《HASEENAH》PAGE 35&36
Advertisement
🌸 *HASEENAH*🌸
Story &written
By👇🏻
Aysher Abbakar (meerah)
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
#
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-08144932303
Follow me on
*Long Live Pml*
*Dan Allah ina me bada hakuri na jina shiru da akayi na wasu 'yan kwanaki, hakan ya farune sakamakon rashin wuta da aka samu, na gode sosai da dakuwarku da kulawarku kaina, wa'yanda suke kirana da masu bina pc na gode sossai expecially meerah novels, I love u guyx much much Allah bar zumunci*
*35~36*
Wuta ne ya bi Haseenah sakamakon buɗe k'ofar da tayi, da sauri ta ja da baya haɗe da salati.
Haseenah na jin salatin Umman ta amma ba halin fita dalilin zafin wuta da hayak'in da ya cika d'akin, tun tana jiyo ummah har taji shuru.
Zubewa tayi wajan tana kuka tana faɗin " wayyo ummah na wayyo Aaman"
Tari ne ya turnuk'e Haseenah, kafin kace meye itama wuta ya mamaye d'akin ta.
Hakan yayi dai dai da dawowan Abba daga masallaci, Mummy na ganin shi ta daka tsalle ta hau kurma ihu tana birgima, ihun tane ya tada Saratu daga barci.
Da gudu ta fito dan ganin abinda ke faruwa, ganin wuta na tashi a side d'in Ummah ya sa Saratu ihu tana faɗin" Mummy Umman Haseenah a ciki"
Abba ko ganin wutan na dad'a tashi ya sashi fita da gudu dan neman d'auki.
Watsa ruwa ake da k'asa amma kamar fetur ake dad'a zuba wa.
Hakan yasa wani mak'wabcin su kiran fire service.
Mummy Zuwaira kuwa tunda tayi asuba ta kasa zaune ta kasa tsaye, haka haseen ma, shi mafarkin Haseenah yayi ta faɗa rijiya.
Hakan yasa shi kasa nutsuwa ya d'au makullin motar shi ya nufa gidan.
Isowar shi yayi dai dai da isowar Mummy Zuwaira.
Ganin mutane cike a gate d'in gidan ga motar fire service yasa Mummy Zuwaira firgice wa.
Haseen kuwa cike da tashin hankali ya fara ture mutane yana kutsawa ciki Mummy Zuwaira na bin shi a baya.
Ganin wuta na tashi wajan su Haseenah yasa Haseen rugawa da gudu ya nufa ciki.
Ganin ana ta shek'a ruwa ya sashi waigawa yana duba Ummah da Haseenah amma baiga kowa ba.
Mummy ya gani can gefe tayi zaman 'yan bori daga ita sai d'aurin k'irji kanta ko d'an kwali babu fuskanta sha6e sha6e da hawaye da majina tana ihu tana faɗin " wayyo Ni na shiga uku ku ceto rayuwar bayin Allan nan"
Advertisement
Nan Haseen ya fahimci abinda Mummy ke nufi.
Da gudu ya nufa wajan da nufin shiga nan aka rik'e shi, fisgewa yake yana faɗin" ku kyale Ni in shiga in fito da su tunda ku kun kasa ceton rayuwar su"
Rik'e shi sukayi suna faɗin ya nutsu amma ina baima san suna yi ba, ganin basu da niyan sake shi ya sa Haseen fashewa da kuka yayi zaman dirshan.
Mummy Zuwaira kuwa zare ido take tana faɗin" ina k'anwata take? A ina kuka barta? Ku matsa in fito da ita"
Abba ma firgici ya hana shi magana, zare ido kawai yake yana sharce zufa.
Da k'yar aka samu aka kashe wutan.
Ana kashewa kuwa aka 6alle k'ofar aka shiga.
Ummah dai babu ita babu alamar ta, cikin d'akunan aka shiga ana dubawa, d'akin Ummah ba kowa, nan suka wuce na Haseenah, can gefe suka ganta kwance ta gama k'onewa da ka ganta babu alamar rai a jikin ta.
