《HASEENAH》PAGE 49&50
Advertisement
🌸 *HASEENAH*🌸
Story &written
By👇🏻
Aysher Abbakar (meerah)
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
#
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-08144932303
Follow me on
*Long Live Pml*
Da Allah ina me bada hak'urin rashin jina da akayi na wasu kwanaki, hakan ya faru ne sakamakon wasu uzurori da nakeyi da kuma rashin wuta,wanda ke kirana da kuma wa'yanda suke mun magana privately Dan jin dalilin rashin ganin post Dina na gode sossai da kulawarku da kuma soyayyarku gareni da kuma littafi na, i hope my excuses will b considered.
*Team Haseenah*
Haseenah na Nan tana gaisuwa ga masoyan ta, kuma ta gode da tausayawar ku gareta, tace ku kwantar da hankalin ku Dr Sameer is by her side.
Iya comments d'inku iya d'adin page d'in gaba.
Thnx all.
*49~50*
Haseen bayan sun gaisa da iro me gadi ya dubeshi yace" Baba nazo maka da wata magana ne me girma, da fatan zaka bani had'in Kai?"
Shuru Baba yayi na wasu seconds kaman me tunani sannan yace" ina jinka yaro"
Gyara zama Haseen yayi sanann ya fara cewa" ba wani abu bane ya kawoni baba, Kan mutuwar Umma ce da kuma Haseenah, wanda kowa yake zargin mutuwar akan kunna wutar akayi, ko Kanada wata 'yar masaniya kan faruwar hakan?"
Malam iro shuru yayi, yayin da k'irjin shi yake dukan uku uku, saboda tsananin tsoron dake zuciyar shi, dukda ba wani abu ya sani ba amma yasan halin matar gidan kamar yunwar cikin shi, abinda ya dad'a firgitashi kenan dan yasan ko wucewa ta zo yi tagan su tare da Haseen to Allah ne kawai ze k'wace shi daga cin mutunci.
Ganin ya tafi duniyar tunani yasa Haseen ta6a shi yace" Baba lafiya kuwa?"
A firgice ya d'ago yace" ba komai Haseen, maganar gaskiya bansan komai akai ba nima lokacin ina nan waje naga Alhaji ya fito yana kwalalar wuta"
Haseen ya kula a birkice Baba yake dan haka mik'ewa kawai yayi ya sa hannu a aljihu ya ciro dubu biyar ya bawa Baba, hannu na rawa ya k'ar6a ya hau washe baki yana an gode.
Hakan ya tabbatar wa da Haseen cewa wannan baban mayen kud'i ne, ta haka kawai ze sa ya ja hankalin shi har ya samu abinda yake so.
Bai sake cewa komai ba ya nufa wajan motar shi ya shiga da niyar barin wajan.
Advertisement
Reverse ya fara yi da nufin juyawa nan ya hango wata mota CRV tazo tayi parking, wani bak'in saurayi ne a ciki bakin shi ma bak'ikk'irin, Bai gama k'arewa na cikin motar kallo ba yaga Saratu ta fito cikin gida.
Wajan motar ya ga ta nufa, sanye take cikin wasu dogayen riga armless, ta d'aura kimono a Kai, kanta yaci uwar attachment, fuskan ta Babu masaka tsinke saboda kwalliya, ga uban glass tafkeke data maka wanda ya kusan rufe mata hanci, k'afar ta kuwa high heel ne kalan kayan sai hanunta d'aya rik'e da jaka d'ayar kuma wayar ta ce tana wasa dashi.
Gayen kuwa yana ganin ta ya hau washe baki itama tana mayar mishi, gidan gaba ya bud'e mata ta shiga sannan ya rufe.
Duban shi tayi suka fuskanci juna sannan suka sake sakewa wa juna murmushi ta manna mishi kiss a kumatu.
Zaro Ido Haseen yayi ya k'ame a wajan saboda tsananin kad'uwa, yaushe Saratu ta zama haka?
