《HASEENAH》PAGE 19&20
Advertisement
🌸 *HASEENAH*🌸
Story &written
By👇🏻
Aysher Abbakar (meerah)
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
#
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-08144932303
Follow me on
*Long Live Pml*
'''ban san taya zan fara godiya ba,kwanana biyu banyi typing ba dalilin rasuwar da aka mun,Amma yanda mutane sukemun magana yasa dole na zanyi Koda kadanne,na gode sossai da ta'aziyar ku gareni Allah bar kauna da zumunci,Koda yaushe Kuna raina'''
*19-20*
Ko wannen su d'auke da adda su shida, wata uwar birki Hajiya Saudatu ta taka saida motar ta juya dasu, jikin su gaba d'aya rawa yake barin ma Mummy da tuni ta hau kyarma, nuni d'aya daga cikin su ya musu akan su sauko, Nan suka hau kallon kallo, daka musu tsawa ya sake yi Wanda ya dad'a firgita su, da sauri suka 6alle murfin motar suka fito, ganin irin shigan da sukayi ya tabbatar musu da cewa ba mutanen arzik'i bane dukda yawan shekarun su, wasu zaro zaron 'yan kunne Hajiya Saudatu ta saka Wanda ya sauko har kafad'un ta, ga hujin hancin ta biyu a jere ta ko wani gefe, Mummy kuwa taci bleaching har ya wuce misali, Dan in ka kalli k'afan ta da hanunta bazaka ce itace me wannan fuskar ba.
Mum Haseen kuwa Riga da skirt taci ta buga wani uban rolling ta cakka d'an kwali, hakan yasa su bushewa da dariya ya dubesu yace "ku yi kneeldown",
duban su Mummy tayi tace "menene nildawun kuma?"
Dariya suka saka yayin da bak'in ciki ya Kama Hajiya Saudatu ta dube ta tace
" ai ko Baki shiga aji ba a tunanin Zaki Gane abunda suke nufi jaka kawai"
Ta k'arashe maganar had'e da janyo Mummy k'asa Nan ta kife, d'aya daga cikin su ne ya dube su yace " gidan uban wa kuka fito a Daren Nan Kuma cikin jejin Nan?"
Advertisement
Shuru dukan su sukayi sun rasa Mai zasu ce, kallon wani a cikin su yayi da Ido Aiko basu Ankara ba sukaji d'aya ya d'auke Mummy da Mari da take gaba, ihu ta saki tana "wayyo Allah wallahi ban sani ba ku tanbayi wannan zata muku bayani"
Ta nuna Hajiya Saudatu, d'aga musu hannu Hajiya Saudatu tayi sannan tace" bayin Allah me kuke buk'ata?"
Dariya sukayi sannan babban su yace" da tuntuni abunda kukayi magana kenan da Baku Kai wannan matsayin ba"
Mik'ewa Hajiya Saudatu tayi ta shiga motar ta bud'e jakar Mummy da Mum Haseen ta tattaro kap k'udin ciki kusan dubu dari biyu tazo ta mik'a musu, kar6a sukayi sannan sukace " Zaku iya tafiya ku biyun Nan"
Suka nuna Hajiya Saudatu da Mum Haseen.
Duban su Mummy tayi a razane tace" Dan Allah Nima ku barni in tafi"
Nan ta hau kuka kamar yarinya, d'aya daga cikin su ne yace" su ja motar sukai zuwa can, ya nuna wata bishiya, kekuma seki bisu da tsallen kwad'o"
Ai su Hajiya Saudatu da Mum Haseen na jin Haka suka shige mota da gudu suka barta Nan tsugune.
Nan Mummy ta hau yin tsallen kwad'o biyu tayi ta kife wajan, juyowa tayi ta ga suna magana ko takalmi Bata tsaya sawa ba ta mik'e da k'yar ta arta da gudu.
Dariya sukeyi sossai dukan su, Mummy ko kulasu Bata yiba damuwar ta ta ganta cikin motar ne.
Tana shiga motar Hajiya Saudatu ta bushe da dariya tace " a dai koma makaranta saboda 6acin Rana.