Haseen kuwa yana ganinta ya kurma ihu ya yanki jiki ya fad'i.
D'akin Aaman kuwa ganin shi sukayi can gefe kwance, babu alamar k'una ko ciwo a jikin shi, sai dai baya numfashi.
Nan aka kira ambulance, ba tare da 6ata lokaci ba aka fito da Haseenah da Aaman.
Amma Ummah kam an duba ta ko ina babu ita babu dalili.
Mummy Zuwaira ce ta shigo ta fara dube dube, tana zuwa wajan corridor da Ummah tayi sallah taga shatin toka, tsugunawa Mummy Zuwaira tayi nan taga d'an kunnen Ummah sai zoben hanunta.
Hanunta ne ya fara rawa tana maimaita innalillahi wa inna ilaihir raji'un.
Zubewa tayi a wajan numfashin ta na fita da k'yar.
Jin tana salati cikin kuka yasasu garzaya wa dan ganin abinda ya faru.
Ganin abinda Mummy Zuwaira ta tsinta ba k'aramin firgita Abba yayi ba.
Fad'uwan shi kawai akaji nan aka fitar da shi.
Da gudu Mummy ta shigo tana faɗin" ta mutu ko? Halima ta mutu?"
D'agowa Mummy Zuwaira tayi cike da tuhuma ta dubi Mummy, ganin yanda take ya sa Mummy Zuwaira mik'ewa ta shak'o Mummy, turata tayi har bango ta d'auke Mummy da Mari sau uku, duban ta tayi cikin wata irin murya sannan tace
" Lauratu wallahi na rantse da Allah in na samu da hanunki wajan mutuwar er uwata sai na d'au fansa akan ki,kap zuriyar ku sai sun k'are".
Da k'yar aka k'waci Mummy hanun Mummy Zuwaira, kafin kace meye magana ya karad'e family.
Advertisement
Gida ya cika Mak'il ba masaka tsinke, banda sautin shesshek'ar kuka ba abinda kake ji.
Haseen kuwa allurar bacci aka mishi.
Mummy Zuwaira masu investigation ta d'auko Nan tasa aka kewaye side d'in Ummah ba shiga ba fita har sai an gama bincike.
Hankalin Mummy ba k'aramin tashi yayi ba dan tasan ba makawa za aga cylinder d'in gas d'in.
Da k'yar aka samu Aaman ya farfaɗo sakamakon hayak'in da ya shak'a ya mishi illa.
Haseenah kuwa dama likita ya sanar musu ta riga da ta rasu.
Lokacin da wannan labari ya iske su anga tashin hankali, barin Umaimah da baby, Suma Kan suma, ba abinda ya d'aga musu hankali sai in sun tuna jiya ma suna tare da ita.
Hakan ya jefa kowa cikin rud'ani da tashin hankali.
Abban Ummah kam jinin shi ya dad'a hawa.
Ummah kam ruwa aka yayyafa aka tattara tokan aka saka cikin likkafani.
Haseenah ma dawowa da ita akayi aka shiga da ita side d'in Abban ta, Nan aka mata wanka aka sutura ta.
Nan akace a shigo a mata addu'a.
Lokacin Haseen ma ya farfaɗo, k'arfin hali kawai yake, yaci kuka har ya gaji.
Shigowa shi gidan kenan daga asibiti, yana ganin kowa nata faman alwala zuciyar shi ta tsinke, nan ya tabbatar da ya rasa masoyiyar shi kenan har abada.
Tafe yake kaman wanda zai fad'i, yana shiga cikin gidan cikin kuka yaji Umaimah ta faɗa jikin shi tana faɗin" ya Haseen sun kashe mun Ummah da Haseenah na, Ya Haseen ko wanene yake da hannu karka barshi"
Kasa magana yayi dan kuka yaci k'arfin shi, zubewa yayi gaban Mummy Zuwaira cikin kuka yana faɗin" Mummy Kinga abunda sukamin ko? Kinga tozarci da wulak'ancin da akamun ko? Meyasa za'amun haka? Meyasa Ni basu kasheni ba? Meyasa....
