《HASEENAH》PAGE 13&14
Advertisement
🌸 *HASEENAH*🌸
story nd written
by👇🏻
Aysher Abbakar (Meerah)
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
#
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-08144932303
follow me on wattpad @Aysherabbakar
*long live pml*
*Dan Allah masu min magana ta private kan cewa in tura musu littafina daga farko suyi hak'uri suna tanbaya a group, in basu samu ba sannan sumin magana, wallahi tura novel daga farko yafimin typing wahala, nagode sossai Allah bar zumunci*
*Meerah novels group 1 nagode sossai da soyayyarku gareni Allah bar k'auna, ina yinku sossai da sossai, meerah heart u guys*
*13-14*
A hankali ta d'ago da idanuwanta dake faman mata zogi dan ganin waye, Haseen ta gani tsaye da farin handkerchief a hanunshi yana mik'a mata, ba musu ta amsa ta fara goge fuskarta.
tsugunawa yayi gaban ta sannan ya fara mata magana kamar haka " kiyi hak'uri ko ban tanbayeki ba nasan aikin mummy ce, ki k'ara hak'uri kan wanda kike yi, komai na duniya me wucewa ne, babu abunda yake tabbata banda ikon Allah, bazan hanaki kuka ba, nasan shi kad'ai ne ze rage miki zogi da rad'ad'in da kikeji, amma dan Allah ki rik'a ragewa kar ya zama miki damuwa kinji?"
gyad'a Mishi kai tayi ba tareda tace komai ba.
nan yace ta mik'e suje chemist a mata dressing d'in wajan.
cikin gida ta wuce tana d'ingisawa ta shiga ciki dan d'auko mayafin ta.
a wajan ta dawo ta sameshi, nan suka shiga mota suka fice a gidan, seda aka mata alluran TT saboda kwalbar sannan aka dressing k'afarta da goshin ta sannan aka bata anti biotics aka sallamesu suka kamo hanyar gida.
a tare suka nufo cikin palour, salatin da Mummy take yine yasasu tsayawa dukansu, dubansu tayi dukansu sannan ta kalli Haseen tace" gidan uban wa ta d'aukeka ta kaika?"
Advertisement
mamakine ya kama Haseen wato bama shi ya d'auketa ba itace ta d'auke shi.
d'aga murya tayi ta nufosu ta dubi Haseenah tace " dan ubanki bakiji abunda nake fad'i bane? nace gidan uban wa kika kaimun d'a?"
tsoro ne ya kama Haseenah nan ta fara 6ari, nufota Mummy tayi da nufin dukan ta, Haseen ne ya sha gabanta yace " haba Mummy, kiga jikin yarinyar nan duk rauni in baki tausaya mata ba ai bazaki k'ara mata ba"
" eh lallai fa, ka kare ta mana, saboda kar ka zagayo da daddare ta hanaka shiga ko? dan iska mara mutunci fetsararre"
tunda Haseen yake ranshi bai ta6a 6aci irinna yau ba, ba abunda ya tsana illa k'azafi, lokaci d'aya idonshi ya kad'a yayi ja, wani mummunan 6acin rai ya ziyarci zuciyarshi, hanunshi da k'afanshi ya hau rawa, ji yake kamar ya kifar da Mummy a wajan saboda 6acin rai, dubanshi Mummy tayi tace " ka bigeni mana da wannan rawar jikin da kake isheshshe, bigeni nace"
lokacin Saratu ta fito daga kitchen d'auke da plate ta yanyanka fruits, isowa wajansu tayi tace " Mummy ina ya kaita wai?"
"yawon iskancin su mana Saratu, inba hakanba ina zasuje da wannan uwar ranan?"
salati Saratu ta kama na munafurci tace" haba yaya Haseen yaushe ka fara bin k'azaman mata? ni wlhy ban....
bata k'arasa ba Haseen ya kife Saratu da wani wawan mari seda ta hantsila ta kifa a gefe, plate d'in hanunta ya fad'i gefe ya tarwatse, baiyi wata-wata ba ya bita da bugu ta ko ina, ihu take tana neman d'auki, Mummy kuwa kururuwa take tana janyoshi tana dukanshi, amma ko sauraronta beyi ba dukan Saratu yake sai kace mai fad'a da sa'ar shi, ganin yana neman hallaka mata 'ya ne ya sata fita da gudu tana k'wallawa mai gadi da driver kira.
