《HASEENAH》PAGE 17&18
Advertisement
*HASEENAH*🌸
Story &written
By👇🏻
Aysher Abbakar (meerah)
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
#
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-08144932303
Follow me on
*Long Live Pml*
*17-18*
Da sauri suka nufa wajan Dan ganin abunda ya faru, Haseenah suka gani tsugune a wajan Tana tattara glasses d'in da suka tarwatse, yayin da ruwan da ta zubo a ciki ya wanke sauran maganin da Mummy ta barbad'a, hankalin Mummy ba k'aramin tashi yayi ba, Nan taji wani gumin ba zata ya fara karyo mata, ji tayi kaman ta shak'e Haseenah saboda bak'in ciki, batasan lokacin da ta d'aga hannu ta daidaici bayan Haseenah ta sake mata wani tafi ba, gantsarewa Haseenah tayi saboda azaba, Nan Mummy ta cigaba da banbami tana fad'in
" shegiyar yarinya dak'ik'iya mara tunani tinkiya, wato duk yanda akayi da jaki sai yaci Kara, ku na Kula ba a abun arzik'i daku tunda Baku ga da ba,ja ki bani waje in wuce kafin insa k'afa in yi k'wallo dake"
Mummy ta k'arashe maganar had'e da bangaje Haseenah gefe.
Haseenah Bata Kula Mummy ba saboda tasan dalilin masifar, Umma ma komawa ciki tayi Haseenah Kuma ta cigaba da gyara wajan.
Mummy na komawa d'aki ta lalubo numbar Mum Haseen, tana d'agawa tace mata tazo tana neman ta, ba ta sake jiran abunda zata ce ba ta katse wayar.
Cikin minti goma kuwa saiga ta ta iso, Nan Mummy ta Bata labarin abunda ya faru ta d'aura da cewa " nifa wallahi malamin Nan inaga garin k'uli ya Bamu, Babu wani canji, kina ga na dama kunu na Kai wa matsiyaciyar ba kunya ba tsoron Allah ta tand'e, maimakon inga wani canji ita bacci ma takeji, mtwxxx"
Shuru Mum Haseen tayi ta kasa cewa komai, Mummy ce to sake dubanta a fusace tace" Dan ubanki kinma mayar Dani mahaukaciya kenan, nayi magana kinja kinyi shuru seka ce Wanda nake Miki tafsiri ko? In bazaki iyq komai akai ba tashi ki ficemun daga gida"
Advertisement
Waya Mum Haseen ta zaro ta Danna numbar abokiyar kasuwancin ta, tana d'agawa taji tace" dama yanzu nakeson kiranki Kan ansamu wajan bokan Nan ya za'ayi muje yau Dan inason ganinshi"
"Yauwa fad'uwa tazo dai dai da Zama, dama Kan maganan na kiraki yanzu ki biyo gidan Yaya ta sai mu wuce" Mum Haseen ta Bata amsa.
Lokaci d'aya Mummy ta saki murmushin jin dad'i tace " ko ke fa yanzu naji Batu Mana"
Suna ta zance saiga Hajiya Saudat ta iso, Nan ta Kira Mum Haseen suka fita suka shiga motar ta suka wuce, tafiya suke tun suna hango cikin gari har suka fice, wani kwana suka yanka Banda kukan tsuntsaye ba abunda ke tashi, sunyi kusan tafiyar awa d'aya cikin wanna jeji Amma ko bukka Basu gani ba, Nan fa hankalin Mummy ya fara tashi Amma tayi shuru Banda sak'e 2 ba abunda take, wani kwanar taga an sake yanka an d'au hanya, ga hanyar ba kyau sai bubbuga Kai suke suna gware, can Kan Mummy ya fara ciwo ta ga yamma tayi kusan k'arfe 5:45pm na yamma, gashi taga kaman duniyan zasu bari Amma har yanzu ba.a iso ba, ga uban gudun da Hajiya Saudat ke yi Kai kace sama zata tashi, can Mummy dai ta kasa daurewa tace " wai inane zamuje haka saikace tafiyar ya da shege? Tun Rana muke tafiya har yanzu ba'a iso ba Banga Kuma Ana da niyar tsayawa ba"
Harara Hajiya Saudat ta zabga mata sannan tace" Dalla Malama tsaya, ni da nake driving bance komai ba sai keda kike zaman banza? Wallahi ni inkika ce Zaki mun mita Allah tsakiyar dajin Nan Zaki sauka mun a mota"
Jin haka yasa Mummy Kama bakinta tayi k'wafa sannan tayi shuru.