Kafin ya samu amsar tambayar shi buzzing d'in motar ne ya dawo dashi daga tunanin da ya tafi, k'urar motar kawai ya gani dan bai ma san ta inda suka yi ba.
Jiki a sanyaye ya bar wajan shima ya nufa hanyar gida.
*Abuja*
Bayan kwana biyu da yin aiki wa Haseenah Ammi ta ce wa Sameer a sallame su kawai su koma gida su fara shirin tafiya turkey, tunda ance nan da sati d'aya zasu tafi.
Ba musu Sameer ya k'ar6a musu sallama suka tattara kaya suka koma gida.
Da daddare ne kowa na zaune a palour, yayin da Mahmud ke zaune chan gefe yana buga game.
Haseenah kuwa duk a takure take ganin irin hararar da Mahmud ke zabga mata.
Hakan yasa jikinta yin sanyi ta sunkuyar da kanta k'asa tana hawaye.
Tausayin kanta kawai take dan bata san inda take ba balle tayi tunanin inda zata ga wanda ta sani.
Sameer ne ya sauko daga kan steps, duban shi Ammi tayi sannan tace" son dama Kai nake jira tuntuni akwai maganar da nakeso muyi dakai"
Zama yayi gefen ta sannan ya dube ta yace" Ammi am here"
Nan ta Fara cewa" magana kan rashin jin yarinyar nan nake so muyi, nace why not mu sami malam Kabir yana mata rubutu ko Allah zesa a dace, tunda in Allah ya wuce gaba sukan dawo da jinsu"
Kafin yayi magana Mahmud yayi karap yace" Ammi karku wahalar da kanku da kud'in ku, kuka sani ko dama tuntuni kurma ce?"
Advertisement
Tsawa Sameer ya daka mishi cikin 6acin rai yace" tashi ka fice a nan"
Mik'ewa yayi yana k'ananan surutu ya haye sama ranshi a 6ace.
Tsuka ya ja sannan yace" Ammi nima dama inaso in Miki maganar sai kika rigani, yanzu da asuba in mun had'u a masallaci zan tsayar dashi in mishi bayani sai muji yanda abun ze kasance"
Nan suka cigaba da maganar yanda tafiyar zata kasan ce.
Tare suka ci abinci sannan kowa ya kama gaban shi.
Dama Haseenah wani d'aki dake jere dana Ammi aka gyara mata.
Seda ta gama cin kukan ta sannan tayi nafila raka'a biyu sannan ta kwanta.
Bayan anyi asuba ne Sameer ya tsayar da malam Kabir ya mishi bayani, ya gamsu da bayanin shi sannan yace yau ze Fara mata rubutu zuwa k'arfe goma zai shigo mata dashi gida.
Nan sukayi sallama ya koma ciki.
Ammi bayan ta idar da sallah ta fito da niyar tashin Haseenah, nan ta hangota zaune kan sallaya , murmushi tayi ta juya ta koma.
Nan Haseenah na idar wa ta koma bacci.
K'arfe bakwai da rabi ta tashi a firgice, sakamakon mafarkin Umman ta da tayi, kuka ta saka tana 6ari, ta rasa da wani bakin zata yi bayani, waye ze Gane halin da take ciki? Wa ze mayar da ita cikin dangin ta? Ina zata ga Haseen d'in ta? Ina zata ga Mummy Zuwaira da su Umaimah da Baby, ga Aaman d'inta ma?"
Wanann abubuwan suke sata kuka.
Mik'ewa kawai tayi ta shige toilet, wanka tayi ta fito sanann ta zura dogon riga cikin kayan da Sameer ya siya mata ta fito, dan ko mai bata shafa ba balle taje garin kallon madubi dan ta dena kalla.
Fitowa tayi ta lek'a d'akin Ammi amma bata nan, palour ta fito nan ma ba kowa, kitchen ta lek'a Nan ta hango Ammi tana k'ok'arin had'a kayan breakfast.
