《HASEENAH》PAGE 93&94
Advertisement
🌸 *HASEENAH*🌸
story &written
By👇🏻
Aysher Abbakar chuchu (meerah)
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
#
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-08144932303
Follow me on
*93~94*
Wuni ranan Mummy tayi tana zage zage, saratu kuwa ta kasa zaune ta kasa tsaye, ta shiga ta fita duk tana jiran zuwan Haseen.
K'arfe 5 na yamma kuwa Haseen ya iso, fita Haseenah tayi ta ajiye musu plastic chair dake ajiye a harabar gidan ta gefe wanda aka ajiye domin zama.
Umaimah ce ta kawo mai ruwa da drink da snack d'in da sukayi yau ta ajiye mishi.
Kallon ta yayi yace" ku dai ba a rabaku da wanan abu sannun ku da aiki"
Dariya tayi sanann tace" wanann aikin Aunty Haseenah ce"
Murmushi kawai yayi ba tare da yace komai ba.
Zuba ma Haseenah ido yayi yana kallon ta, sunkuyar da kai tayi tana Wasa da yatsun ta, kusan wasu mintuna suka d'iba a haka sanann ya daure yace" meyasa bakiso nayi ma daddy maganan auran mu? Ko dai yanzu kin dena sona ne?"
Da sauri ta d'ago ta kalleshi jin abinda ya furta.
Gyad'a mata kai yayi alamar eh.
Ganin batada niyar magana ya sanya shi cewa" tunda baki son magana dani shikenan barina tafi"
Mik'ewa yayi da niyar tafiya da sauri batasan lokacin da ta rik'o hanunshi ba.
Tsayawa yayi cak ya kasa motsa wa, da sauri ta saki hanun a hankali ta furta" am so sorry plx ba abunda kake tunani bane, amma ba komai gani nake kaman yayi wuri, amma ka samu Mummy Zuwaira ka sanar da ita duk yanda kukayi dai dai ne"
Sai alokacin yaji wani sanyi a ranshi, bai san lokacin da ya koma ya zauna ba, duban ta yayi sanann ya ce" Are U serious?"
Advertisement
Gyad'a mishi kai kawai tayi itama tana murmushi k'asa k'asa.
Nan ya fara cin snacks sunayi suna hira, jifa jifa take amsa mishi.
Can ta nisa tace " yaya Haseen dama inaso na maka magana kan komawa ta makaranta ne"
Duban ta yayi sanann yace" nima naso miki magana to amma se nayi shuru saboda nayi tunanin karkice daga dawowarki baki huta ba shiyasa"
Girgiza kai tayi alamar a'a.
" To ai ba a ciro result d'in naki ba"
" Eh zanje in Ciro"
" No ba saikin je ba in Zan tafi ki d'aukomun slip d'inki in tafi dashi"
Cikin jin dad'i ta amsa da to Nagode.
Nan suka cigaba da tattaunawa.
Can cikin gida kuwa saratu ce ta tsala wanka ta fito ta sanya kaya, zama tayi gaban mirror ta shek'a kwalliya, turaren ta d'auko ta bulbule shi duka a jikinta, ita kanta warin turaren be mata dad'i ba amma ya zatayi.
Kwallin ta bud'e ta shafa har yana gangaro wa, abun ba kyan gani.
Mummy ce ta shigo ta fara mata masifa me take jira da bata fita ba.
Nan saratu ta kalli kanta a madubi yanda tayi sai kace balamar rago, duban Mummy tayi tace" dan Allah Mummy ki ganni fa?"
" Dalla ki fita damuwar mu a samu biyan bukata, ko kin daina sonshi ne?"
Girgiza kai tayi.
Nan ta fice ko gyale babu, Baby da Umaimah dake zaune a palour suka ga fitowar ta, kasa gimtse dariyar sukayi suka tuntsire da dariya, Baby har da hawaye..
Ko kulasu batayi ba ta fice, Haseen da Haseenah ta hango zaune gefe, nan ta canja taku har ta k'arasa basu sani ba.
Warin turaren ta ne ya bugi hancin su , da sauri Haseenah ta dubi waye me wanann warin? Ido biyu sukayi da Haseenah, sunkuyar da kai Haseenah tayi tana dariya k'asa k'asa.
Advertisement
Haseen kuwa zuba mata ido yayi yana kallon ikon Allah...
Ita duk tunanin ta tarkon tane ya kama, dan haka ta hau rausaya tana fari da ido.
Dariya ma shi abun ya so ya bashi.
Kujera d'aya taja wanda ke gefen Haseen ta zauna.
