《HASEENAH》PAGE 83&84
Advertisement
🌸 *HASEENAH*🌸
story &written
By👇🏻
Aysher Abbakar (meerah)
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
#
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-08144932303
Follow me on
*83~84*
Mummy ce ta share hawaye sannan ta dubi Haseenah tace" ki bani labari ya akayi hakan ta faru"
Shuru Haseenah tayi kaman ba zatayi magana ba, dan batasan ta inda zata fara ba, da k'yar ta iya buɗe baki nan ta fara basu labari tun sanda ta tsinci kanta cikin kabari da temakon da Sameer ya mata kawo da surgery d'in da aka mata, daga nan ta d'aura da basu labarin rikicin da ya faru da matsalar da suka fara samu kan mutanen gidan.
Dukan su kuka suke saboda ba k'aramin tausaya mata sukayi ba, duk wannan abinda ake Aaman na mak'ale jikin Haseenah ya kwanta har bacci ya ɗauke shi.
Jinjina kai Mummy tayi sannan ta tuno da maganar haseen, wato lokacin da ya tubure kan shi jikin shi na bashi Haseenah bata mutu ba.
Sauke ajiyar zuciya tayi sannan Mummy tace" Haseen yayi gaskiya"
Da sauri Haseenah ta d'ago ta kalli Mummy jin an ambaci sunan abun k'aunar ta, dama tun tuni ta rasa ta yaya zata fara tanbayar Mummy, hakan ya sanya ta cewa" me ya faru Mummy?"
Nan ta kwashe labari ta faɗa mata irin abubuwan da suka faru bayan rabuwa da kuma irin rikicin da Haseen keyi kan shi zaije neman ta.
Tausayin shi ne ya kamata haɗe da k'aunar shi da ya k'aru cikin ranta, sunkuyar da kai kawai tayi ba tare da tace komai ba.
Mummy ce ta dubi Umaimah da ke manne jikin Haseenah tace" ki kawo mata abinci mana da Allah kin d'afe jikinta kaman zata gudu"
Mik'ewa tayi ta shiga kitchen, Nan ta cika wa Haseenah abubuwan ciye ciye, aiko taci da yawa dan dama yunwa take ji.
Advertisement
Bayan ta gama ne suka shige d'akin su Umaimah tayi wanka sannan ta kwanta.
Aaman na kwance gefen ta yana sharara bacci.
Nan suka cigaba da labari har wajan 12 na dare kafin nan suka kwanta.
Haseenah kam da k'yar bacci ya ɗauke ta dan tunani ne cike a zuciyar ta.
Da safe misalin ƙarfe 8 na safe Mummy ta Kira Haseen tace tana son magana dashi.
Ji yayi gaban shi na fad'uwa, da k'yar ya samu ya shirya sannan ya d'auko hanyar gidan.
Haseenah ko tunda tayi sallar asuba ta koma bacci har lokacin bata tashi ba.
Sallama Haseen yayi daga waje nan Mummy tace ya shigo.
Waje ya nema ya zauna sannan suka gaisa, ganin Mummy na ta faman sakin murmushi ya sanya zuciyar shi ta ɗan yi sanyi.
Breakfast ta d'auko mai nan ya ɗan ci kaɗan sannan ya koma ya jingina da jikin kujera, shi duk ya matsu yaji dalilin kiran.
Aaman ne ya taho da gudu ya faɗa jikin shi, d'aga shi sama yayi yana mishi wasa, shi kuwa sai ihu yake yana dariya.
Dariyar shi ne ya farkar da Haseenah daga baccin da take.
Agogo ta kalla taga har tara ta gota, durowa tayi daga kan gadon ta shiga toilet, wanka ta fara yi a gurguje sannan ta fito ta sanya ɗaya daga cikin rigar Umaimah,
Ko ɗan kwali babu a kanta ta sanya flat shoe ta nufo hanyar palour, k'anshin turaren da taji ne ya sanya gaban ta ke fad'uwa, tanbayar kanta take a ina ta ta6a jin irin turaren nan?
Haka ta iso palour tana faman tunani.
Tunda ya fara jin tafiya ya kafe k'ofar da ido, haka kawai yaji yana son ganin me fitowar.
Ita bata ma kula ba ta k'araso, kafe ta da ido yayi ya runtse idon shi, bugun k'irjin shi ya k'aru lokaci ɗaya yaji kanshi ya k'ara mishi nauyi.
Advertisement
Dafe kai yayi dan gani yake kaman gizo idon shi ke mishi.
Hannu ya sanya ya mutsike idon shi dan kawar da wannan gizon.
Amma seya ga yarinyar ma dad'a matsowa takeyi.
Sai a lokacin Haseenah ta d'ago da kanta dan ganin me wannan turaren.
Cak ta ja ta tsaya bakin ta na rawa ta nuna shi da hannu sannan cikin rawar murya tace" yaya Haseen?"
Tsam ya mik'e shima ya dubeta sannan yace" kece Haseenah?"
Kasa bashi amsa tayi illa gyad'a mishi kai da take faman yi alamar eh nice.
Innalillahi wa inna ilaihir raji'un, abunda bakin shi yake iya furta wa kenan.
Is this real life or just dreaming and imagination?
Kuka Haseenah ta fashe dashi dai dai lokacin da mummy ta fito daga kitchen.
Da sauri ta k'araso ta ja Haseenah ta zaunar da ita ganin kukan da take, shiko Haseen din hawaye ke zuba a fuskar shi.
Wayyo dad'i, duban Mummy yayi sannan ya fara cewa" mum ban faɗa miki ba? I told u she's alive but u denied me keda mum D'ina, har kuna cewa na haukace, Ni kaɗai na san abinda nake ji cikin raina"
Alhamdulillah.....
