《HASEENAH》PAGE 27&28
Advertisement
🌸 *HASEENAH*🌸
Story &written
By👇🏻
Aysher Abbakar (meerah)
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
#
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-08144932303
Follow me on
*Long Live Pml*
'''Dan Allah masu mun magana ta pc in tura musu novel dina suyi hakuri suna tanbaya a group, ina da matsalar network daga lokacin da nace kowa xan bishi in tura mishi in personal network dina yakan dad'e bai dawo dai dai ba, kuyi hakuri plx'''
*27~28*
Da gudu Saratu ta fito jin irin Kiran da Mummy ke Mata, duban ta tayi sannan tace" Ina wannan matsiyaciyar take?"
Ta nuna k'ofar d'akin su Haseenah.
Ta6e Baki Saratu tayi tace" na dai ga Haseenah ita da Yar Uwarta sun kamo Uwar an fita da ita da sauri, ban dai San menene ba"
Wani shewa Mummy ta saki tana fad'in" Haka akeso, Allah yasa tafiyar kenan"
Nan ta wuce ciki zuciyar ta fari tas, gani take yanzu Kap duniya Bata da wata damuwa, gida ya Zama nata, miji ya Zama nata Haka dukiyar shi ma daga ita sai 'yar ta.
Haka yau Mummy da kanta ta shiga kitchen ta zuba girki, tana gamawa ta fito musu dashi palour suka baje sai Kwasa suke suna Hira ita da Mum Haseen.
Can asibiti kuwa sai son barka ake, Hajiya Saudatu ne ta je har kasuwa ta tasa Abba a gaba suka shiga suka siya kayan abinci, da akwati gudu hud'u, da kanta ta shiga shagon Abba ta had'a kayan Umma akwati guda, sannan suka je baby care aka cika akwati biyu tam da kayan baby, d'ayan Kuma aka cikeshi da kayan shafe shafe sannan tace su taho asibiti.
Shi dai Abba ya rasa Gane kanshi, farin ciki yake ko bak'in ciki oho, Amma kana kallon shi kasan akwai abunda ke damun shi.
Advertisement
Haka suka k'arasa asibitin lokacin har Umma ta tashi, dangi duk sun zagaye ta, dad'i ne ya Kama Umma Dan rabon da taga dangi an taru a kanta tun auran ta.
Tunani take to dama me yasa suka guje ta? Wata zuciyar tace mata halin Mummy.
Abba ma da yazo yaga jaririn shi d'aukan shi kawai yayi ya zuba ma yaron Ido, can sai ya share k'walla, Mummy Saudat ta kula da hakan, duk yanda akayi tasan d'an uwanta Yana cikin wani mawuyacin hali, addu'a kawai yake buk'ata, Dan tasan ba Haka yake ba.
Ganin jikin Umma ya koma normal yasa Mummy Zuwaira ta buk'aci sallama, Haseen ne ya biya duka bill d'in sannan aka kwashi Kaya sai gida, Abba kuwa da sunan Abban Ummah yayi wa yaro hud'uba wato *Abdullahi*, Haseenah tace za.ana kiranshi (Aaman).
Dangin Ummah kuwa murna kaman ba gobe, Nan aka Kira Abban Ummah aka sanar dashi, Nan yace ga tukwicinshi Yana isowa.
Motoci biyar akayi duk 'yan raka Ummah gida ne.
Mummy da Mum Haseen da Kuma Saratu na tsaka da Hira sukaji horn d'in mota, kallon kallo suka Fara yi, can Mummy tayi tsuka tace" Abban su ne fa"
Jin motar ba guda d'aya bane ya sasu duka yin shuru Dan sauraron abunda ke faruwa.
Kafin su yunk'ura su tashi sukaji Muryar Mummy Saudat tana rangad'a gud'a, mutuwar zaune dukansu sukayi, Mummy Zuwaira ce ta Fara shigowa rik'e da Aaman a hanunta an nad'e shi cikin showel farare tas, sai Ummah dake biye da su, sai Kuma jama'ar da suka rufa musu baya anata San barka.
Ko kallon inda Mummy take Basu Yi ba, palour Ummah suka wuce, Nan aka Fara shigowa da akwatuna Wanda Abba ya siya, Nan fa hankalin Mummy ya tashi.
Haseen ne shigowan k'arshe rik'e da basket sun jero tare da Haseenah gwanin sha'awa.