Bai iya k'arasawa ba dan kuka yaci k'arfin shi.
Kama hanun shi kawai tayi tana girgiza mishi kai.
Nan ta mik'ar dashi ta duba su Umaimah tace" suje su mata addu'a za.a tafi da ita"
A tare suka shiga su hud'u, Haseen, Mummy Zuwaira, Umaimah da baby.
Ganinta shinfid'e cikin makara an gama shirya ta, ga tokan Ummah a gefe shima cikin likkafani.
Zubewa duka sukayi a wajan, baby kuwa tunda ta zube bata sake motsawa ba.
Addu'a kawai Haseen da Mummy Zuwaira keyi suna kuka, Umaimah kam ta kasa cewa komai sai rungume Haseenah da tayi tana wani irin kuka.
Bud'e gefen fuskan ta Haseen yayi, da sauri ya sake ganin irin k'onewan da tayi inba fad'a maka akayi ba bazaka gane Haseenah bace.
Kuka sossai yake ya dubi Mummy Zuwaira yace" dan Allah Mummy ki fad'a Mata ta tashi, wallahi zan aure ta a haka, Mummy ina sonta ki tashe ta dan Allah, inaso tamun magana ko da sau ɗaya ne"
Da ka ganshi kasan baya cikin hankalin shi.
Hakan yasa Mummy ta Kama hanunshi ta d'ago Umaimah suka kama hanyar fita.
Mummy Haseen ya hango tsaye bakin k'ofar ta, kallon da ya mata ya sata sunkuyar da kai k'asa alamar rashin gaskiya.
Saratu kuwa duk ta daburce saboda mutuwar tagirgiza ta.
Aaman kuwa na can asibiti ana mishi k'arin ruwa.
Lokacin da aka zo fita da gawar su ba k'aramin tashin hankali aka shiga ba, dan Mummy Zuwaira Suma tayi, haka baby Kam an rasa gane kanta.
Tunda suke basu taɓa shiga tashin hankali irin na yau ba.
Abba ma tafiya kawai yake kai kace mara hankali ne, janshi kawai ake duk yanda aka bi dashi nan yake bi, ji yake kaman ba shi ba, mafarki yake ko gaske sai Allah.
Seda akayi sallar su a masallacin juma'a ta anguwan sanna aka wuce dasu mak'abar ta, Haseen ma shuru kawai yayi amma idon shi bai dena zubar da hawaye ba.
A jere aka tona kabarin Ummah da Haseenah, tare da Haseen aka kama gawan da kanshi ya saka Haseenah.
Lokacin da aka gama rufe su kuwa Haseen durk'ushe wa yayi wajan yana kuka yana faɗin
" me yasa zakimun haka? meyasa Baki barni na fara mutuwa ba? me yasa kika za6i jefa rayuwata cikin garari da tashin hankali? Meyasa kinsan bazaki rayu tare da niba kika barni na shiga rayuwar ki? Meyasa baki bari munyi ban kwana ba kika tafi Haseenah? Why? Why?"
Kamashi daddy shi yayi cike da tausayin ɗan nashi ya rungume shi, cikin kuka Haseen ya k'ank'ame daddy shi yana faɗin" daddy kaga abinda rayuwa tamun ko? Kaga abunda mutuwa tamun ko? Kaga Haseenah ta tafi ta barni? Daddy fad'amun ya zanyi? Ka tashe ta dan Allah kace mata zan aure ta a haka, daddy ka fad'a mata ina sonta a haka daddy...
Toshe mishi Baki daddy yayi yana faɗin" haba Haseen kar ka zama mara tawakkali mana, ka rungumi k'addara sai Allah ya musanya maka da wata"
Da sauri ya dubi daddy yace....
Na gaji wlhy....