Dai dai wata tafkekekiyar kogi tayi parking sannan ta dubesu tace " ku fito mu tafi"
Nan fa Mummy da Mum Haseen suka hau kallon kallo Ana zare Ido, ganin Saudatu ta fara gaba Suka sa6a jaka suka bi bayan ta, tattara zani sukaga tayi ta cire takalmi da mayafi ta zuba cikin jaka, Suma da sauri suka cire nasu sukayi yanda tayi, shiga ta fara yi Suma cike da tsoro suka bi bayanta, Kama hanun juna sukayi suna shiga a hankali, haka ruwan ya hauro har kwankwanson su suna tafiya cike da tsoro, ita dai Mummy duk ta karaya ba yanda ta iya ne kawai Amma ta gama sadaukar da rayuwa yau zata bar duniyan, kusan minti talatin suna Abu d'aya daga bisani suka Kai bakin kogin suka fice.
Advertisement
Lokacin kuwa yamma sossai ta kawo Kai Dan ankusa Kiran magriba, Nan suka Chiro takalma suka sa da mayafan su, wani uban dutse suka ga Hajiya Saudatu ta nufa Nan suka fara Hawa da Nishi da wayyo Allah, da Mummy taga mayafin zai Zama mata Kaya Nan ta cire taci d'amara dashi daka ganta kaga 'yar k'auye sak, Hawa suke suna k'arawa, duk gumi ya jik'asu ga yunwa ga k'ishir ruwa, da k'yar suka k'arasa Hawa Nan suka hango bukka, wata ajiyar zuciya duka sukayi, Basu kaiga sauke numfashi ba sukaji wata mummunar murya tana fad'in " karku 6ata mun lokaci"
Ihu Mummy ta saki tana fad'in" wayyo Aljanu"
Dariya taji Muryar ta sake yi seda dajin ya amsa sannan cikin tsawa taji ance" ki rufa Mana baki"
Toshe bakin ta tayi da duka hannayen ta tana furta " wallahi nayi"
Dukansu seda abun ya Basu dariya ganin yanda Mummy ta koma cikin seconds, Nan suka fara takawa a hankali har suka Isa bakin k'ofar bukkar.
Basu Ankara ba suka sake jin wannan Muryar tace" auta shigo min dasu"
Cikin abun da baifi k'iftawar Ido ba sukaji kaman anyi patali da su, sai ganin su sukayi gaban wannan boka mai Kama da aladen jeji, kyarma Mummy ta fara yi ita da Mum Haseen, ganin ya tsare su da Ido ne ya sasu nutsuwar dole.
Sunkuyawa Hajiya Saudatu tayi kamar Mai sujada sannan ta fara rafka mishi kirari Kai da kaji kasan tsuran sa6o ne kawai da barin Kan tafarkin Allah (S.W.A) *Allah ya tsare Mana imaninmu ameen*
Ganin yanda ta durk'ushe yasa Suma suka yi, shi Kuma ya hau yashe hak'ora Yana fad'in
" buk'atar ku ta biya"
D'agowa sukayi Nan ya dube su duka yace " nasan damuwarku"
nuna Mummy yayi yacigaba da cewa " ke akan abokiyar zamanki da Kuma mijinki ne, Amma kashetan da kikeso kiyi bazai yuwa yanzu ba, farkon abunda zakiyi shine shiga tsakaninta da mijinki ya Dena Kula ta"
Da sauri a razane Mummy ta dube shi jin abunda yace, maimaita wa take a ranta, gyad'a Kai yayi yace" hak'ika Yana kula ta Dan Nan bada dad'ewa ba Zaki ga sakamakon had'uwar da suke Nanda wasu 'yan watanni"
Cikin rashin fahimta Mummy tace" wani irin sakamako kenan?"
