《HASEENAH》PAGE 17&18
Advertisement
*HASEENAH*🌸
Story &written
By👇🏻
Aysher Abbakar (meerah)
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
#
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-08144932303
Follow me on
*Long Live Pml*
*17-18*
Da sauri suka nufa wajan Dan ganin abunda ya faru, Haseenah suka gani tsugune a wajan Tana tattara glasses d'in da suka tarwatse, yayin da ruwan da ta zubo a ciki ya wanke sauran maganin da Mummy ta barbad'a, hankalin Mummy ba k'aramin tashi yayi ba, Nan taji wani gumin ba zata ya fara karyo mata, ji tayi kaman ta shak'e Haseenah saboda bak'in ciki, batasan lokacin da ta d'aga hannu ta daidaici bayan Haseenah ta sake mata wani tafi ba, gantsarewa Haseenah tayi saboda azaba, Nan Mummy ta cigaba da banbami tana fad'in
" shegiyar yarinya dak'ik'iya mara tunani tinkiya, wato duk yanda akayi da jaki sai yaci Kara, ku na Kula ba a abun arzik'i daku tunda Baku ga da ba,ja ki bani waje in wuce kafin insa k'afa in yi k'wallo dake"
Mummy ta k'arashe maganar had'e da bangaje Haseenah gefe.
Haseenah Bata Kula Mummy ba saboda tasan dalilin masifar, Umma ma komawa ciki tayi Haseenah Kuma ta cigaba da gyara wajan.
Mummy na komawa d'aki ta lalubo numbar Mum Haseen, tana d'agawa tace mata tazo tana neman ta, ba ta sake jiran abunda zata ce ba ta katse wayar.
Cikin minti goma kuwa saiga ta ta iso, Nan Mummy ta Bata labarin abunda ya faru ta d'aura da cewa " nifa wallahi malamin Nan inaga garin k'uli ya Bamu, Babu wani canji, kina ga na dama kunu na Kai wa matsiyaciyar ba kunya ba tsoron Allah ta tand'e, maimakon inga wani canji ita bacci ma takeji, mtwxxx"
Shuru Mum Haseen tayi ta kasa cewa komai, Mummy ce to sake dubanta a fusace tace" Dan ubanki kinma mayar Dani mahaukaciya kenan, nayi magana kinja kinyi shuru seka ce Wanda nake Miki tafsiri ko? In bazaki iyq komai akai ba tashi ki ficemun daga gida"
Advertisement
Waya Mum Haseen ta zaro ta Danna numbar abokiyar kasuwancin ta, tana d'agawa taji tace" dama yanzu nakeson kiranki Kan ansamu wajan bokan Nan ya za'ayi muje yau Dan inason ganinshi"
"Yauwa fad'uwa tazo dai dai da Zama, dama Kan maganan na kiraki yanzu ki biyo gidan Yaya ta sai mu wuce" Mum Haseen ta Bata amsa.
Lokaci d'aya Mummy ta saki murmushin jin dad'i tace " ko ke fa yanzu naji Batu Mana"
Suna ta zance saiga Hajiya Saudat ta iso, Nan ta Kira Mum Haseen suka fita suka shiga motar ta suka wuce, tafiya suke tun suna hango cikin gari har suka fice, wani kwana suka yanka Banda kukan tsuntsaye ba abunda ke tashi, sunyi kusan tafiyar awa d'aya cikin wanna jeji Amma ko bukka Basu gani ba, Nan fa hankalin Mummy ya fara tashi Amma tayi shuru Banda sak'e 2 ba abunda take, wani kwanar taga an sake yanka an d'au hanya, ga hanyar ba kyau sai bubbuga Kai suke suna gware, can Kan Mummy ya fara ciwo ta ga yamma tayi kusan k'arfe 5:45pm na yamma, gashi taga kaman duniyan zasu bari Amma har yanzu ba.a iso ba, ga uban gudun da Hajiya Saudat ke yi Kai kace sama zata tashi, can Mummy dai ta kasa daurewa tace " wai inane zamuje haka saikace tafiyar ya da shege? Tun Rana muke tafiya har yanzu ba'a iso ba Banga Kuma Ana da niyar tsayawa ba"
Harara Hajiya Saudat ta zabga mata sannan tace" Dalla Malama tsaya, ni da nake driving bance komai ba sai keda kike zaman banza? Wallahi ni inkika ce Zaki mun mita Allah tsakiyar dajin Nan Zaki sauka mun a mota"
Jin haka yasa Mummy Kama bakinta tayi k'wafa sannan tayi shuru.