Shiga tayi sannan ta tsaya bayan Ammi.
Knocking k'ofar tayi, da sauri Ammi ta juyo, nan suka sake wa juna murmushi kawai.
Nuna mata kujera Ammi tayi, girgiza kai tayi sannan ta nufa wajan ta d'au wuk'a ta fara fere dankalin da Ammi ta d'ebo.
Tare suka gama komai, nan taje da kanta ta jera su kan dinning ta dawo tayi wanke wanke ta goge wajan.
Shirin da tayi kan table ya burge Ammi, dan haka ta tsaya kawai tana kallon ta.
Yanda Ammi taga Haseenah ta iya sarrafa ko wani na'urar girki da tsarin shirya table hakan ya tabbatar wa Ammi ba daga gidan talaka ta fito ba, to ina iyayen ta suke?
Sallamar Malam Kabir ne ya katse wa Ammi da tunanin ta.
Nan ta bashi umarnin shigowa, hanun shi d'auke da robar swan k'arama, rubutu ne aciki.
Bayan sun gaisa ne yayi wa Ammi bayanin yanda za tayi amfani dashi.
Nan Ammi tace kaga dama ba abinda ta ci sai a fara amfani dashi yanzu.
Nan sukayi sallama ya fice.
Haseenah dake zaune gefe suka haɗa ido da Ammi, da hannu Ammi ta kira ta nan ta taso ta zo.
Cup Ammi ta d'auka ta zuba mata rubutun sannan ta sake tofa addu'a ta mik'a mata, Bismillah tayi itama dukda batasan na meye ba ta shanye.
Kar6an cup d'in Ammi tayi ta ajiye sannan ta jawo Haseenah ta sunkuyar da ita had'e da kwantar da kanta kan cinyar Ammi, kad'an ta zuba a murfin goran sannan ta d'an zuba kad'an cikin kunnen Haseenah, seda ta tabbatar ya shiga sannan ta juya ta zuba mata a d'ayan.
Murna ne fal zuciyar Haseenah dan ta gane ko na menene.
Dama kullum setayi addu'a Allah dawo mata da kunnen ta.
Lokacin ƙarfe goma harta gota.
Da yake weekend ne suna ta bacci.
A tare Sameer da Mahmud suka sauko k'asa.
Gaida Ammi sukayi sannan Sameer ya dubi Haseenah ya sake mata murmushi, sunkuyar da kanta kawai tayi.
Idon Mahmud ne ya kai kan table, zaro ido yayi haɗe da furta" wow, Nice deco"
Dariya Ammi tayi sannan tace" k'anwar ka ce tayi"
6ata rai yayi ganin ance wannan mummunar ce k'anwar shi, har zeyi magana yaga kallon da Sameer ke mishi hakan ya sashi yin shuru.
Nan suka hau table d'in suka fara cin abinci.
Bayan sun gama ne Ammi take sanar dashi ankawo rubutun harta fara sha.
Dad'i sossai yaji sannan yace Allah ya sa a dace.
Mik'ewa Ammi tayi ta koma d'aki yayin da Mahmud ya nufa wajan computer ya fara game.
Haseenah kuwa zama tayi a takure waje d'aya.
Hakan ya sashi bud'e side drawer ya d'auko paper da biro ya nufa inda take ya zauna gefen ta sannan ya d'au biron yayi rubutu ya mik'a mata.
For comments only 08144932303
Advertisement
- In Serial36 Chapters
Old Man's Adventure
A plane flying over the Atlantic Ocean suddenly loses power and prepares to make a water landing. Yet as they crash into the ocean the passengers suddenly find themselves on land. A message greets them, stating that a System has taken over the world and that monsters will begin to spawn in two hours. Due to their circumstances, they have been transported to a special zone, away from the rest of civilization. Amongst the passengers is an old man named Frank Wolfe. At seventy-nine years old, his best days are far behind him. But when the System arrives, he realizes that regaining his youth is possible. The System might bring devastation to the population, but for Frank, it's a chance to have a second go at life in this new world. If he and his fellow passengers can survive, that is. Author's note: I am also participant in the Royal Road Writathon challenge :)
8 513 - In Serial19 Chapters
The Corradi Effect
While on patrol near the Coalition's border, the crea of the starship Galaxie receive a transmission from deep space. Ordered to investigate the source and intent of the signal, the crew stumbles upon an even greater mystery, concerning the planet of origin and their welcoming committee...