Ita dai Haseenah ta kasa magana se kuka, ita kaɗai ta san ynda take ji a halin yanzu, kwantar da kanta Mummy tayi a jikin ta ta na faman rarrashi.
Nan Haseen fa ya kira mum d'inshi yace ta zo yanzun nan.
Cike da tashin hankali ta k'araso tunanin ta wani abun ne,
Amma tana zuwa labari ya sha bambam.
Da farko da taga Haseenah tsorata tayi, seda Mummy ta Basu labari sannan ta nuna murnar ta a fili.
Farin ciki biyu takeyi, na dawowar Haseenah da kuma nutsuwar d'anta Haseen.
Mummy ce ta kira abban Haseenah, nan ya taho da sauri, ganin Haseenah ba k'aramin ta da mishi hankali yayi ba, kuka yake sossai dan shi sai yanzu yake jin mutuwar umman Haseenah.
Nan yace Haseenah ta biyo shi su tafi.
Murmushi Haseenah tayi tace" Abba nima inason in dawo kusa da kai, amma ba yanzu ba, se an gyara side din ummah na"
Cikin rawar jiki yace" Haseenah ko yau kikace a fara gyara wa za'a gyara"
Nan suka cigaba da tattaunawa, kafin Abba ya bar gidan har ya kira wani architecture ya sanar dashi abinda yake so ayi.
Nan ya mishi transfer kuɗi na duk abinda zasu bukata sannan sukayi sallama da niyar gobe zasuzo su fara aiki.
Mum Haseen sai wajan azahar ta tafi, while Haseen shi ko niyar tafiya bayida shi, hakan ma Haseenah dama ba so take ya tafi ba.
Hirar su suke kaman yau suka fara haduwa dan ji yake ta dad'a shiga zuciyar shi.
Washe gari kuwa nan aka zo aka buɗe side d'in mum aka fara gyara.
Nan fa hankalin Mummy da saratu ya tashi tunanin ta kishiya zai mata, ta tada hankali tace bazai yiwu ba.
Abba ko kallon ta baiyi ba balle ya bata amsa, nan ta tada hauka da bori, Abba yace su cigaba da aikin su kar su kula ta.
Aiko hakan a kayi, kafin kace meye waje ya fara kyau, cikin kankanin lokaci zuwa yamma sun kammala.
Nan aka taho da masu saka POP da penti.
Basu gama ba sai washe gari.
Matasa Abba ya kwaso suka share wajen.
Da kanshi yayi ordering furnitures da komai da su kayan kitchen.
Bayan an gama share wajan ne ya kulle da kanshi.
Yanzu jiran zuwan kayan kawai ake.
Mummy kuwa duk ynda ta kai da maitarta dan gano me yake shirin faruwa amma abun yaci tura.
To me yake shirin faruwa ne?
For comments 08144932303
Advertisement
- In Serial21 Chapters
The Soul Wielder
In the vast expanse of the Khaantul Empire, military medic Meira has always been certain--of her place, of her love, of the good things the Empire brings to unclaimed territories the military settles. When Meira is caught behind enemy lines, she's mistaken for the fabled Soul Wielder of the Juri'a people, a group who can master the elements and bend them to their will. As Meira fights to get home, she'll learn more about her enemies, her people, and forces binding them all as one. Updated every Monday and Thursday. Crossposted on Wattpad. Cover art used with permission from MyaBeeArt on Etsy.
8 182 - In Serial43 Chapters
Sovereign of Creation
The ambition of the people has made this whole place a field of war, and when the abysmals race arrived, they took this one step further, transforming everything into a Hell.Asherit is a 6 year old little boy, due to he is the only hybrid between the human race and the abysmal race, he is hated by everyone except his mother whom, although she is Queen of the greatest Kingdom, is also a prisoner of the Abysmal King.In order to protect those that he loves most, Asherit will enter in a world full of wars, schemes, assassinations and mysteries where only the strongest Cultivators can survive.Join Asherit on this journey full of action, adventure, romance and fantasy, which will help him grow and become stronger to fulfill his goals. This webnovel is also available at scribblehub.com, wattpad.com and redsky194.blogspot.com
8 110 - In Serial54 Chapters
#2: Mister Sweet Talker || Beomryu √
Mister Series 2 of 5 taglish epistolary completedJust because of his consistency and bubbly personality, she started to get interested on him that it came to the point where she tried to entertain him, just so she can know if the guy will still be the same or not despite her cold treatment towards him.
8 134 - In Serial20 Chapters
crossed over
modern day au x no white star au og cale is busy feeling sorry for himself when he winds up in a modern au where he's dating alberu. meanwhile, his modern day self is now stuck in the fantasy world he came from with no idea how or why he got there just a lot of chaos because i enjoy hurting og cale taking some suggestions for other characters/relationships if they comply well with the story outline i have
8 229 - In Serial32 Chapters
Through Blood We Grow
Monsters come in many shapes. Men, animals, spirits, dreams, feelings. Sometimes it feels as if this world is a monster, simply waiting to devour you and all you hold dear. Grim knows this feeling better than most. Like many he was happy with his life, friends aplenty, a loving mother, a stable home, and a bright future. Like many that life was taken from him. But unlike many that wasn’t the end of him. He wasn’t devoured by the world, he was given a second chance and new name. With that name comes new people, new dangers, and a new outlook. This monster of a world wouldn’t consume him, he would grow. He would grow beyond the nightmares, beyond the weakness, and beyond his past. And the only way he can do that, is through blood.
8 204 - In Serial12 Chapters
Bottom Dream Oneshots
Bottom Dream with DSMP members
8 97

