《HASEENAH》PAGE 63&64
Advertisement
🌸 *HASEENAH*🌸
Story &written
By👇🏻
Aysher Abbakar (meerah)
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
#
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS- 08144932303
# http://
Follow me on Aysherabbakar
*63~64*
Ihu Mahmud ya saka yana faɗin " wayyo Ammi ku temakeni"
Ya k'arasa maganar yana nuna Haseenah, Junaid dake saukowa daga stairs ya k'araso da gudu dan ganin meke faruwa.
Har lokacin jikin Mahmud tsuma yake, Haseenah kuwa sororo tayi tana kallon shi dan ganin yana nuna inda take.
Juyawa tayi bayan ta dan ganin abinda yake nuna wa amma bata ga komai ba.
Mik'ewa Sameer yayi ya daka mishi tsawa ganin yanda yá tukwikwiye shi kaman ze yarda shi sannan yace" ka rufa mana baki ka shiga hankalin ka"
Zare ido ya hau yi ji yake kaman ya zura a guje.
Haseenah bata san meke faruwa ba dan ba ji take ba, dan haka ta ja kujera ta nema waje ta zauna.
Ammi kam kasa magana tayi dan haushi ne ya kama ta, dan gani take iskancin Mahmud k'aruwa yake.
Dan haka ya sa ta ja plate ta Fara zuba abincin ta.
Sameer ma Zama yayi ya fara damuwar shi, Junaid matsawa kusa da shi yayi dan bai ma kula da Haseenah ba ya zaunar da shi sannan shima ya zauna kusa da shi.
Har lokacin kallon Haseenah yake da take k'ok'arin cin abinci.
Zungure shi Sameer yayi yace" meye ka k'ura mata ido?"
A firgice a dubi Sameer yace " yaya kaima kana ganin aljanar ne?"
Dariya Junaid da Sameer suka saka sannan Junaid yace" kai da Allah bak'uwa Ammi tayi baka ganta bane?"
Wata ajiyar zuciya ya saki sai alokacin yaji hankalin shi ya kwanta.
To amma wannan wata irin halitta ce wannan?
A hankali ya fara cin abincin shi amma ba'a minti biyu Bai kalleta ba, har a lokacin he's wondering wannan kyau d'in yayi yawa.
Gani yayi har suna k'ok'arin gama cin abinci bai ga haseenah ba, murna har cikin zuciyar shi a ranshi yace Allah yasa sun yar da ita.
Advertisement
Can dai ya kasa hak'uri ya dubi Ammi yace" Ammi wannan d'in wacece?"
" Haseenah"
Ta bashi amsa a tak'aice.
" To Ammi itace daughter d'in uncle d'inmu Wanda Kika ce a Cairo ta girma?"
Haushi ne ya kama Ammi dan gani take raina mata hankali yake.
A fusace tace" kai karka dameni, Haseenar da muka Kaita Turkey d'inne baka Santa ba? Ko zaka cemun baka ganeta bane?"
A razane ya dubi Ammi yace" haba Ammi, this not possible, wancan mummuna ce wannan kuma fa she's a halfcas"
Tsuka Ammi ta ja ta cigaba da cin abincin ta, duban Sameer yayi yace" bro Dan Allah tell me who is she"
Sameer da ke sunkuye yace" ita Ammi da ta fad'a maka baka yarda ba sai Ni ne zaka yarda? To she's d one, wannan wanda kake kira fatalwar, itace wannan thats how she looks like before "
Waiiii Mahmud Kam he can't believed that, Wai itace wanann yarinyar? Gaskiya akwai damuwa.
Junaid ma kallon ta yake ya kasa d'auke kai.
Haseenah ko bata sake d'agowa ba seda ta gama cin abinci.
Tashi tayi ta koma kan sofa ta zauna.
'Daura ƙafa tayi ɗaya kan ɗaya ta jingina tana kallon tv, da yake akwai subtitle shiyasa ta zauna tana kalla.
Kallon kallo aka fara yi tsakanin Mahmud da Junaid.
Suna gamawa ta mik'e ta kwashe plates d'in ta nufa kitchen.
Seda ta wanke sanann ta goge wajan ta koma ta zauna.
Ammi ma zama tayi kusa da ita ta bata maganin ta tasha sannan ta d'iga na kunnen ta.