Plx vote nd comments
Advertisement
- In Serial13 Chapters
Tails In The Water (BXB)
Calum was happy. Despite something that happened when he was a child, he felt content with his life. He had a good twin brother, an amazing father, and was doing decently in college. But the night after he had finished freshman year, he saw something. Something far from normal, something extraordinary. Something... supernatural. Aka wanted something more. He needed something that wasn't in his life. When he saw Calum, he knew that he was the missing puzzle piece in his life. But he couldn't approach him. Not when he was something that was considered a myth in the world. When they meet, Aka and Calum find themselves and their friends and family brought in the middle of a division between humans and the supernatural. I have posted this story both on Quotev and Wattpad as well.
8 218 - In Serial24 Chapters
Brave World Online
Revolving around a new VRMMO Game which was called Brave World Online at 2045, the game quickly stole the attentions of millions and was flooded with constantly increasing popularity for the past three years. It was a fantasy themed online game in which Players found themselves in a large floating continent called Daedalus. And in this game too--a youth called Steve Westdale entered. A cowardice one both in real life and in game. Sunk deeply after so many malice directed to him, he stayed submissively and pessimistic as if neither alive nor dead. What kind of thing will await the Greatest Coward in this brand new world he escaped to?
8 317 - In Serial9 Chapters
The 15th Story: Chariots Of Troubles
Donald Silva stopped being a child at fifteen. Being a child meant he could do what he wanted without being responsible for whatever consequences. That goes away when you're responsible for the crippling of your mother. His life continually went downhill from that point but just when all hope seemed lost he find an opportunity for redemption. The question is, can he redeem himself?
8 274 - In Serial26 Chapters
I Want to Be the Emperor, so I'll Fight Tooth and Nail to Achieve my Goal
Alden Lyons awakes in the clinic of a strange fantasy world, uncertain of where he is and how he got there. Stranger still, he has been granted a power known as the All-Maker, which he unwittingly uses to give himself RPG-like abilities. Leveraging his new found power and the good will of those around him, Alden sets his eyes on the throne. Current Release Schedule: Friday 11:15AM & Saturday 4:30PM Eastern time for the free release. Patrons receive both chapters a week early on Saturday 4:30PM.
8 109 - In Serial13 Chapters
Dragons of Dark Rebellion in A World of Essence
In a world where cultivation is the highest form of virtue, the purity of one’s blood is of absolute value. Saul is neither Arloni, nor Delcairan. He’s both. But when a strange ring suddenly falls into his hands, nineteen year old Saul is more than willing to push the boundary between fantasy and reality. However, things are not as they once were in Falden. At a time where Saul finally confronts lord Albryte’s sons after years of torment and abuse, his father’s health is fading fast. Suddenly faced with the consequences of his actions, Saul is forced to make a difficult decision. And as he fights his own battle, dark forces descend upon Lucidia. Followed by a pair of glowing red eyes, a stranger appears in the night, visiting Falden with unfavorable intentions. Even worse, nameless assassins strike at the heart of the capital, leaving Eliza Zaryph, the black sheep of the ruling house of Lucidia, shouldering the burden of governing a kingdom that once turned its back on her. As the world marches toward chaos, their lives take a drastic turn. Will Saul abandon those he holds most dear? Will Eliza drown herself in the past? Or will they struggle against fate and seize the future with their own hands? Tomorrow remains uncertain. But the Sun will show them the way. Author's Note: Inspired by the Wuxia/Xianxia genre the magic system is comprised of cultivating through different Worlds of power, where each World offers more strength and abilities. Currently there are five Worlds known: Essence Practitioner, Essence Channeler, Essence Warrior, Essence Conquerer, and finally Essence Ruler. (And for the best reading experience I recomend altering your width setting to about 70 or 80 percent on desktop.) Table of Contents: Prologue Part 1: Homecoming (chapters 1-12) Part 2: Journey (chapters 13-25) About 70 percent complete. I'll update this figure over time and begin posting again after I finish it and go through several rounds of editing.
8 152 - In Serial160 Chapters
Life Quotes
Quotes to help you reflect or remember times from your life. VOTE | COMMENT | FOLLOW MY PROFILE | CHECK OUT MY OTHER STORIES
8 205

