《HASEENAH》PAGE 49&50
Advertisement
🌸 *HASEENAH*🌸
Story &written
By👇🏻
Aysher Abbakar (meerah)
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
#
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-08144932303
Follow me on
*Long Live Pml*
Da Allah ina me bada hak'urin rashin jina da akayi na wasu kwanaki, hakan ya faru ne sakamakon wasu uzurori da nakeyi da kuma rashin wuta,wanda ke kirana da kuma wa'yanda suke mun magana privately Dan jin dalilin rashin ganin post Dina na gode sossai da kulawarku da kuma soyayyarku gareni da kuma littafi na, i hope my excuses will b considered.
*Team Haseenah*
Haseenah na Nan tana gaisuwa ga masoyan ta, kuma ta gode da tausayawar ku gareta, tace ku kwantar da hankalin ku Dr Sameer is by her side.
Iya comments d'inku iya d'adin page d'in gaba.
Thnx all.
*49~50*
Haseen bayan sun gaisa da iro me gadi ya dubeshi yace" Baba nazo maka da wata magana ne me girma, da fatan zaka bani had'in Kai?"
Shuru Baba yayi na wasu seconds kaman me tunani sannan yace" ina jinka yaro"
Gyara zama Haseen yayi sanann ya fara cewa" ba wani abu bane ya kawoni baba, Kan mutuwar Umma ce da kuma Haseenah, wanda kowa yake zargin mutuwar akan kunna wutar akayi, ko Kanada wata 'yar masaniya kan faruwar hakan?"
Malam iro shuru yayi, yayin da k'irjin shi yake dukan uku uku, saboda tsananin tsoron dake zuciyar shi, dukda ba wani abu ya sani ba amma yasan halin matar gidan kamar yunwar cikin shi, abinda ya dad'a firgitashi kenan dan yasan ko wucewa ta zo yi tagan su tare da Haseen to Allah ne kawai ze k'wace shi daga cin mutunci.
Ganin ya tafi duniyar tunani yasa Haseen ta6a shi yace" Baba lafiya kuwa?"
A firgice ya d'ago yace" ba komai Haseen, maganar gaskiya bansan komai akai ba nima lokacin ina nan waje naga Alhaji ya fito yana kwalalar wuta"
Haseen ya kula a birkice Baba yake dan haka mik'ewa kawai yayi ya sa hannu a aljihu ya ciro dubu biyar ya bawa Baba, hannu na rawa ya k'ar6a ya hau washe baki yana an gode.
Hakan ya tabbatar wa da Haseen cewa wannan baban mayen kud'i ne, ta haka kawai ze sa ya ja hankalin shi har ya samu abinda yake so.
Bai sake cewa komai ba ya nufa wajan motar shi ya shiga da niyar barin wajan.
Advertisement
Reverse ya fara yi da nufin juyawa nan ya hango wata mota CRV tazo tayi parking, wani bak'in saurayi ne a ciki bakin shi ma bak'ikk'irin, Bai gama k'arewa na cikin motar kallo ba yaga Saratu ta fito cikin gida.
Wajan motar ya ga ta nufa, sanye take cikin wasu dogayen riga armless, ta d'aura kimono a Kai, kanta yaci uwar attachment, fuskan ta Babu masaka tsinke saboda kwalliya, ga uban glass tafkeke data maka wanda ya kusan rufe mata hanci, k'afar ta kuwa high heel ne kalan kayan sai hanunta d'aya rik'e da jaka d'ayar kuma wayar ta ce tana wasa dashi.
Gayen kuwa yana ganin ta ya hau washe baki itama tana mayar mishi, gidan gaba ya bud'e mata ta shiga sannan ya rufe.
Duban shi tayi suka fuskanci juna sannan suka sake sakewa wa juna murmushi ta manna mishi kiss a kumatu.
Zaro Ido Haseen yayi ya k'ame a wajan saboda tsananin kad'uwa, yaushe Saratu ta zama haka?
Kafin ya samu amsar tambayar shi buzzing d'in motar ne ya dawo dashi daga tunanin da ya tafi, k'urar motar kawai ya gani dan bai ma san ta inda suka yi ba.