Advertisement
da gudu suka nufota ganin yanda ta birkice ko d'an kwali babu akanta, ba abunda take cewa illa " zai kashe ta" tana nuna musu hanyar palour.
da sauri suka shiga dan ganin abunda ke faruwa, lokacin Saratu ko ihun bata iya wa, da k'yar suka ja Haseen suka fito dashi, Mummy kuwa sai kunduma ma iyayenshi ashar take, kallon Mummy yayi kawai yayi k'wafa ya fice, a saba'in ya figi motarshi ya fice a gidan.
ganin haka yasa Haseena sulalewa tayi side d'insu ta mai da k'ofa ta datse dan tasan in tsautsayi yasa ta fitowa yau to sunanta marigayiya.
da gudu Mummy ta nufa Saratu dake kwance shame-shame tana wayyo hanuna wayyo k'afata.
likita Mummy ta kira, nan ya iso ya fara duba ta, targad'e ne hanu da k'afa, da k'yar ta tsaya aka gyara ya nad'e wajan da bandage, nan danan zazza6i ya rufe ta, ya bata magunguna sannan ya tafi.
huci kawai Mummy keyi tama rasa wani mataki zata d'auka kan Haseen.
wayarta ta zaro ta danna numbar k'anwar tata wato Mum Haseen, bugu biyu ta d'aga da fara'arta ta fara fad'in " yaya kardai kicemun aikin malamin nan yayi, an dace knan ko yaya"
Mum Haseen bata ankara ba taji Mummy tace " an dace da uwarki ko? saboda tsabar rashin tarbiya na d'anki, har gida yazo yayi yunk'urin kashemun yarinya kan wata karuwa, to wallahi daga ke harshi senayi maganinku"
tana kaiwa nan ta datse wayar, hankalin Mum Haseen ba k'aramin tashi yayi ba, mayafinta taja ta d'au makullin motarta ta d'au hanyar gidan Mummy.
da sauri-sauri ta shiga palour mum amma ba kowa banda k'aran AC da yake tashi.
hanyar bedroom d'inta ta nufa da niyar dubata ta can, muryar Mummy taji na fad'in " karki yarda ki shigamun d'aki,.ki kama hanya ki fitar a gida ynxu kinji na fad'a miki, inba so kike in rama dukan 'yata a kanki ba"
hak'uri Mum Haseen ta fara bata amma bata kula ta ba, sai ma shigewa da tayi ta barta nan tsaye, ganin haka yasa Mum Haseen rufa mata baya, ahankali ta shiga, Mummy ta hango zaune gefen Saratu ta zabga uban tagumi, yayinda ita kuma taketa rawar sanyi.
kuka Mummy ta fashe da shi ta kalli Mum Haseen tace" ki duba kiga cin mutuncin da Haseen yayi wa Saratu akan wancar yarinya, badan da maza a gidan nan ba wallahi kasheta yayi niyar yi"
cikin rashin fahimta Mum Haseen tace " wata yarinya kike magana ne kan Yaya?"
" wa kuwa inba Haseenah ba"
zaro ido waje tayi tace meya had'a Haseen da 'yar mak'iyarmu kuma ni Hajara?"