8 201 - In Serial12 Chapters
Becoming Itachi Uchiha in a Different world!
Good bit of your time. (maybe...not) Based off of Naruto and IDWWNS. Warning : Contains profanity usage, a bit of sexual content, and gore. Introduction: 37 year old, Charlton Triston was a huge fan of Naruto. At first, he thought it was some random anime his colleagues wanted to torture him with, but as he watched episode after episode, he became addicted to the fighting secenes, justus, but most of all, The Sharingan. (Most thought he was too old for something so childish. However he didn't mind.) His favorite character was Itachi Uchiha, because of his tranquility and intellegence. He even admired Itachi for planning the future for Sasuke. On one saturday morning, Charlton Triston was driving to the store where popular manga was sold, he was caught up in an accident (truck-san), so in order to keep his childern safe, he sacrifced himself... ........ "Welcome Charlton, atlthough it feels rushed, but you shall be reincarnated into a world that will be similar to the anime you will choose." Happily said the odd voice. Ranks for Different World: -G,G, -F,F, -E,E, -C,C, -D,D -B,B, -A, A, -S, S Academy Student, Genin, Chuunin, Jounin, Special(SS) Jounin, Kage, Other : Medical-ninja, S-class, Missing-ninja, Hunter-ninja, Courier-ninja, Disclaimer : I do not own Naruto nor anything associated to it. As it is owned by Kishimoto. Any images or quotes are owned by their respective owners. I'm not accurate with my naruto knowledge, so please, deal with it.
8 117 - In Serial38 Chapters
Pride X Kämpfer ReVamp
Caelum Desanto, Caprice Steiner, Simone Alucard, and the gang of Galatea Academy are back in this the second volume of the shamelessly perverse "Pride X ReVamp" light-novels.With Galatea Academy reopening for business a mere two weeks after the destruction caused by Crimson Crescent's Familiars, Caelum and the gang are left with little choice but to pick up the pieces and carry on with the semester. As Caelum continues to make inroads toward unlocking the Kaiser's Blessing, the antagonism between Caprice and the Countess reaches new heights leaving one to savor victory and the other to lick her wounds.However, all is not fair in love and war, and when a new player enters the arena with unknown intentions toward Caprice, Caelum finds himself facing an opponent he is quite simply ill prepared to fight.Sequel to: """"Pride X Familiar ReVamp"""" available on Amazon Kindle in ebook format.Authors note: Cover Artwork is not final.
8 187 - In Serial8 Chapters
Gacha BD
Des gacha bd quoi ^^
8 111 - In Serial19 Chapters
Adopted by McQueen (humanized) Book One
Chloe is a 9 year old girl in Creek of Angels Orphanage. Her parents died when she was only a baby. The crazy guard of the orphanage, Mrs Nelson, abuses Chloe for her own pleasure. Chloe does chores and stays in her room everyday. She doesn't get to have fun like the other kids. For years she has been adopted, but also brought back. The families only wanted her for slave reasons. Chloe loves to watch the Piston Cup races and watch her favorite racer, Lightning McQueen. Once she hears that he's coming to her orphanage to adopt, she prays that he'll be the one. The one who would be her hero to save her from this prison. Her prayers come true; she's adopted by McQueen. But Mrs Nelson threatened that if Chloe ever came back, she would suffer the consequences. Will Chloe love her new life? Or will she be brought back and spend the rest of her life suffering and rotting in an orphanage?
8 76