Jiki a sanyaye ya bar wajan shima ya nufa hanyar gida.
*Abuja*
Bayan kwana biyu da yin aiki wa Haseenah Ammi ta ce wa Sameer a sallame su kawai su koma gida su fara shirin tafiya turkey, tunda ance nan da sati d'aya zasu tafi.
Ba musu Sameer ya k'ar6a musu sallama suka tattara kaya suka koma gida.
Da daddare ne kowa na zaune a palour, yayin da Mahmud ke zaune chan gefe yana buga game.
Haseenah kuwa duk a takure take ganin irin hararar da Mahmud ke zabga mata.
Hakan yasa jikinta yin sanyi ta sunkuyar da kanta k'asa tana hawaye.
Tausayin kanta kawai take dan bata san inda take ba balle tayi tunanin inda zata ga wanda ta sani.
Sameer ne ya sauko daga kan steps, duban shi Ammi tayi sannan tace" son dama Kai nake jira tuntuni akwai maganar da nakeso muyi dakai"
Zama yayi gefen ta sannan ya dube ta yace" Ammi am here"
Nan ta Fara cewa" magana kan rashin jin yarinyar nan nake so muyi, nace why not mu sami malam Kabir yana mata rubutu ko Allah zesa a dace, tunda in Allah ya wuce gaba sukan dawo da jinsu"
Kafin yayi magana Mahmud yayi karap yace" Ammi karku wahalar da kanku da kud'in ku, kuka sani ko dama tuntuni kurma ce?"
Advertisement
Tsawa Sameer ya daka mishi cikin 6acin rai yace" tashi ka fice a nan"
Mik'ewa yayi yana k'ananan surutu ya haye sama ranshi a 6ace.
Tsuka ya ja sannan yace" Ammi nima dama inaso in Miki maganar sai kika rigani, yanzu da asuba in mun had'u a masallaci zan tsayar dashi in mishi bayani sai muji yanda abun ze kasance"
Nan suka cigaba da maganar yanda tafiyar zata kasan ce.
Tare suka ci abinci sannan kowa ya kama gaban shi.
Dama Haseenah wani d'aki dake jere dana Ammi aka gyara mata.
Seda ta gama cin kukan ta sannan tayi nafila raka'a biyu sannan ta kwanta.
Bayan anyi asuba ne Sameer ya tsayar da malam Kabir ya mishi bayani, ya gamsu da bayanin shi sannan yace yau ze Fara mata rubutu zuwa k'arfe goma zai shigo mata dashi gida.
Nan sukayi sallama ya koma ciki.
Ammi bayan ta idar da sallah ta fito da niyar tashin Haseenah, nan ta hangota zaune kan sallaya , murmushi tayi ta juya ta koma.
Nan Haseenah na idar wa ta koma bacci.
K'arfe bakwai da rabi ta tashi a firgice, sakamakon mafarkin Umman ta da tayi, kuka ta saka tana 6ari, ta rasa da wani bakin zata yi bayani, waye ze Gane halin da take ciki? Wa ze mayar da ita cikin dangin ta? Ina zata ga Haseen d'in ta? Ina zata ga Mummy Zuwaira da su Umaimah da Baby, ga Aaman d'inta ma?"
Wanann abubuwan suke sata kuka.
Mik'ewa kawai tayi ta shige toilet, wanka tayi ta fito sanann ta zura dogon riga cikin kayan da Sameer ya siya mata ta fito, dan ko mai bata shafa ba balle taje garin kallon madubi dan ta dena kalla.
Fitowa tayi ta lek'a d'akin Ammi amma bata nan, palour ta fito nan ma ba kowa, kitchen ta lek'a Nan ta hango Ammi tana k'ok'arin had'a kayan breakfast.
Shiga tayi sannan ta tsaya bayan Ammi.
Knocking k'ofar tayi, da sauri Ammi ta juyo, nan suka sake wa juna murmushi kawai.