" ba fa wani abu bane, yawo ya d'auketa suka fita tun k'arfe biyu sai biyar suka shigo gidannan, dan kawai na tare su ina tanbaya ya hau rawa da jiki kaman zai bigeni, da Saratu tayi magana shine ya hauta da bugu ya huce akanta"
haushine ya kama Mum Haseen jin Mummy tace d'anta ne d'an iska, dan duk yanda ta kai ga rashin gaskiyarta ta san Haseen baya bin mata, ballan tana yabi Haseenah wanda da ganinta dukda son zuciyarsu tasan Haseenah bata yi kama da wannan yaran ba.
amma gudun 6acin ran Mummy yasa ta fara fad'a tana zage-zage, tana fad'in seta sa6a mishi kuma har nan zata sakoshi a gaba seya bada hak'uri, jin haka yasa Mummy ta fara saukowa.
seda ta tabbatar ta gama tsara Mummy sannan ta dubi Mummy tace" nikam yaya lauratu ya maganan maganin da boka ya baki? kin jaraba kuwa?"
harara Mummy ta zabga mata ta nuna Saratu da baki, nan suka fice a d'akin suka nufa bedroom d'in saratu.
Mummy ce ta dubeta tace"......
Advertisement
- In Serial341 Chapters
All Soccer Abilities Are Now Mine!
Woo Hoyoung has returned to the past and gained the ability to steal the abilities of others!
8 1296 - In Serial184 Chapters
A Fractured Song
Just because you’re transported to another world, doesn’t mean you’ll escape from your pain. Abused by her parents, thirteen-year-old Frances only wants to be safe and for her life not to hurt so much. And when she and her class are transported to the magical world of Durannon to fight the monsters invading the human kingdoms and defeat the self-titled Demon King, Frances is presented with a golden opportunity. If she succeeds, Frances will have the home she never had. If she fails, Frances will be summoned back to the home she escaped. Yet, despite her newfound magic and friends, Frances finds that trauma is not so easily lost. She is dogged by her abuse and its physical and invisible scars. Not only does she have to learn magic, she has to survive the nightmares of her past, and wrestle with her feelings of doubt and self-loathing. If she can heal from her trauma, though, she might be able to defeat the Demon King and maybe, just maybe, she can find a home for herself. Beautiful Cover by Rianne Draws (https://twitter.com/RianneDraws) Full cover at: https://www.reddit.com/r/VrensLibrary/comments/iwhsar/a_fractured_song_new_cover_courtesy_of/
8 138 - In Serial53 Chapters
Samurai NOT
By his master's request, Tadayoshi ended his life. Now he must look for the reason behind the request.
8 204 - In Serial6 Chapters
Kazan - The Hero No One Wanted
Shall it be witnessed that a hero came in times unneeded and from a world towering over us, it will mean an alliance with all races to battle this unwanted invader. A hero it will not be called, for these are dark invaders that are written in prophecies old. A hero may be called upon by the energies of humans and demons, but a dark invader is limitless with unforeseeable power... - Maximilian II, Jade Iron Emperor. I have seen it all now, a god is just like the rest of us if stripped from all power. So there isn't a need to be afraid any more, as I will take your place after you leave. So promise me you will return home. - Elianora Hexasy, God's Child. It has happened...a miracle fell upon our lands. - Sophia Alfinedia, Nature Queen. Anti-hero protagonist with a few screws loose, and a plot that will take itself seriously to the very end. Chapters this month: 6/30
8 199 - In Serial24 Chapters
The Love That Define Us {Completed}
Anuraag Agnihotri is a 27 years old NRI, comes India to attend, Wedding of his childhood's best friend, Sivan Rana's younger sister; Diya, who is living with her Uncle's family in a small town of Shimla, after the death of their parents.Unaware of the fact about Diya's wedding, Anuraag develops feelings for her when he first meets her; after he gets to know the truth, it's getting harder for him to live under one roof with her and her family only to see her get married to another man.......The day she supposed to get married, something happens that turns everything upsides down for Diya....the the only choice that is left for her is to get married to her brother's best friend to save her family's reputation. But the question still stands will Diya fall in love with Anuraag or will choose a different path in the end?
8 200 - In Serial117 Chapters
The Original Lamelo Ball Imagines | Book 1
LaMelo Ball Imagines made by a black girl 🤎This imagines book is completed but there is a second entitled "Lamelo Ball Imagines 2"Completed 04/2022
8 156