Girgiza Kai yayi yace" ba a bani Daman fad'an hakan ba, Amma inkika bi hanyoyin da na fad'a Miki ke da kanki Zaki fahimta abunda nake nufi"
Da sauri tace " ayi duk abunda ya Dace boka"
Seda ya gama wasu dube duben shi sannan sukaga an cillo wa kowa k'ulli gaban su, Mummy ya fara kallo yace" wannan k'ullin ki nemi inda kikasan ko yaushe Yana tsallakawa ki binne a wajan, wannan garin Kuma ki barbad'a mishi a abinci daga 'yar har uwar zai tsanesu, wannan Kuma inkin fara al'ada ki kwa6a da jini ki sake tusawa a gaban ki, Kuma kisan duk hanyar da zakibi ya yi kwanciyar aure dake lokacin buk'atar ki ta gama biya sai Kuma ta gaba"
Nan dukansu ya musu bayani, murna ne fal zuciyar Mummy Nan ta kwaso bunch na dubu d'add'aya guda uku ta dire mishi.
Nan suka fice suka d'au hanya, duk tsoron hanya da Mummy keyi duk sai taji ya kau, gudu kawai suke zabgawa lokacin har an dad'e da idar da sallar isha'i, sun k'ure kid'a irinna 'yan matan bariki sai shewa suke, Basu Ankara ba suka hango wash manyan mutane kowannen su d'auke da......
For comments 0814493230
Advertisement
- In Serial38 Chapters
Reborn in abyss
"What would you do if you could go back in time?" After living years in the abyss, Theo is thrown back to the beginning of it all. Creatures, devilish games and the cruel human ambitions; nothing will block his path. He will fight hard to not let hope be taken away from the heart of his friends this time around. Risk yourself, challenge the world and kill... But above all, survive. Welcome to the abyss and have a nice day.
8 494 - In Serial12 Chapters
Shades of the Moon
I'm rewriting this story! I have taken down Arc 2 and Arc 3 already to avoid spoiling my new novel. The only reason I'm keeping the first 10 chapters is nostalgia; the writing is awkward and the story is not plotted out properly, but it's here if anyone wants to compare it to the new one. If you'd like to read a more professionally written version of this story, I highly suggest checking out my Synergy. Synopsis version too-many-to-count: “I see,” Kiona said. “But . . . you’re changing once again, aren’t you?” The entity considered her question, lifting a clawed hand towards the night sky. They observed the back of their hand idly, watching the glowing orange veins pulse alongside their pitch-black exoskeleton. The wind picked up right then, and Kiona shivered—just as much from the cold as from the savage grin on the creature's face. “That’s right,” the entity said, clenching their hand slowly into a fist. They let out a quiet laugh, staring defiantly at the Moon as it rose from behind the clouds. “We are shades, yet not exactly. Not like the others. Here, in this world, we've become something more. We are the Shades of the Moon.” There was a heartbeat of silence, during which Kiona joined the entity in their skygazing. The light-green Moon loomed over the city, shining like the entity's eyes. It promised otherworldly knowledge and terrible secrets. It promised progress. It promised change. In that moment, Kiona couldn't have imagined anything more beautiful. “Shades of the Moon, huh?” she said, smiling a bit. It had a nice ring to it.
8 210 - In Serial15 Chapters
THE SECRET OF THE 23 DOORS
A girl name Sia whose having a continuous nightmares because of her serial killer stepfather. He killed her mother. he's dead but she feels like he's soul is still alive somewhere. tired of this things she goes on a trip. unfortunately she had to stay at a place.that place was her stepfather's biggest secret which no one knows. When that mystery was uncovered it was unbelievable.
8 197 - In Serial7 Chapters
IM A SNAKE!!
Im riding to school in my bus all a sudden Razor Wheel Kun Appears and takes my life and WTH IM A SNAKE Now avaliable on webnovel
8 116 - In Serial8 Chapters
My Desires
Read it and find out :)
8 178 - In Serial32 Chapters
YOONMIN ¦ before debut
(COMPLETED - under editing)"We were perfectly fine without you.".....Jimin's the new and final member of the BTS lineup.Namjoon, Jin, Hoseok, Taehyung and Jungkook all have their opinions on the new guy, but Yoongi thinks otherwise......"Please don't go, you're all I have left."- Tea
8 234