Dai dai wata tafkekekiyar kogi tayi parking sannan ta dubesu tace " ku fito mu tafi"
Nan fa Mummy da Mum Haseen suka hau kallon kallo Ana zare Ido, ganin Saudatu ta fara gaba Suka sa6a jaka suka bi bayan ta, tattara zani sukaga tayi ta cire takalmi da mayafi ta zuba cikin jaka, Suma da sauri suka cire nasu sukayi yanda tayi, shiga ta fara yi Suma cike da tsoro suka bi bayanta, Kama hanun juna sukayi suna shiga a hankali, haka ruwan ya hauro har kwankwanson su suna tafiya cike da tsoro, ita dai Mummy duk ta karaya ba yanda ta iya ne kawai Amma ta gama sadaukar da rayuwa yau zata bar duniyan, kusan minti talatin suna Abu d'aya daga bisani suka Kai bakin kogin suka fice.
Advertisement
Lokacin kuwa yamma sossai ta kawo Kai Dan ankusa Kiran magriba, Nan suka Chiro takalma suka sa da mayafan su, wani uban dutse suka ga Hajiya Saudatu ta nufa Nan suka fara Hawa da Nishi da wayyo Allah, da Mummy taga mayafin zai Zama mata Kaya Nan ta cire taci d'amara dashi daka ganta kaga 'yar k'auye sak, Hawa suke suna k'arawa, duk gumi ya jik'asu ga yunwa ga k'ishir ruwa, da k'yar suka k'arasa Hawa Nan suka hango bukka, wata ajiyar zuciya duka sukayi, Basu kaiga sauke numfashi ba sukaji wata mummunar murya tana fad'in " karku 6ata mun lokaci"
Ihu Mummy ta saki tana fad'in" wayyo Aljanu"
Dariya taji Muryar ta sake yi seda dajin ya amsa sannan cikin tsawa taji ance" ki rufa Mana baki"
Toshe bakin ta tayi da duka hannayen ta tana furta " wallahi nayi"
Dukansu seda abun ya Basu dariya ganin yanda Mummy ta koma cikin seconds, Nan suka fara takawa a hankali har suka Isa bakin k'ofar bukkar.
Basu Ankara ba suka sake jin wannan Muryar tace" auta shigo min dasu"
Cikin abun da baifi k'iftawar Ido ba sukaji kaman anyi patali da su, sai ganin su sukayi gaban wannan boka mai Kama da aladen jeji, kyarma Mummy ta fara yi ita da Mum Haseen, ganin ya tsare su da Ido ne ya sasu nutsuwar dole.
Sunkuyawa Hajiya Saudatu tayi kamar Mai sujada sannan ta fara rafka mishi kirari Kai da kaji kasan tsuran sa6o ne kawai da barin Kan tafarkin Allah (S.W.A) *Allah ya tsare Mana imaninmu ameen*
Ganin yanda ta durk'ushe yasa Suma suka yi, shi Kuma ya hau yashe hak'ora Yana fad'in
" buk'atar ku ta biya"
D'agowa sukayi Nan ya dube su duka yace " nasan damuwarku"
nuna Mummy yayi yacigaba da cewa " ke akan abokiyar zamanki da Kuma mijinki ne, Amma kashetan da kikeso kiyi bazai yuwa yanzu ba, farkon abunda zakiyi shine shiga tsakaninta da mijinki ya Dena Kula ta"
Da sauri a razane Mummy ta dube shi jin abunda yace, maimaita wa take a ranta, gyad'a Kai yayi yace" hak'ika Yana kula ta Dan Nan bada dad'ewa ba Zaki ga sakamakon had'uwar da suke Nanda wasu 'yan watanni"
Cikin rashin fahimta Mummy tace" wani irin sakamako kenan?"