Bata kula ta ba sai haki take tana wangale hanci, takai kusan minti biyar sannan ta daidai ta, duban su tayi tace" koma menene tunda na tsira da abunda boka ya bani shikenan, bashi zai hanani dawowa ba indai buk'ata ta biya"
Dariya sukayi sannan Hajiya Saudatu tace" dama Waze ja da d'iyar makafi mabarata Kuma 'yar jagora, Kinga jiya Kinga yau saura gobe, duk Wanda ya ganki ai yaga manyan arna Kuma wahalalliya, keda kika san layi- layi na titina da shagona ai zakiyi abunda yafi haka ma"
Advertisement
Haushi ne ya turnuk'e Mummy Amma ta kasa furta komai Dan tasan tana magana ba mutunci zata ajiye ta cikin wannan tsakiyar dajin.
Sai wajan k'arfe 10:30 na dare suka hau Kan titi, zuwa 11:00 kuwa sai ga su k'ofar gidan Mummy, duban Hajiya Saudatu tayi dukda haushin da take ji tace " na gode sossai fa sai kin jini"
Ko Kula Mum Haseen Bata yi ba ta figi jakar ta tayi ciki.
Gidan shuru ba kowa hakan ya sata wucewa side d'inta da sauri, d'akin saratu ta fara lek'awa ta ganta zaune ta buga tagumi, Nan ta had'e Rai, duban ta Saratu tayi tace"Mummy Ina Kika shiga tun safe"
A tak'aice Mummy tace" gidan uwar wata"
Bata sake bi ta kanta ba tayi wucewar ta d'aki, Allah Allah take asuba tayi ta fara aiwatar da aikin ta.
Kasa bacci tayi Kota Fara sai ta mik'e ta duba agogo, a haka har asuba tayi, tana jin ficewar Abba zuwa masallaci ta d'auro zani Kan kayan baccin ta ta fito, side d'inshi ta nufa cikin sand'a Nan ta tsaya dai dai bakin shiga palour shi, rasa ta inda zata fara tayi Dan ganin wajan duk mamaye yake da tiles, takai kusan 5 mins Nan tsaye tana neman mafita, jin anyi sallama a masallaci ne ya firgitar da ita Dan tasan yanzu mijinta zai shigo, Nan wata dabara ta fad'o mata, Wani dariyar mugun ta ta saki sannan ta tsuguna ta d'aga k'asan carpet din ta tura maganin sannan ta juya da sauri ta koma ta la6e, Nan kuwa ya shigo hanun shi rik'e da carbi, Yana wuce k'ofar d'akin yaji zuciyar shi tayi bak'ikk'irin, zuciyar shi tayi zafi kamar an chaka mishi mashi haka yaji, lokaci d'aya yaji ranshi ya 6aci, wata tsuka ya ja Wanda baisan dalilin ba yayi k'wafa sannan ya wuce ciki had'e da banko k'ofar.
Wata tsalle Mummy ta daka ta murna ta taka rawa Wanda Bata San ma ta iya shi ba sannan ta wuce ciki tana Allah Allah gari ya waye taga irin dramar da za a kwashe.
Wajan k'arfe 9 da yake yau weekend ne Mummy taci wanka ta nufo d'akin su Haseenah, Nan ta fara knocking, da sauri Haseenah ta diro daga gado ta sako slifas ta fito, zubewa tayi gaban Mummy tana kwasar gaisuwa, ko amsawa Mummy batayi ba tace " ki shiga kitchen ki had'a mana breakfast da Abbanki inkin gama kizo ki jera a dinning.
Da sauri Haseenah ta mik'e ta wuce kitchen ta hau aiki, tana gama ta jere su cikin babban basket ta d'auka ta nufa wajan dinning, Abba ta hango yanata faman dariya ko me Mummy ke fad'a mishi oho.
Yana ganin Haseenah ta nufo yanda suke ya had'e Rai kaman Bai ta6a dariya ba, tsuka ya ja ya kau da kai, Kai kace wani mak'iyin shi ya gani.
Tana zuwa ta gaidashi Amma ko kallonta baiyi ba, ta sake gaidashi karo na biyu tunanin ta ko baiji bane.
Wata tsawa ya daka mata sannan yace" ki ajiye da Allah ki 6acemun a nan"
Razana tayi da firgici ya sata tsayawa cak Nan ita batayi baya ba Kuma batayi gaba ba, k'afan shi ya saka Nan ya tokare ta ta kife wajan, jini ne ya fara zuba a hancin ta, a firgice ta mik'e ta zuba a guje ta bar wajan, saboda tsabar rikicewa ma bata san inda ta nufa ba.....
