《HASEENAH》PAGE 19&20
Advertisement
🌸 *HASEENAH*🌸
Story &written
By👇🏻
Aysher Abbakar (meerah)
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
#
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-08144932303
Follow me on
*Long Live Pml*
'''ban san taya zan fara godiya ba,kwanana biyu banyi typing ba dalilin rasuwar da aka mun,Amma yanda mutane sukemun magana yasa dole na zanyi Koda kadanne,na gode sossai da ta'aziyar ku gareni Allah bar kauna da zumunci,Koda yaushe Kuna raina'''
*19-20*
Ko wannen su d'auke da adda su shida, wata uwar birki Hajiya Saudatu ta taka saida motar ta juya dasu, jikin su gaba d'aya rawa yake barin ma Mummy da tuni ta hau kyarma, nuni d'aya daga cikin su ya musu akan su sauko, Nan suka hau kallon kallo, daka musu tsawa ya sake yi Wanda ya dad'a firgita su, da sauri suka 6alle murfin motar suka fito, ganin irin shigan da sukayi ya tabbatar musu da cewa ba mutanen arzik'i bane dukda yawan shekarun su, wasu zaro zaron 'yan kunne Hajiya Saudatu ta saka Wanda ya sauko har kafad'un ta, ga hujin hancin ta biyu a jere ta ko wani gefe, Mummy kuwa taci bleaching har ya wuce misali, Dan in ka kalli k'afan ta da hanunta bazaka ce itace me wannan fuskar ba.
Mum Haseen kuwa Riga da skirt taci ta buga wani uban rolling ta cakka d'an kwali, hakan yasa su bushewa da dariya ya dubesu yace "ku yi kneeldown",
duban su Mummy tayi tace "menene nildawun kuma?"
Dariya suka saka yayin da bak'in ciki ya Kama Hajiya Saudatu ta dube ta tace
" ai ko Baki shiga aji ba a tunanin Zaki Gane abunda suke nufi jaka kawai"
Ta k'arashe maganar had'e da janyo Mummy k'asa Nan ta kife, d'aya daga cikin su ne ya dube su yace " gidan uban wa kuka fito a Daren Nan Kuma cikin jejin Nan?"
Advertisement
Shuru dukan su sukayi sun rasa Mai zasu ce, kallon wani a cikin su yayi da Ido Aiko basu Ankara ba sukaji d'aya ya d'auke Mummy da Mari da take gaba, ihu ta saki tana "wayyo Allah wallahi ban sani ba ku tanbayi wannan zata muku bayani"
Ta nuna Hajiya Saudatu, d'aga musu hannu Hajiya Saudatu tayi sannan tace" bayin Allah me kuke buk'ata?"
Dariya sukayi sannan babban su yace" da tuntuni abunda kukayi magana kenan da Baku Kai wannan matsayin ba"
Mik'ewa Hajiya Saudatu tayi ta shiga motar ta bud'e jakar Mummy da Mum Haseen ta tattaro kap k'udin ciki kusan dubu dari biyu tazo ta mik'a musu, kar6a sukayi sannan sukace " Zaku iya tafiya ku biyun Nan"
Suka nuna Hajiya Saudatu da Mum Haseen.
Duban su Mummy tayi a razane tace" Dan Allah Nima ku barni in tafi"
Nan ta hau kuka kamar yarinya, d'aya daga cikin su ne yace" su ja motar sukai zuwa can, ya nuna wata bishiya, kekuma seki bisu da tsallen kwad'o"
Ai su Hajiya Saudatu da Mum Haseen na jin Haka suka shige mota da gudu suka barta Nan tsugune.
Nan Mummy ta hau yin tsallen kwad'o biyu tayi ta kife wajan, juyowa tayi ta ga suna magana ko takalmi Bata tsaya sawa ba ta mik'e da k'yar ta arta da gudu.
Dariya sukeyi sossai dukan su, Mummy ko kulasu Bata yiba damuwar ta ta ganta cikin motar ne.
Tana shiga motar Hajiya Saudatu ta bushe da dariya tace " a dai koma makaranta saboda 6acin Rana.