Advertisement
Wani zagi Mummy ta kutuntuma, lokaci d'aya tayi zubur ta mik'e ta fisge d'an kwali, Nan ta hau surfa masifa da zagi tana fad'in
"ba.a Isa a munafurce ta aci amanar ta ba, anje anyo ciki sannan za.a lank'aya wa mijin ta saboda anga yanada dukiya"
D'aya daga cikin 'yan uwan Umma ta lek'o tace" sai gashi kuwa aka haifo namiji Kuma ba"
Ihu Mummy ta sake tana fisge fisge, ganin zaninta na Shirin fad'uwa yasa Mum Haseen janta da k'yar sukayi ciki, tana tirjewa tana komai suka ja ta ita da Saratu suka turata d'aki suka kulle ta.
Dukda Haka bakin Mummy Bai mutu ba fad'i take" in dai da jini aka haifeta wallahi saita hallaka Ummah da d'an data Haifa.
Bata gama tsinkewa da Al amarin ba seda taji ana sake wani gud'an ganin galleliyar motar da Abban Ummah ya siya Mata, lek'awa Mummy tayi ta window Nan ta hango motar ko gama cire ledar jiki ba'a Yi ba, zaman dirshan Mummy tayi Kan tiles ta fashe da kukan bak'in ciki, ganin duk dangin shi sun cika wajan Mummy, gashi ta jiyo yanda ake ta yaba kayan akwati Wai Abba ne yayi Mata.
Kan uba, wallahi bazata yarda ba, ita za.a ciwa Amana, wannan karon ta d'au alwashi ko ta tsiya ko ta arzik'i ba bokan da zataje da kanta zata d'au mataki.
Ganinta kawai suke.
Kuka Tasha bana wasa ba, seda tayi Mai isarta sannan ta koma ajiyar zuciya.
Jin tayi shuru yasa Mum Haseen bud'e k'ofar ta shiga a hankali, Mummy ta hango gashin kanta a tsatstsaye sai kace mahaukaciya, Nan Mum Haseen ta Fara kwantar Mata da hankali, ta Bata shawara ta tashi su koma wajan boka.
Wani ashar d'in da Mummy ta k'unduma Mata ya sata Jan bakin ta tayi shuru, Mummy ta kalleta tace" ba wajan d'an iskan da Zan Kuma zuwa, da kaina da Kuma hanuna Zan d'au mataki"
Girgiza Kai Mum Haseen ta Fara yi tace" Yaya in hankali ya 6ata hankali ke Nemo shi, karkije ki aikata abunda zakiyi Dana sani daga baya, Haka Allah ya nufa ki d'au kaddara sai kiga Allah ya sauya Miki da mafi Alheri"
Tunda Mum Haseen ta Fara magana Mummy ta zuba Mata Ido take kallon ta Kai kace maganar ya shigeta ne, seda Mum Haseen ta yi shuru sannan Mummy ta dube ta tace " kin gama Dan ubanki? Munafuka kawai, dama nasan da saninki aka ci Amana ta, shiyasa naga Haseen bini bini Yana bin Mata kin kasa tsawatar mishi, ba ruwanki da damuwa ta dama nasan ba don Allah kike k'aunata ba, ki tashi ki ficemun a gida karna sake ganinki inba nice na nemeki ba"
Maganganun Mummy ya ta6a wa Mum Haseen zuciya, hakan ya sata mik'ewa ta d'au jakan ta ta fice a wajan, Haseen ta gani ya fito Nan tace ya ajiye ta a gida.
Tun da Mummy ta haihu kullum gidan shiga ake ana fita, Mummy kuwa ko fitowa Bata yi duk ta rame tayi bak'i ta fita a hayyacin ta, ta sak'a wannan ta kunce wannan duk ta rasa abin Yi.
Da Haka har yau akazo shagalin suna.
