《HASEENAH》PAGE 13&14
Advertisement
🌸 *HASEENAH*🌸
story nd written
by👇🏻
Aysher Abbakar (Meerah)
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
#
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-08144932303
follow me on wattpad @Aysherabbakar
*long live pml*
*Dan Allah masu min magana ta private kan cewa in tura musu littafina daga farko suyi hak'uri suna tanbaya a group, in basu samu ba sannan sumin magana, wallahi tura novel daga farko yafimin typing wahala, nagode sossai Allah bar zumunci*
*Meerah novels group 1 nagode sossai da soyayyarku gareni Allah bar k'auna, ina yinku sossai da sossai, meerah heart u guys*
*13-14*
A hankali ta d'ago da idanuwanta dake faman mata zogi dan ganin waye, Haseen ta gani tsaye da farin handkerchief a hanunshi yana mik'a mata, ba musu ta amsa ta fara goge fuskarta.
tsugunawa yayi gaban ta sannan ya fara mata magana kamar haka " kiyi hak'uri ko ban tanbayeki ba nasan aikin mummy ce, ki k'ara hak'uri kan wanda kike yi, komai na duniya me wucewa ne, babu abunda yake tabbata banda ikon Allah, bazan hanaki kuka ba, nasan shi kad'ai ne ze rage miki zogi da rad'ad'in da kikeji, amma dan Allah ki rik'a ragewa kar ya zama miki damuwa kinji?"
gyad'a Mishi kai tayi ba tareda tace komai ba.
nan yace ta mik'e suje chemist a mata dressing d'in wajan.
cikin gida ta wuce tana d'ingisawa ta shiga ciki dan d'auko mayafin ta.
a wajan ta dawo ta sameshi, nan suka shiga mota suka fice a gidan, seda aka mata alluran TT saboda kwalbar sannan aka dressing k'afarta da goshin ta sannan aka bata anti biotics aka sallamesu suka kamo hanyar gida.
a tare suka nufo cikin palour, salatin da Mummy take yine yasasu tsayawa dukansu, dubansu tayi dukansu sannan ta kalli Haseen tace" gidan uban wa ta d'aukeka ta kaika?"
Advertisement
mamakine ya kama Haseen wato bama shi ya d'auketa ba itace ta d'auke shi.
d'aga murya tayi ta nufosu ta dubi Haseenah tace " dan ubanki bakiji abunda nake fad'i bane? nace gidan uban wa kika kaimun d'a?"
tsoro ne ya kama Haseenah nan ta fara 6ari, nufota Mummy tayi da nufin dukan ta, Haseen ne ya sha gabanta yace " haba Mummy, kiga jikin yarinyar nan duk rauni in baki tausaya mata ba ai bazaki k'ara mata ba"
" eh lallai fa, ka kare ta mana, saboda kar ka zagayo da daddare ta hanaka shiga ko? dan iska mara mutunci fetsararre"
tunda Haseen yake ranshi bai ta6a 6aci irinna yau ba, ba abunda ya tsana illa k'azafi, lokaci d'aya idonshi ya kad'a yayi ja, wani mummunan 6acin rai ya ziyarci zuciyarshi, hanunshi da k'afanshi ya hau rawa, ji yake kamar ya kifar da Mummy a wajan saboda 6acin rai, dubanshi Mummy tayi tace " ka bigeni mana da wannan rawar jikin da kake isheshshe, bigeni nace"
lokacin Saratu ta fito daga kitchen d'auke da plate ta yanyanka fruits, isowa wajansu tayi tace " Mummy ina ya kaita wai?"
"yawon iskancin su mana Saratu, inba hakanba ina zasuje da wannan uwar ranan?"
salati Saratu ta kama na munafurci tace" haba yaya Haseen yaushe ka fara bin k'azaman mata? ni wlhy ban....
bata k'arasa ba Haseen ya kife Saratu da wani wawan mari seda ta hantsila ta kifa a gefe, plate d'in hanunta ya fad'i gefe ya tarwatse, baiyi wata-wata ba ya bita da bugu ta ko ina, ihu take tana neman d'auki, Mummy kuwa kururuwa take tana janyoshi tana dukanshi, amma ko sauraronta beyi ba dukan Saratu yake sai kace mai fad'a da sa'ar shi, ganin yana neman hallaka mata 'ya ne ya sata fita da gudu tana k'wallawa mai gadi da driver kira.