Bata kula ta ba sai haki take tana wangale hanci, takai kusan minti biyar sannan ta daidai ta, duban su tayi tace" koma menene tunda na tsira da abunda boka ya bani shikenan, bashi zai hanani dawowa ba indai buk'ata ta biya"
Dariya sukayi sannan Hajiya Saudatu tace" dama Waze ja da d'iyar makafi mabarata Kuma 'yar jagora, Kinga jiya Kinga yau saura gobe, duk Wanda ya ganki ai yaga manyan arna Kuma wahalalliya, keda kika san layi- layi na titina da shagona ai zakiyi abunda yafi haka ma"
Advertisement
Haushi ne ya turnuk'e Mummy Amma ta kasa furta komai Dan tasan tana magana ba mutunci zata ajiye ta cikin wannan tsakiyar dajin.
Sai wajan k'arfe 10:30 na dare suka hau Kan titi, zuwa 11:00 kuwa sai ga su k'ofar gidan Mummy, duban Hajiya Saudatu tayi dukda haushin da take ji tace " na gode sossai fa sai kin jini"
Ko Kula Mum Haseen Bata yi ba ta figi jakar ta tayi ciki.
Gidan shuru ba kowa hakan ya sata wucewa side d'inta da sauri, d'akin saratu ta fara lek'awa ta ganta zaune ta buga tagumi, Nan ta had'e Rai, duban ta Saratu tayi tace"Mummy Ina Kika shiga tun safe"
A tak'aice Mummy tace" gidan uwar wata"
Bata sake bi ta kanta ba tayi wucewar ta d'aki, Allah Allah take asuba tayi ta fara aiwatar da aikin ta.
Kasa bacci tayi Kota Fara sai ta mik'e ta duba agogo, a haka har asuba tayi, tana jin ficewar Abba zuwa masallaci ta d'auro zani Kan kayan baccin ta ta fito, side d'inshi ta nufa cikin sand'a Nan ta tsaya dai dai bakin shiga palour shi, rasa ta inda zata fara tayi Dan ganin wajan duk mamaye yake da tiles, takai kusan 5 mins Nan tsaye tana neman mafita, jin anyi sallama a masallaci ne ya firgitar da ita Dan tasan yanzu mijinta zai shigo, Nan wata dabara ta fad'o mata, Wani dariyar mugun ta ta saki sannan ta tsuguna ta d'aga k'asan carpet din ta tura maganin sannan ta juya da sauri ta koma ta la6e, Nan kuwa ya shigo hanun shi rik'e da carbi, Yana wuce k'ofar d'akin yaji zuciyar shi tayi bak'ikk'irin, zuciyar shi tayi zafi kamar an chaka mishi mashi haka yaji, lokaci d'aya yaji ranshi ya 6aci, wata tsuka ya ja Wanda baisan dalilin ba yayi k'wafa sannan ya wuce ciki had'e da banko k'ofar.
Wata tsalle Mummy ta daka ta murna ta taka rawa Wanda Bata San ma ta iya shi ba sannan ta wuce ciki tana Allah Allah gari ya waye taga irin dramar da za a kwashe.
Wajan k'arfe 9 da yake yau weekend ne Mummy taci wanka ta nufo d'akin su Haseenah, Nan ta fara knocking, da sauri Haseenah ta diro daga gado ta sako slifas ta fito, zubewa tayi gaban Mummy tana kwasar gaisuwa, ko amsawa Mummy batayi ba tace " ki shiga kitchen ki had'a mana breakfast da Abbanki inkin gama kizo ki jera a dinning.
Da sauri Haseenah ta mik'e ta wuce kitchen ta hau aiki, tana gama ta jere su cikin babban basket ta d'auka ta nufa wajan dinning, Abba ta hango yanata faman dariya ko me Mummy ke fad'a mishi oho.
Yana ganin Haseenah ta nufo yanda suke ya had'e Rai kaman Bai ta6a dariya ba, tsuka ya ja ya kau da kai, Kai kace wani mak'iyin shi ya gani.
Tana zuwa ta gaidashi Amma ko kallonta baiyi ba, ta sake gaidashi karo na biyu tunanin ta ko baiji bane.
