《HASEENAH》PAGE 27&28
Advertisement
🌸 *HASEENAH*🌸
Story &written
By👇🏻
Aysher Abbakar (meerah)
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
#
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-08144932303
Follow me on
*Long Live Pml*
'''Dan Allah masu mun magana ta pc in tura musu novel dina suyi hakuri suna tanbaya a group, ina da matsalar network daga lokacin da nace kowa xan bishi in tura mishi in personal network dina yakan dad'e bai dawo dai dai ba, kuyi hakuri plx'''
*27~28*
Da gudu Saratu ta fito jin irin Kiran da Mummy ke Mata, duban ta tayi sannan tace" Ina wannan matsiyaciyar take?"
Ta nuna k'ofar d'akin su Haseenah.
Ta6e Baki Saratu tayi tace" na dai ga Haseenah ita da Yar Uwarta sun kamo Uwar an fita da ita da sauri, ban dai San menene ba"
Wani shewa Mummy ta saki tana fad'in" Haka akeso, Allah yasa tafiyar kenan"
Nan ta wuce ciki zuciyar ta fari tas, gani take yanzu Kap duniya Bata da wata damuwa, gida ya Zama nata, miji ya Zama nata Haka dukiyar shi ma daga ita sai 'yar ta.
Haka yau Mummy da kanta ta shiga kitchen ta zuba girki, tana gamawa ta fito musu dashi palour suka baje sai Kwasa suke suna Hira ita da Mum Haseen.
Can asibiti kuwa sai son barka ake, Hajiya Saudatu ne ta je har kasuwa ta tasa Abba a gaba suka shiga suka siya kayan abinci, da akwati gudu hud'u, da kanta ta shiga shagon Abba ta had'a kayan Umma akwati guda, sannan suka je baby care aka cika akwati biyu tam da kayan baby, d'ayan Kuma aka cikeshi da kayan shafe shafe sannan tace su taho asibiti.
Shi dai Abba ya rasa Gane kanshi, farin ciki yake ko bak'in ciki oho, Amma kana kallon shi kasan akwai abunda ke damun shi.
Advertisement
Haka suka k'arasa asibitin lokacin har Umma ta tashi, dangi duk sun zagaye ta, dad'i ne ya Kama Umma Dan rabon da taga dangi an taru a kanta tun auran ta.
Tunani take to dama me yasa suka guje ta? Wata zuciyar tace mata halin Mummy.
Abba ma da yazo yaga jaririn shi d'aukan shi kawai yayi ya zuba ma yaron Ido, can sai ya share k'walla, Mummy Saudat ta kula da hakan, duk yanda akayi tasan d'an uwanta Yana cikin wani mawuyacin hali, addu'a kawai yake buk'ata, Dan tasan ba Haka yake ba.
Ganin jikin Umma ya koma normal yasa Mummy Zuwaira ta buk'aci sallama, Haseen ne ya biya duka bill d'in sannan aka kwashi Kaya sai gida, Abba kuwa da sunan Abban Ummah yayi wa yaro hud'uba wato *Abdullahi*, Haseenah tace za.ana kiranshi (Aaman).
Dangin Ummah kuwa murna kaman ba gobe, Nan aka Kira Abban Ummah aka sanar dashi, Nan yace ga tukwicinshi Yana isowa.
Motoci biyar akayi duk 'yan raka Ummah gida ne.
Mummy da Mum Haseen da Kuma Saratu na tsaka da Hira sukaji horn d'in mota, kallon kallo suka Fara yi, can Mummy tayi tsuka tace" Abban su ne fa"
Jin motar ba guda d'aya bane ya sasu duka yin shuru Dan sauraron abunda ke faruwa.
Kafin su yunk'ura su tashi sukaji Muryar Mummy Saudat tana rangad'a gud'a, mutuwar zaune dukansu sukayi, Mummy Zuwaira ce ta Fara shigowa rik'e da Aaman a hanunta an nad'e shi cikin showel farare tas, sai Ummah dake biye da su, sai Kuma jama'ar da suka rufa musu baya anata San barka.
Ko kallon inda Mummy take Basu Yi ba, palour Ummah suka wuce, Nan aka Fara shigowa da akwatuna Wanda Abba ya siya, Nan fa hankalin Mummy ya tashi.
Haseen ne shigowan k'arshe rik'e da basket sun jero tare da Haseenah gwanin sha'awa.
Advertisement
Wani zagi Mummy ta kutuntuma, lokaci d'aya tayi zubur ta mik'e ta fisge d'an kwali, Nan ta hau surfa masifa da zagi tana fad'in
"ba.a Isa a munafurce ta aci amanar ta ba, anje anyo ciki sannan za.a lank'aya wa mijin ta saboda anga yanada dukiya"
D'aya daga cikin 'yan uwan Umma ta lek'o tace" sai gashi kuwa aka haifo namiji Kuma ba"
Ihu Mummy ta sake tana fisge fisge, ganin zaninta na Shirin fad'uwa yasa Mum Haseen janta da k'yar sukayi ciki, tana tirjewa tana komai suka ja ta ita da Saratu suka turata d'aki suka kulle ta.
Dukda Haka bakin Mummy Bai mutu ba fad'i take" in dai da jini aka haifeta wallahi saita hallaka Ummah da d'an data Haifa.
Bata gama tsinkewa da Al amarin ba seda taji ana sake wani gud'an ganin galleliyar motar da Abban Ummah ya siya Mata, lek'awa Mummy tayi ta window Nan ta hango motar ko gama cire ledar jiki ba'a Yi ba, zaman dirshan Mummy tayi Kan tiles ta fashe da kukan bak'in ciki, ganin duk dangin shi sun cika wajan Mummy, gashi ta jiyo yanda ake ta yaba kayan akwati Wai Abba ne yayi Mata.