Nuna mata kujera Ammi tayi, girgiza kai tayi sannan ta nufa wajan ta d'au wuk'a ta fara fere dankalin da Ammi ta d'ebo.
Tare suka gama komai, nan taje da kanta ta jera su kan dinning ta dawo tayi wanke wanke ta goge wajan.
Shirin da tayi kan table ya burge Ammi, dan haka ta tsaya kawai tana kallon ta.
Yanda Ammi taga Haseenah ta iya sarrafa ko wani na'urar girki da tsarin shirya table hakan ya tabbatar wa Ammi ba daga gidan talaka ta fito ba, to ina iyayen ta suke?
Sallamar Malam Kabir ne ya katse wa Ammi da tunanin ta.
Nan ta bashi umarnin shigowa, hanun shi d'auke da robar swan k'arama, rubutu ne aciki.
Bayan sun gaisa ne yayi wa Ammi bayanin yanda za tayi amfani dashi.
Nan Ammi tace kaga dama ba abinda ta ci sai a fara amfani dashi yanzu.
Nan sukayi sallama ya fice.
Haseenah dake zaune gefe suka haɗa ido da Ammi, da hannu Ammi ta kira ta nan ta taso ta zo.
Cup Ammi ta d'auka ta zuba mata rubutun sannan ta sake tofa addu'a ta mik'a mata, Bismillah tayi itama dukda batasan na meye ba ta shanye.
Kar6an cup d'in Ammi tayi ta ajiye sannan ta jawo Haseenah ta sunkuyar da ita had'e da kwantar da kanta kan cinyar Ammi, kad'an ta zuba a murfin goran sannan ta d'an zuba kad'an cikin kunnen Haseenah, seda ta tabbatar ya shiga sannan ta juya ta zuba mata a d'ayan.
Murna ne fal zuciyar Haseenah dan ta gane ko na menene.
Dama kullum setayi addu'a Allah dawo mata da kunnen ta.
Lokacin ƙarfe goma harta gota.
Da yake weekend ne suna ta bacci.
A tare Sameer da Mahmud suka sauko k'asa.
Gaida Ammi sukayi sannan Sameer ya dubi Haseenah ya sake mata murmushi, sunkuyar da kanta kawai tayi.
Idon Mahmud ne ya kai kan table, zaro ido yayi haɗe da furta" wow, Nice deco"
Dariya Ammi tayi sannan tace" k'anwar ka ce tayi"
6ata rai yayi ganin ance wannan mummunar ce k'anwar shi, har zeyi magana yaga kallon da Sameer ke mishi hakan ya sashi yin shuru.
Nan suka hau table d'in suka fara cin abinci.
Bayan sun gama ne Ammi take sanar dashi ankawo rubutun harta fara sha.
Dad'i sossai yaji sannan yace Allah ya sa a dace.
Mik'ewa Ammi tayi ta koma d'aki yayin da Mahmud ya nufa wajan computer ya fara game.
Haseenah kuwa zama tayi a takure waje d'aya.
Hakan ya sashi bud'e side drawer ya d'auko paper da biro ya nufa inda take ya zauna gefen ta sannan ya d'au biron yayi rubutu ya mik'a mata.
For comments only 08144932303
Advertisement
- In Serial24 Chapters
Observations of the Nameless
Sometimes the world will just whirl by without a care for its inhabitants. Each passing day bring a new experience unlike the one before it. Why do we do anything... That's a really good question, isn't it? Author's Note: Each chapter is about 300 words, so that's the reason for the short story tag even though this will be a (somewhat) ongoing series. Expect an update twice a week on Tue/Wed and on Fri/Sat. No set time, but likely afternoon or evening.