Wata tsawa ya daka mata sannan yace" ki ajiye da Allah ki 6acemun a nan"
Razana tayi da firgici ya sata tsayawa cak Nan ita batayi baya ba Kuma batayi gaba ba, k'afan shi ya saka Nan ya tokare ta ta kife wajan, jini ne ya fara zuba a hancin ta, a firgice ta mik'e ta zuba a guje ta bar wajan, saboda tsabar rikicewa ma bata san inda ta nufa ba.....
For comments 08144932303
Advertisement
- In Serial54 Chapters
Reborn in Another World as a (Colorless) Demon Prince
He made his break through and proved the naysayers wrong. But just as everything in life was falling into place, he died. A strange being meets him in the in-between, and he is given a second chance at life. The world he's reborn into in full of wonderous monsters and adventures to be had. However, he's not human anymore, but a demon. And not just any demon, but a Colorless prince. Even worse, demons and humans don't exactly...get along. War looms between the two nations, and threatens to capsize his life into chaos and blood. If he wants to make anything of himself, he will need to work very, very hard. It's a shame he's not sure what to do or where he wants to go. Please note: The story is a slow burn and only starts to pick up after chapter 8. Also, if you like Re:Zero, give this one a shot. It is also a weak to strong story.
8 199 - In Serial11 Chapters
Strongest Immortal Ninja with a Naruto System
Watch Fang Li, reincarnated into another world as an orphan with weak cultivation talent who shares the same name as him, he is granted a heaven defying system that can give him abilities and tools from the naruto universe. I don't own anything from the naruto franchise
8 172 - In Serial15 Chapters
A Beginning and its End
The One that was not created, but exists. Alone in the void. Until that being created more. During creation, that being felt things. Boredom. Anticipation. Until the Old One came to the world it helped to create. But, he doesn't remember anything. Fate wouldn't allow it.
8 155 - In Serial13 Chapters
Drama Club [Rannett]
[ "Why don't you introduce yourself?" Eula suggested, gesturing for him to come to the front of the class. He timidly walked up to the front of the class, picking up the piece of chalk in a cup next to the board. He wrote down his name. "My name... is Razor. I'm turning seventeen soon. And uh... I just transferred here.""He's shy. Very shy." Bennett whispered to Fischl as she nodded in agreement. "True.""But... he seems interesting, nonetheless." ]Modern AU. Pairing: Bennett/Razor.Cover art is not mine, credits to @_nnaao4 on twt
8 56 - In Serial11 Chapters
In your hands (vkook)
داستان ما دربارهی جئون جانگکوک پسری پاک و مظلوم و کیم تهیونگ رییس بزرگترین باند مافیای سئول که از قضا عاشق و دلباخته ی جئون جانگکوک داستان ماست. تهیونگ بعد از اعتراف به جانگکوک به عنوان دوست پسر رسمیش شناخته میشه ولی.........چی میشه اگه جانگکوک شغل واقعیه تهیونگ رو بفهمه و همه چی از هم بپاشه و جانگکوک دیگه تهیونگ رو نخواد؟؟؟؟؟؟؟ به نظرتون تهیونگ دست برمیداره؟؟؟معلومه که نه......کیم تهیونگ هیچوقت چیزی که ماله خودشه رو از دست نمیده.جانگکوک سعی میکنه خودش رو نجات بده ولی اگه فقط خودش بود این قضیه امکان داشت.ولی الان که پای یه بچه وسطه چی؟؟؟؟؟؟درسته ....... بچه ی تهیونگ و جانگکوک • نام فیک : in your hands • ژانر : امپرگ ، مافیایی ، انگست ، اسمات • نویسنده : melina• روز های اپ : یکشنبه ها / چهارشنبه ها•کاپل : دوورژن kookv و vkook
8 99 - In Serial20 Chapters
Min Kjære. -TordTom
"What the fuck have you've done?"-TordTom-Paultryk(I ship the characters only.)*Future AU. - lots of angst. enjoy. ʕ'• ᴥ•̥'ʔ
8 208