Kan uba, wallahi bazata yarda ba, ita za.a ciwa Amana, wannan karon ta d'au alwashi ko ta tsiya ko ta arzik'i ba bokan da zataje da kanta zata d'au mataki.
Ganinta kawai suke.
Kuka Tasha bana wasa ba, seda tayi Mai isarta sannan ta koma ajiyar zuciya.
Jin tayi shuru yasa Mum Haseen bud'e k'ofar ta shiga a hankali, Mummy ta hango gashin kanta a tsatstsaye sai kace mahaukaciya, Nan Mum Haseen ta Fara kwantar Mata da hankali, ta Bata shawara ta tashi su koma wajan boka.
Wani ashar d'in da Mummy ta k'unduma Mata ya sata Jan bakin ta tayi shuru, Mummy ta kalleta tace" ba wajan d'an iskan da Zan Kuma zuwa, da kaina da Kuma hanuna Zan d'au mataki"
Girgiza Kai Mum Haseen ta Fara yi tace" Yaya in hankali ya 6ata hankali ke Nemo shi, karkije ki aikata abunda zakiyi Dana sani daga baya, Haka Allah ya nufa ki d'au kaddara sai kiga Allah ya sauya Miki da mafi Alheri"
Tunda Mum Haseen ta Fara magana Mummy ta zuba Mata Ido take kallon ta Kai kace maganar ya shigeta ne, seda Mum Haseen ta yi shuru sannan Mummy ta dube ta tace " kin gama Dan ubanki? Munafuka kawai, dama nasan da saninki aka ci Amana ta, shiyasa naga Haseen bini bini Yana bin Mata kin kasa tsawatar mishi, ba ruwanki da damuwa ta dama nasan ba don Allah kike k'aunata ba, ki tashi ki ficemun a gida karna sake ganinki inba nice na nemeki ba"
Maganganun Mummy ya ta6a wa Mum Haseen zuciya, hakan ya sata mik'ewa ta d'au jakan ta ta fice a wajan, Haseen ta gani ya fito Nan tace ya ajiye ta a gida.
Tun da Mummy ta haihu kullum gidan shiga ake ana fita, Mummy kuwa ko fitowa Bata yi duk ta rame tayi bak'i ta fita a hayyacin ta, ta sak'a wannan ta kunce wannan duk ta rasa abin Yi.
Da Haka har yau akazo shagalin suna.
For comments 08144932303
Advertisement
- In Serial36 Chapters
Gaia's little Gamer
The planet is under attack and Gaia is in desperate need of help. Evil gods, demonic corporations, and devils in human form. All that stands against them is...Pef.
8 123 - In Serial31 Chapters
It That Laments
The time waits for no man, so is the case for Selv, who had lost everything. In the stagnant world where everything is standing still, a change occurred. Everything begins when she haunted him. She, who has that face, came to him together with the memories he locked away. The train to the past blew its horn while everything is moving toward the inevitable end. What will he, who was at the center of everything, do when it pushed him from the back line to the center again?
8 164 - In Serial23 Chapters
Daniel Haley and the Immortal Ninja
For thousands of years, the ninja have ruled the world in secret, orchestrating history and protecting humanity from the strange creatures that lurk in the shadows and beings with extraordinary abilities. So far, they’ve done an impeccable job. The humans are convinced that they live in an average world.But all of that is about to change.Our unseen guardians are being overwhelmed and the planet is rapidly succumbing to chaos as the climate changes, the enemies of the ninja grow stronger, and everything the ninja fought to keep hidden threatens to break loose.The ninja have sent Katherine Carvosso to recruit humanity’s best hope for survival—a clumsy and socially dysfunctional seventeen-year-old Daniel Haley.Of course, Daniel figures this must all be the world’s best prank—until he sees Katherine tearing the roofs off of cars with her bare hands, bounding over impossible distances, and somehow having the power to create earthquakes.Daniel has no idea the fate of the world rests on his shoulders. All he wants is to find a way to win over the girl of his dreams.Will he get his head out of the clouds and save us, or will he let the Earth burn chasing after his heart?
8 165 - In Serial40 Chapters
Transition and Restart, book two: The Billion Dollar Empress
The billion dollar empress is back in town. Without her empire, and most definitely without a billion dollars. After her transition and arrival in a world where she was never born fifty years earlier, Christina Agerman has started to rebuild her life as a high school student in Japan. She has found friends and love, and now it's time to restart the fashion empire she never created. But it comes at a cost. How strong are those ties of friendship and love when she starts out on a road she has to walk alone?
8 163 - In Serial7 Chapters
Birth of God
A story of a man becoming a True God and establishing his religion in a medieval fantasy world. The world with humans, elves, dwarf, fantasy creatures(eg. dragons) and more. Various races that try to survive in this harsh world. The day he descend onto this world is when everything start to change. Main character OP from start but not the main focus of the story. What will he bring to this world? Hope? Terror? Blessing? Destruction?What kind of God is he? Look forwards: Many legendary creatures, races/tribe, kingdom(group of creatures), religion, interaction, and more. There will be many minor stories and characters that might or might not interact with one another.
8 67 - In Serial47 Chapters
The Silent Guard (mxm)
Sometimes, words are not necessary.Zen has been mute since the day he was born. Having grown up unwanted and on the streets, he unexpectedly found himself a hero in the prince of his country, Qi. The man had appeared when other children had been throwing stones at him, trying to drive him from the safety of the town's protective walls. Qi ends up saving him, and as thanks, Zen decided to dedicate his life to protecting his master. Years later, as tensions begin to rise with one of their much-larger neighboring countries, he finds himself and his master thrown into unfamiliar territory, both physically, and mentally.
8 149