Girgiza Kai yayi yace" ba a bani Daman fad'an hakan ba, Amma inkika bi hanyoyin da na fad'a Miki ke da kanki Zaki fahimta abunda nake nufi"
Da sauri tace " ayi duk abunda ya Dace boka"
Seda ya gama wasu dube duben shi sannan sukaga an cillo wa kowa k'ulli gaban su, Mummy ya fara kallo yace" wannan k'ullin ki nemi inda kikasan ko yaushe Yana tsallakawa ki binne a wajan, wannan garin Kuma ki barbad'a mishi a abinci daga 'yar har uwar zai tsanesu, wannan Kuma inkin fara al'ada ki kwa6a da jini ki sake tusawa a gaban ki, Kuma kisan duk hanyar da zakibi ya yi kwanciyar aure dake lokacin buk'atar ki ta gama biya sai Kuma ta gaba"
Nan dukansu ya musu bayani, murna ne fal zuciyar Mummy Nan ta kwaso bunch na dubu d'add'aya guda uku ta dire mishi.
Nan suka fice suka d'au hanya, duk tsoron hanya da Mummy keyi duk sai taji ya kau, gudu kawai suke zabgawa lokacin har an dad'e da idar da sallar isha'i, sun k'ure kid'a irinna 'yan matan bariki sai shewa suke, Basu Ankara ba suka hango wash manyan mutane kowannen su d'auke da......
For comments 0814493230
Advertisement
- In Serial11 Chapters
Evolved
in 2021 a secret government facility underneath a chemical plant is housing gene 175 aka the evolution gene. when the chemical plant blows up, it unleashes gene 175 upon the world. after laying dormant for a year, gene 175 activates; thus begins the apocalypse. people either evolve to gain power, or they deviate becoming abhorred. ten years into the apocalypse Noah Brookhart, who lost his family, now loses his life. in the ten years he experienced the apocolypse, he never once "awakened" his powers. after dying he wakes up nearly 10 years in the past (about a month after the apocolypse started,) after which, he evolves to stage 2 (which he never managed to do before,) discovering his power. now that he has a new found streangth can he avoid his bleak future?
8 137 - In Serial12 Chapters
The Human Who Became A Definitive Golem.
After falling off the edge of the hills, Ryker found himself in another world. Now in the body of a "golem", Ryker will have to explore this new place, struggling to survive and grow strong enough to deal with the dangers of this mysterious land and the possible adversities that will come to him.
8 69 - In Serial10 Chapters
Blackened Blossoms
Bloodthirsty and cruel to the bone, Tears make it their mission to sow discord and horror everywhere they go. But they weren't always that way, no. Tears used to be the light of the lands, apprehending evildoers and lifting up the helpless. Until someone corrupted their very nature... Newborn and not yet affected by the corruption, one Tear is on a desperate mission to save her sisters. Publishing schedule currently under review
8 207 - In Serial13 Chapters
Clusterfuck
Mia is a bounty hunter—ok, fine, that's a lie. Mia wants to be a bounty hunter, which didn't quite work out in the past few years, but now she finally received her first proper job. Her mark is a fugitive drug dealer called Lara Milbourne, and she has three days to find her. Easy. ---------------------- This book is written by two queer women, for queer women and anyone else that may take enjoyment in it. New chapters will be added every Monday. (Yes, we're giving you a reason to dislike Mondays a little bit less) Do you want more now? We are 7 chapters ahead on Neovel. Just Google "Clusterfuck Neovel" to find it!
8 200 - In Serial141 Chapters
That Time I Got Reborn In Another World With My Black Friend
What happens when a goddess summons more people than expected? Well, this story explains just that. This is the story of two college students, Will and Quincy, who meet a sudden and unfortunate end. Now they must embark on an adventure to defeat the demon king to fulfill an age old prophecy. The two adventurers, one willing, the other unwilling, end up facing chaos and pain at every step. Arc 1: Chapters 1-29: The Introduction Arc Arc 2: Chapters 30-77: The Ayana Rebellion/Reaper Arc Arc 3: ??? Arc 4: ??? Arc 5: ??? Big thanks to Momonon for drawing the cover! I loved how it turned out. If you ever need to commission an artist, check them out on Sketchmob.com
8 222 - In Serial27 Chapters
Stonequiet: A Proficiomancer in Another World
It was in a dream that I heard her voice. She, a goddess, had offered me a place to be her champion and heal my pain, but I declined. Even with that someone else decided to take me away regardless of my choice. It was not long before I realized I was not the only one taken. Eleven of us were forced into this world in order to fight monsters. My girlfriend and her best friend were taken as well. I had little interest in fighting for a nation that would kidnap people from another world. So by the grace of god, I was given access to the Grimoire Magic System in which a game-like system was offered to me. It even included an in-game shop. With this we will find a way back to Earth. Extra Tags: Cheat Skill, OP-MC, Harem, Crafting.
8 64