For comments 08144932303
Advertisement
- In Serial325 Chapters
A Cliché Multiverse Story
I, Asahi was just a filthy rich young master who died? But why I am following the plotline of a third rate novel? Why is this Goddess named Cliche? And wait, this didn't end there. I'm also getting this great system for fulfilling my fantasies.
8 1196 - In Serial9 Chapters
Worlds Apart
I've been separated from society my entire life, bound to be out of reach for which I care for the most, forced to the gutters by my only salvation. Hope. Yet death came ever so slowly, I never wished to live a full life, however, fate loves to joke around but sometimes jokes aren't funny. Luke was a slave to modern society unable to break free from poverty, an orphan stripped of his home, abandoned to his own devices until the fateful day he closed his eyes his last and opened them anew as Argile. Chazillah with the title named Azure Dreamshaper for credit> Link: https://www.deviantart.com/chazillah/art/azure-dreamshaper-471719197 I currently have no permission for me to use the image, however, if the artist may message me giving permission to use or take down the image it would be kindly appreciated.
8 124 - In Serial23 Chapters
Scabbard
This is the tale of a man named Michael, or Mika for those who knew him in his last days. Michael was not a very interesting man, nor had a very interesting life, some would argue he didn't had a life at all, at least not up to the beginning of his journey on a strange new land. This is the story of how such a man helped shape a whole universe.
8 121 - In Serial52 Chapters
Pioneer 0: Rise of the machine in a world of sword and magic.
In the year of 2062, Earth is destroyed by a massive nuclear war as a result of years of power struggling and multiple conflicts between various nations, 12 billion lives was lost on Earth, followed by 40 million humans on Mars's colony, humanity went extinct, followed by their faithful robot army as the machine rust away and crumble down to nothing in the passage of time. All but one machine, an planetary explorating and colony constructing robot designed by a mega-conglomerate before the nuclear war on Earth and forgotten because of the same war, one unimportant piece of technology resting on the right spot and the right time when the Earth exploded, the blast created a rift in space and time, tossing the machine to a parallel world, a world of sword and magic, a world of gods and devils, heroes and demon kings. A world for the forgotten machine to awaken and carry out its duty with only one unknown directive: -Live
8 218 - In Serial23 Chapters
A Trillion Trillion Years
Jake has been in love with Abby ever since she was just an idol. Everything in his world has been about her since he first laid eyes on Abby. He has seen her grow as an idol, become a star, and slowly begin her solo career, all with his support. But its not enough. He needs Abby to love him! After an embarrassing accident with Abby he finally puts his plan into motion. Master PlanOne: Get a job in the same management company. Even as a janitor!Two: Get a chance to talk with Abby.Three: ???Four: Marry Abby. Will the girls he meets along the way stop him from making his dream a reality? Or will he find out that reality itself is never as simple, or bright, as it may seem… ————————Authors note————————I’ll update this three times a week. S at 5pm est (I will be publishing daily until I catch up with my original posting) I will be publishing on RoyalRoad and Scribblehub I hope you enjoy reading this, at least for a couple minutes of your day.
8 79 - In Serial317 Chapters
Abominable King
(Rebooted version Synopsis) I was just a man like any other, until I got sucked into a world that wants me dead. I can’t think of a reason why they want me dead, aside from the fact that I command a massive army of the unliving and have the reputation of being the embodiment of evil. Between a character I had created in my youth who wants nothing less than to conquer the world in my name, a force made up of unholy monstrosities and the Forces of Light constantly trying to kill me, how am I to live peacefully or find a way back home and will I even want to by the end of my journey? I will do what is needed and fight for survival, even if it means becoming what the slanderous rumors about me proclaim as truth. The reign of darkness has come again on this fantasy world, and all who try to fight me will face the wrath of the Abominable King. (I did not make the art.) (WARNING! THIS NOVEL CONTAINS CONTENT THAT IS NOT SUITABLE FOR YOUNG READERS! IF YOU ARE UNDER 16-21 OR HAVE ISSUES WITH INTENSE DEPICTIONS OF CRUELTY AND/ OR OTHER NSFW CONTENT, THEN KNOW THAT YOU HAVE BEEN WARNED!) (There are acts and opinions in this novel that I do not condone. Read at your own peril and watch out for depictions of violence, cruelty, evil in the extreme and more.) (Updates every Saturday at 8:00AM when not on Haitus.)
8 240

