Chapters
The New Destiny ( New Game +)
My name is Harris Cage. Several years ago, a game called The New Destiny was released. A game so successful, it created it own phenomena but also the hardest game in history. It didn't take long for me to get addicted to it. After 5 years of being a shut in, I finally managed to beat this game. As a consequence, I lost my job and love life,but who need those? . I then decided to play the new game + mode and to my surprise, I get plunged into the game world. Well then, how should I survive?
8 182 - In Serial152 Chapters
The Bellators
It is the year 2864, a time where a hundred parallel Earths orbit around a single Supersun, a place full of beauty and wonder. However, deep entrenched in that wonder is chaos, as after a golden age of heroes that had once inspired serenity shattered, wars broke out between people and a mutated population morphed with dangerous abilities, and greater threats loom both old and new, with the only resistance to it all is one frail man. But one spark lights a flame, for there are others out there willing to fight, a second chance at bringing the worlds a freedom to live again. But will a makeshift team who harbor their own curses truly be enough to save what could be tomorrow, or is today all that will ever be?
8 141 - In Serial11 Chapters
World App
A mysterious app of supreme power has drifted in and out of the app stores for years looking for worthy users.
8 160 - In Serial49 Chapters
Awakening (Book 1)
Looking for a spooky read?(Chapters uploaded daily thru Sept! Reworked as a New Adult series so expect some spice!) She'll do anything for vengeance, even confront death itself.Born a healer, nineteen-year-old Colina has been taught to fear dark magic. But now vengeance and survival are her only goals, and she seeks the help of the Death Dealers-dark mages who wield the death arts, drawing their power from the spirits of the unsettled dead.Colina asks a death dealer named Luke for help. Little does she know convincing him to train her will be the easiest part of her journey.Three dark rituals, each more terrifying than the last.If she survives her trials, what will she become?Content and trigger warning: This story contains scenes of violence, death and demonic possession.d
8 252