Sameer, Mahmud, Junaid duk tunani suke, kowa satan kallon Haseenah yake da gefen ido.
Ammi kuwa ciki ta shige dan kwanciya.
Tana tashi Sameer ya mik'e ya koma wajan Haseenah, d'agowa tayi suka haɗa ido, murmushi ya sakar mata itama ta mayar mishi sannan ta cigaba da kallon ta.
Haka kawai Mahmud yaji haushin murmushin da Sameer ya Mata, baisan sanda ya saki tsuka ba.
Sameer Bai ma san yana yi ba, dan biro ya d'auko ya fara mata rubutu, inta karanta ta bashi amsa.
Advertisement
Haushi ya kama Mahmud ya tashi ya wuce sama fuuuuu.
Bin bayan shi Junaid yayi da sauri, amma harya wuce d'aki ya banko k'ofar.
Zaune ya tarar da shi ya buga uban tagumi, zama yayi gefen shi yace " bro lafiyarka kuwa?"
Mchewww " wanann yayan harda wani zuwa wajanta, to me ze Mata oho? Yarinya ma da baji take ba amma seya takura mata?"
Mchewww ya sake jan wata tsukar..
Duban shi yayi da mamaki sannan Junaid yace" did u care about her now?"
"Why would I care about her? By d way who is she to me?"
Junaid ya dubi idon Mahmud, yasan ba makawa kishi ne da soyayyar Haseenah ta kama shi, but amma bazai san hakan ba tunda idon shi ya rufe.
Nan Junaid yace " to tunda U don't care about her let him be Mana, ko lefi ne dan ya kulata? Atleast she needs someone besides her huh?"
" To ai se yayi ta yi"
Mahmud ya bashi amsar tare da mik'ewa ya wurgar da pillow ya shige toilet.
Murmushi Junaid yayi a ranshi yace akwai damuwa knan.
Ganin Mahmud ba shida niyar fitowa ya sa shi barin d'akin.
Can ko Sameer ko sai faman washe baki yake ganin yanda suke hira da Haseenah.
Ganin ya cika ta da surutu ya sa ta mik'e tace zata tafi.
Alama ya mata kan ta tsaya, ba musu ta tsaya nan ya mata rubutu ya mik'a mata.
Gani tayi ya rubutu" ki shirya mu fita yawo da yamma"
Duban shi tayi sannan ta nuna mishi d'akin Ammi, ya gane abinda take nufi wato ya tambayi Ammi.
Murmushi yayi sannan ya gyad'a mata kai alamar to.
Wucewa d'aki tayi sanann yabi bayanta da kallo.
Bayan anyi sallan la'asar ne Sameer ya samu Ammi d'aki tana zaune.
Zama yayi kan stool sannan ya gaisheta, bayan ta amsa ne se kuma dukan su sukayi shuru.
Duban shi tayi sannan tace" yaya akayi?"
Shafa kai yayi yana murmushi sannan ya daure yace" Ammi dama inaso mu ɗan fita da Haseenah ne, naga zaman gidan yayi yawa atleast she should fresh up"
Zuba mishi idon da tayi ne ya sashi marairaice wa yace" pleeeeaaaase"
Kaman ba zata bashi amsa ba sai kuma tace" karku dad'e"
"Yeeeeesssoooo" ya furta sai kace ƙaramin yaro, abun mamaki ya ba Ammi dan it's been a while da taga son d'inta cherishing like this.
Fita yayi ya nufa hanyar d'akin Haseenah, a hankali ya lek'ata, ganin ta yayi kwance kan gado, tana sanye da dogon riga amma kanta babu mayafi..
Gashin ta ya gani kan fuskan ta idon ta na kallon sama, da alama tunani take.
Jin kaman ana kallon ta ya sata d'agowa, ganin sameer ba k'aramin mamaki ya bata ba, da sauri ta mik'e ta zauna tana laluben ɗan kwalin ta.
Murmushi ya mata sannan ya mata alama da get ready.
Itama murmushin tayi sannan ta gyada mishi kai.
Hannu ya d'aura kan tsintsiyar hannun shi sannan ya nuna mata five fingers d'inshi, wato karfe biyar zasu fita.
Yana gama haka ya juya ya fice.
Duban agogo tayi taga 4:05 mik'ewa tayi ta shiga toilet Dan yin wanka.
Ta 6ata lokaci sossai wajan 30mins sannan ta fito.