For comments 08144932303
Advertisement
- In Serial1672 Chapters
Sylver Seeker
After fulfilling the duty all arch necromancers are tasked with, Sylver Sezari was not expecting to ever wake up again. But he did. And after crawling his way back into the land of the living, he’s alive once again. In a strange land, a strange time, and with a strange floating screen in front of his new face. Either through plan or chance, he’s alive again, and planning to enjoy himself to his heart's content. -The story isn’t grimdark, but it’s not all sunshine and rainbows either. There will be lighthearted and positive moments, as well as some sad ones. That being said, it’s a whole lot more light than dark. -This is a LITRPG story. Chapters are published every 2 days at 21:00 GMT. Author’s note:-It can get very GORY. I’m somewhat desensitized to gore and violence. So while the story isn’t full of gore for the sake of gore, it can get a little too descriptive.-The MC is a necromancer, so corpses and decay, and all the things that come with it, will be mentioned from time to time.-I’m a huge fan of Egyptian, Slavic, and Greek mythology, so expect quite a bit of that. That said, so much is altered, you’ll be hard-pressed to guess how exactly it is being used.-Despite being ‘immortal’ the MC can die. In the event he does, the story doesn’t end, simply time skips forward. Which in some cases is going to be worse than just dying.-I love plot twists, as much as I love red herrings and Chekhov guns. Deus Ex Machina’s not so much. Cover: https://angshumandhar.artstation.com/projects
8 284 - In Serial27 Chapters
Shine (Mass Effect AI SI)
A Mass Effect Self Insert, except about three hundred years before the games. And the SI has replaced the Geth. Help.
8 399 - In Serial74 Chapters
Mystic Ink
Life is hard for an orphan on the streets of Tyine, Capitol of the "Glorious Empire" of Haj, thirteen year old Cass knows this well and has managed to survive ever since her parents abadoned her five years ago. She thought her life was as terrible as it could be, but now that she has been grabbed off the street and thrown into a dark cell with many other street children, Cass worries that life may get even worse. Join Cass on her journey through blood and magic as she learns the power in the ink tattooed into her back and the horror of the worst kinds of people. (please take the content warnings seriously, this wont be a happy one folks)
8 190 - In Serial223 Chapters
Skyfire Magus
Lynne Hyorn, seventeen years old laziness-personified, manages to enter one of the four prestigious Academies for the Arts of Magic, Skyfire Academy for Magical Arts. However, unlike others, the reason he enrolled was not to pursue Magic, but rather because his father promised him hefty allowance if he manages to enter. His temporary tranquility soon comes to an end, though, as his father is drafted for war and his home is confiscated shortly after, leaving him to sleep on the streets. With no other choice, he decides to finally dedicate himself for the first time in his life, rising up from being just a lowly, Unranked Mage, to the ultimate guardian of the Academy: Skyfire Magus. A coming-of-age story set in a world of Magic follows young Lynne through the perils of strength, dedication, and world where fist isn't always the answer to every question. ~If you find any mistakes, please do comment on them or send me a message. Even though I proofread my chapters, mistakes stay from time to time.~ Glossary of terms (may include spoilers): https://freelanceronfire.wordpress.com/skyfire-glossary/ ~~COMPLETED~~
8 270 - In Serial52 Chapters
The Rest is Riddles
[COMPLETE] Straight-A student Jane Huang cares only about acing her classes and graduating college... until a terrifying encounter with an otherworldly monster plunges her into the mysterious world of Mir. To return to the home she loves, Jane must become an 'avtorka' - one with the gods-given power to write in Mir's Book of Truths and change reality. A brutal series of tests awaits her, each designed by the gods to target her weaknesses and shatter her resolve.Helping her train for her godstests is Nikolay, a ruthless battlemage whose Oath to protect his dying ruler is slowly killing him. Nikolay needs Jane to break his Oath - or so Jane thinks - and despite their mutual enmity, she agrees to help him. But as Jane endures her godstests, she is drawn into a web of magic, mystery, and deceit that forces her to question Nikolay's motives, the godstests, and the very nature of reality itself.***Earnesty Writing Award Fantasy Winner!*** https://www.youtube.com/watch?v=RdMY61yxdPg**First Place in the Punk Rock Awards, 2022, Action/Adventure****First Place in the Dream Awards 2020, Adventure****First Place in the Golden Awards, Adventure****First Place in the Mono Awards 2020, Adventure****First Place in the Shimmer Awards 2020, Adventure****First Place in the Sunshine Awards 2020, Adventure****Second Place in the Paper Awards 2020, Adventure****Second Place in the First Impressions Award (SUAW) 2020****Third Place in the Golden Awards 2020, Fantasy****Third Place in the Noble Awards 2020, Action/Adventure****Third Place in the Imperial Awards 2020, Adventure**
8 203 - In Serial41 Chapters
Born Immortal
Astyr Tyr was found newborn and naked on the side of the road with nothing but a bracelet and a name. After fifteen years of being bounced around the foster system, she finds herself in a small town on the brink of discovering big secrets and maybe... Her place in the world.Credit for the cover photo goes to S Baker under the Creative Commons License. Check out her work here http://www.flickr.com/photos/sarahbaker
8 165