Advertisement
da gudu suka nufota ganin yanda ta birkice ko d'an kwali babu akanta, ba abunda take cewa illa " zai kashe ta" tana nuna musu hanyar palour.
da sauri suka shiga dan ganin abunda ke faruwa, lokacin Saratu ko ihun bata iya wa, da k'yar suka ja Haseen suka fito dashi, Mummy kuwa sai kunduma ma iyayenshi ashar take, kallon Mummy yayi kawai yayi k'wafa ya fice, a saba'in ya figi motarshi ya fice a gidan.
ganin haka yasa Haseena sulalewa tayi side d'insu ta mai da k'ofa ta datse dan tasan in tsautsayi yasa ta fitowa yau to sunanta marigayiya.
da gudu Mummy ta nufa Saratu dake kwance shame-shame tana wayyo hanuna wayyo k'afata.
likita Mummy ta kira, nan ya iso ya fara duba ta, targad'e ne hanu da k'afa, da k'yar ta tsaya aka gyara ya nad'e wajan da bandage, nan danan zazza6i ya rufe ta, ya bata magunguna sannan ya tafi.
huci kawai Mummy keyi tama rasa wani mataki zata d'auka kan Haseen.
wayarta ta zaro ta danna numbar k'anwar tata wato Mum Haseen, bugu biyu ta d'aga da fara'arta ta fara fad'in " yaya kardai kicemun aikin malamin nan yayi, an dace knan ko yaya"
Mum Haseen bata ankara ba taji Mummy tace " an dace da uwarki ko? saboda tsabar rashin tarbiya na d'anki, har gida yazo yayi yunk'urin kashemun yarinya kan wata karuwa, to wallahi daga ke harshi senayi maganinku"
tana kaiwa nan ta datse wayar, hankalin Mum Haseen ba k'aramin tashi yayi ba, mayafinta taja ta d'au makullin motarta ta d'au hanyar gidan Mummy.
da sauri-sauri ta shiga palour mum amma ba kowa banda k'aran AC da yake tashi.
hanyar bedroom d'inta ta nufa da niyar dubata ta can, muryar Mummy taji na fad'in " karki yarda ki shigamun d'aki,.ki kama hanya ki fitar a gida ynxu kinji na fad'a miki, inba so kike in rama dukan 'yata a kanki ba"
hak'uri Mum Haseen ta fara bata amma bata kula ta ba, sai ma shigewa da tayi ta barta nan tsaye, ganin haka yasa Mum Haseen rufa mata baya, ahankali ta shiga, Mummy ta hango zaune gefen Saratu ta zabga uban tagumi, yayinda ita kuma taketa rawar sanyi.
kuka Mummy ta fashe da shi ta kalli Mum Haseen tace" ki duba kiga cin mutuncin da Haseen yayi wa Saratu akan wancar yarinya, badan da maza a gidan nan ba wallahi kasheta yayi niyar yi"
cikin rashin fahimta Mum Haseen tace " wata yarinya kike magana ne kan Yaya?"
" wa kuwa inba Haseenah ba"
zaro ido waje tayi tace meya had'a Haseen da 'yar mak'iyarmu kuma ni Hajara?"
" ba fa wani abu bane, yawo ya d'auketa suka fita tun k'arfe biyu sai biyar suka shigo gidannan, dan kawai na tare su ina tanbaya ya hau rawa da jiki kaman zai bigeni, da Saratu tayi magana shine ya hauta da bugu ya huce akanta"
haushine ya kama Mum Haseen jin Mummy tace d'anta ne d'an iska, dan duk yanda ta kai ga rashin gaskiyarta ta san Haseen baya bin mata, ballan tana yabi Haseenah wanda da ganinta dukda son zuciyarsu tasan Haseenah bata yi kama da wannan yaran ba.
amma gudun 6acin ran Mummy yasa ta fara fad'a tana zage-zage, tana fad'in seta sa6a mishi kuma har nan zata sakoshi a gaba seya bada hak'uri, jin haka yasa Mummy ta fara saukowa.
seda ta tabbatar ta gama tsara Mummy sannan ta dubi Mummy tace" nikam yaya lauratu ya maganan maganin da boka ya baki? kin jaraba kuwa?"
harara Mummy ta zabga mata ta nuna Saratu da baki, nan suka fice a d'akin suka nufa bedroom d'in saratu.
Mummy ce ta dubeta tace"......