Sallan la'asar tayi sannan ta fara shafa mai.
Lokacin is almost to 5, Dan Haka cikin k'ank'anin lokaci ta shirya cikin wata pencil skirt bak'a da red top, ta yane kanta da Black veil, shafa red lipstick tayi sanann ta zira flat Vincci shoes d'inta.
Wrist watch ta saka hanunta sanann ta mak'ala yan kunne.
Short kimono top ta d'auko ta d'aura Kan kayan shima Black sannan ta fesa turare ta fito.
D'akin Ammi ta shiga ta tarar bata nan.
Palour ta nufa nan taga Ammi nan ta tarar da ita zaune tana kallo, tunda ta fito Ammi ta zuba mata ido tana Masha Allah.
Sameer ko dake saukowa daga stairs cak ya tsaya yana kallon wannan halitta.
Kusa da Ammi ta zo ta zauna tana murmushi.
Dafa ta Ammi tayi Sannan ta......
For comments 08144932303
Advertisement
- In Serial20 Chapters
Fallen
He hadn't even gained a consciousness yet that he was bound to lose everything if he ever came to life. He hadn't offended anyone, but they offended him. He hadn't cursed anyone, they cursed him. He hadn't killed anyone, they killed everyone related to him. Thus, he silently vowed. "They plan to offend me for their own interest? I shall give them plenty of reason to do so. Do they want to curse me? Please do so, since I'm more than willing to be your living bane. Kill me? Sadly, you won't be the last having this type of wishful thinking."- The Devil -------------------- I think that I can manage 1 chapter per week now, maybe 2 but certainly not three. PS: As I think that there should be small mistakes here left and right, I'd gladly welcome a proofreader.
8 136 - In Serial16 Chapters
Spaceslime
In the Babylonian debris field, on a derelict spaceship, life again awakens. Authors note: This is my first ever story that I have published on RoyalRoad and I hope you will enjoy it. Feedback is much appreciated.
8 182 - In Serial11 Chapters
The Otherworldly Filmmaker
An aspiring indie filmmaker was suddenly transported to a fantasy world while shooting a scene in a remote tropical jungle. Having no fighting experience or any other experience, he was only left with his film-directing skills and the shooting equipment that was also transported along with him. He finally decided to be the first film director of this strange new world. He will introduce the craft of filmmaking to that world and move the hearts of its inhabitants with his films. Extra lore materials/The World of The Novel: https://www.worldanvil.com/w/grandea-continent-thesilentone This novel is also available in webnovel.com: https://www.webnovel.com/book/11344537705345005 . I am the same author as that website (Diabolique_TSO). TSO Stands for TheSilentOne (my RRL account)Film collage art was done by: https://www.deviantart.com/sandzen/art/Movie-Box-Collage-3-Dramarama-252080201 All rights of the image go to the respective film studio and his contribution to making the art.
8 169 - In Serial11 Chapters
When the throne calls
A newly graduated teacher begins his career while trying to overcome certain things from his past.His mysterious semblance shall attract lots of people, but he shall not care. Well, things are about to change!
8 176 - In Serial17 Chapters
Just Keep Running (Bulldogs MC #2) [Featured]
** Wattpad Featured Story ** Lenni has been running for months, constantly moving and never putting down roots. When she runs into a face from her past, halfway around the world from home, will she finally be able to stop running, or are old habits too hard to break? This is a story of one woman's fight for survival, and the bikers who may make or break her. Contains lots of swearing. Warning: May contain triggers for suicide, domestic abuse, rape and mental health issues. Please don't read if these make you uncomfortable.Copyright © 2017. All rights reserved. This book or any portion thereof may not be reproduced or used in any manner whatsoever without the express written permission of the publisher except for the use of brief quotations in a book review.
8 90 - In Serial47 Chapters
Naruto: The Youngest Anbu
Life is hard for the little Uzumaki. Abused, tortured, and treated like a monster. Naruto constantly walks the streets alone while receiving glares from the villagers and the constant verbal abuse. One day, on his birthday, he meets the nine tailed fox. Instead of hating him, the fox grew to like the little Uzumaki. The nine tails decides to train the little guy and make him into a strong shinobi. Very soon, the 3rd Hokage will call him into his office to reveal the new life of the little child...I, unfortunately, don't own Naruto. Masashi Kishimoto does.
8 98