8 109 - In Serial190 Chapters
Spot of Mummery: Tales of the Bard Technologist
-Webfiction/RolePlay set in the FFXIV MMORPG world of Hydaelyn- In ancient times, Amon was an infamous, immortal Technologist - one of the legends of the late Allagan Empire. However, when calamity strikes his civilization, he's forced to place himself and the remaining Allagans into a time-locked sleep in order to survive. Fast forward many ages later when Amon and his people awaken once more. The world has drastically changed, and his kind is now deemed a threat. The heroic Alliance responded by sending a raid to eradicate the last Allagans, where Amon was ultimately defeated ...or so the world thought. Through his ingenuity and aetheric technology, Amon manged to cheat death. Only, things didn't quite work out the way he planned. Stripped of his magic and technological resources, Amon now takes on the guise of a bard as he struggles to build a new life in a time long after the fall of his empire. But, should the people of this modern time discover who Amon once was, he fears they would put an end to the bard technologist's tale. I've been writing Spot of Mummery since 2018, so there's quite a backlog of story to post! This story was also written before the changes made to lore released in the Endwalker expansion (December 2021). I will address these changes eventually, but only in later chapters - ones written after the expansion came out. I hope that you enjoy and look forward to hearing your thoughts! Interested in seeing more about Amon? Main site: Spot of Mummery Twitter: https://twitter.com/SpotOfMummery
8 259 - In Serial18 Chapters
Frigid Influence
The festive period seems to just be getting longer and longer, and Alex has had enough. What starts as a joke with friends down at the bar ends up with Alex seeing just how close to the truth he was all along, but will he be able to help the inhabitants of a strange alternate Earth powered by the mysterious Frigid? A Gamelit/LitRPG novel heavily influenced by the Veil of the Void ttrpg system.
8 182 - In Serial8 Chapters
Threads of Song and Shadows
A continent on the brink of war. As the daughter of the Skarian Court's Royal Beast Weaver, twelve year old Ning Yue enjoys all the prestige and privileges of the nobility. Even as she struggles to summon her weaving abilities, life traveling within the boundaries of Skarian sovereignty with her father had always been enough. After a betrayal that ends in a massacre, Yue finds herself alone. Homeless, as a fugitive of the country, and with a heart full of burning vengeance, she will have to find her way through harsh landscapes, political minefields and a terrible power taking hold within her. A power that can aid her in her quest for revenge, or save nations across Westhania. Broken treatises. A race on the verge of a mass genocide. A brewing rebellion. And a girl with her qilin in the centre of it all. **Disclaimer: Still a work in progress, so names and sequence of events might change along the way. Thank you for reading! I hope you enjoy Yue's story. :)
8 166 - In Serial20 Chapters
The Man Ruined by The Gods
Eric is an ordinary highschool boy, everything about him is ordinary, if he were to disappear no one would notice. One day while in the middle of detention after being framed of something he didn't do Eric was suddenly wrapped up in light and sent to a white space. Here Eric was given a mission by the old man who appeared before him, he was sent to countless worlds suffering countless tragedies. He experience multiple lives and learned a lot of things, but... even with this he is still unable to break free. A hundred years have passed and Eric was now a broken dark soul, the old man who made him go through hell called himself god, after making Eric suffer he freed him. Feeling happy of being freed Eric was ecstatic at having to be able to rest but as he was going to be revived a message popped up in his head. > With anger consuming his soul Eric promised to himself and to the dark void that he would kill the god who made him suffer, he would erase Vincentius from existence and with those thoughts his mind faded into darkness.
8 139 - In Serial51 Chapters
I am the king of all villainous villian : Volume 1 : against hell devouring beast
"fell in hell , suffered in pain , felt despair and terror for countless time , walked the path of life and death …… he will rise and become the one to rule over dead , spread terror against livings and rule over worlds. ….. mercy isn't thing he knows ,trust ? he doesn't even have one in himself. He , the one who rised from the ashes, crawled out from the depth of hell will now show the world who the true master of the world is ? celestials and demons shall be his vanguard, true dragons and divine phoenix shall be his war mounts , gods and devils shall be his war puppets. heaven shall be his war tetra and everyone remaining shall be his soldiers that follows him with whole heart loyalty. kill anyone that oppose me that's my principle. sometimes when death comes looking for me , I mistake it for my life long friend…..While I mistake life for long lost friend… I shall order and you all shall follow it….. let them show their powers , because a real villain only makes his moves when his pawn and chess pieces has finished their job for the chess master. which is me , a master…….. ……………….be gone thots !!
8 109