Advertisement
- In Serial197 Chapters
Cosmosis
Book 3, Through the Cracks, is ongoing. New chapters Monday and Friday at 8:30 PM EST. Join the Discord for discussion and extra goodies! Caleb hasn't had a good day ever since he was abducted into outer space. The food sucks. Nobody understands a word he says. The aliens won't even let him leave his cell. He's driven to fight his captors and escape their clutches. Confronted with hostile aliens, intent on holding him prisoner, Caleb chooses to dive headfirst among forces he can't understand. He'll either learn the eddies of the alien worlds he's stranded in, or else he'll never make it back home. If his hallucination of one of the other abductees can be trusted, maybe they can make it through the trials before them. At least there's no homework?
8 561 - In Serial64 Chapters
Echoes of Valhalla
(Currently Updates at about 3 chapters a week, generally on Tues, Wend, Thur if I can swing it. 2k average words per chapter) As a cashier at Trollhålans combined corner store and gas station, Saga is stuck out in nowhere, Sweden. Having recently lost their mother, they are at their wit's end as they are pushing close to 30 with a dead-end job and only a few friends that they hold semi-reasonable contact with. Most of them have families, jobs, and lives that they do not. In what is a stroke of extraordinarily bad luck, they come face to face with a being not from their world. A creature not supposed to be there. A being that kills them over a bag of sliced bread. Only for Saga to reincarnate in another world. Armed with nothing but a poor temperament and a strange magical guide, they find themselves in a strange, yet oddly familiar new world, surrounded by runic magic, undead, magical beasts, half-giants, and more. Now Saga must find a way to make a new life for themselves while also figuring out how to not end up dead, again. Journey alongside Saga as they find themselves and grow, both as a warrior and as a person. Note: The author has English as their second language and has ADD. Grammatical errors are continuously fixed throughout as they are noticed or pointed out.
8 197 - In Serial11 Chapters
Dragon Carrier
Hidden away from the world and lands of Creavi, Lilith Frostdane eventually breaks free from the shackles of fear her parents held over her. With her newfound freedom, she discovers there are others like her: humans with a dragon spirit dwelling within them. In a land where dragons once ruled, it becomes apparent that her parents weren't the only ones to fear the powerful beasts.
8 146 - In Serial35 Chapters
Lost Child
Otis finds himself lost in an RPG world full of dangers and adventures. Only thing is he does not know what an RPG is or what an NPC is and why he is one. Lucky (or unlucky) for him most of those rules don't apply to him anyway. How will our little rule breaker survive this place? Will he and his new friends ever make it back home? What is Vilenna and why was it ever created to begin with?I plan to update here at least once a week. On my website content will be posted as soon as it is finished and proof read. yougots.wordpress.comThanks for reading.
8 152 - In Serial27 Chapters
The Hunt for Veritas - Book 2 of the Rosethorn Chronicles
Tunio is orphaned by the dark elves completing the break of the curse. Charged by his father to forgive, Tunio seeks to start his own life. He is sent away from Fort Northern Wiles with Captain Hiwot. Onboard he makes friends with Aquillia the Elf, Metilia the half elf, and Gazali the captain’s son. They arrive at Peace Landing the Gnomish island city.King Angularis fears for his own crown, as plots and intrigue begin to surround him. The first of the eight seals have fallen, and the fear is that another will fall. So, he seeks to find the Belt of Veritas which is rumoured to have the ability to grant the wearer the discernment between lies and truth.Anatoli loses his mother and discovers that his father has another son, a true son that he didn’t abandon and seeks revenge on Tunio. First taking his fathers sword and then doing what he can to hamper Tunio even if it means lying to the king.
8 110 - In Serial21 Chapters
MCU'S Ghost
He is Specter Casey Specter Yo Casey Jones was just thirteen When his Uncle made a strange machine Design to see a world unseen When it didn’t work it was a waste space To bad for Casey it blew up in his face Specter Specter When he woke up, he realizes He had shiny silver hair and burning orange eyes He could go through walls turn invisible and fly He was much more interesting than the other guys Specter Specter To bad that explosion caused a rift in space Causing all the bad ghost to attack the human race Specter Specter Than he knew he had to fight He had to become the people ghostly knight Going catch them all he Casey Specter Going to Catch them all he Casey Specter…… Captain America: Kid what are you singing Casey: Oh, Sorry Captain America Sir It my theme song I had to get pumped for the mission. I can’t believe I am going to Germany with bunch of Super Heros. This is the Story Of how 13-year-old Casey Jones become one of the Best Hero’s in the Marvel Universe.
8 82