Lokacin ranshi ya fara 6aci ga warin ya fara damun shi.
Dubanta yayi yace" ke lafiyar ki kuwa?"
Cikin wata murya tace" me ka gani yaya Haseen?"
Tooo fa, yau ga ikon Allah .
Ji yayi kaman zeyi amai hakan ya sanya shi toshe hanci ya dubeta yace" ke kinada lafiya kuwa? Rabon ki da wanka sati nawa? Kinji warin da kike yi amma kika iya shiga mutane?"
Sororo tayi ta na jin kalaman Haseen kaman yana zuba mata wuta..
Ganin yanda ta zuba mishi ido hakan ya sanya shi daka mata tsawa yace" ki dena kallona da wannan idanun naki marasa kyan gani"
Kasa daurewa tayi ta fashe da kuka ta mik'e ta shige ciki tana matsanancin kuka.
Baby da Umaimah suka sake kallon ta ganin duk hawaye ya jik'a kwallin da ta lapta ya gangaro sai kace wata boka.
Dariya suka sake yi sanann Umaimah tace" ga dukkan alamu maganin baiyi aiki ba kenan"
Dariya suka sake yi suka tafa.
Nan saratu ta sake cika tayi fam.
Mummy na jin kukan ta ta fito da sauri ta iske ta kan gado tana kuka.
Zama tayi tace" meye ne kuma?"
Cikin kuka saratu ta fara kora mata bayani...
Ran Mummy ya sake 6aci ta d'auka waya ta kira Aminiyar ta, ko gaisuwan arziki basuyi ba Mummy ta fara surfa masifa" amma wanann bokan d'an iska ne, abinda ya bamu ba wani aiki sai cin mutunci"
Da k'yar da shawo kan Mummy sanann tace" to ko dai batayi amfani dashi yanda ya dace bane?"
" To ina zan sani yanzu kam Ni talatu"
Duban saratu tayi tace " kinyi amfani dashi yanda nace?"
"Eh"
Kashe wayar Mummy tayi tace" karki damu k'ila an samu kuskure ne gobe zamu sake jarabawa, in Allah ya yarda kin aure shi an gama"
Dad'i ya cika saratu nan ta manta cin mutuncin da Haseen ya mata.
Sai wajan magrib Haseen ya kar6a slip d'in Haseenah sanann ya fito musu da kayan k'walamar da ya kawo mata ya tafi..
Kai tsaye gidan Mummy Zuwaira ya wuce, bayan sun gaisa ne ya sanar mata da abinda ke tafe da shi. .
Sossai taji dad'i nan tace ya sanar da daddyn shi duk yanda suka tsara shkann zata sanar ma Abba.
Cike da murna ya koma gida.
Bai 6ata lokaci ba nan ya sanar da daddyn shi, daddy ya ce ba damuwa ya faɗa ma Haseenar jibi zasuzo neman auranta.
Tsalle Haseen yayi ya rungume daddyn nashi yana godiya.
Mamaki abun ya ba daddy da Mummy duka, dan rabon da su ga farin cikin Haseen haka its been a while, tun kafin Haseenah ta 6ata.
Murna yayi tayi ranan da k'yar ya iya bacci, tunanin Haseenah ne ya sa shi gaba, sai yanzu yake dana sanin meyasa bai siya mata waya ba?
Nan ya ba kanshi amsa nan da kwana uku zai siya mata in Allah ya yarda.
Haka ya kwana cikin shauk'i da farin ciki, hango irin rayuwar da zaiyi da abar k'aunar shi kawai yake.
Nikuma nace Allah ya nuna mana Ameen....
For comments 08144932303
Advertisement
- In Serial349 Chapters
Deity Hero: Me! Gaining Disciples Makes Me Stronger!
"Xuan Yi was transported into the fictional world and became an elder of the Black Sword Sect! The moment he entered the world, he was at the Sea-Splitting Rank! He awakened his disciple accepting system. The more absurdly powerful his disciple, the stronger Xuan Yi would become! Others may depend on cultivation to raise their ranks, he raised his by accepting disciples! Although he was an elder, had anyone ever seen an elder whose strength was hundreds or even thousands of times higher than that of the sect leader?
8 1330 - In Serial11 Chapters
Solitary Elevation
"Did you hear that story about the biggest mountain in the world? I couldn’t get over it." the book is about some guy that likes mountains... yea that's about it... we got some LitRPG as well, litRPG? litrpg? That's the system/fantasy genre right? Ahh, doesn't matter read the book, you might even enjoy it! OHH yea, btw I just added all the content warnings to give me room so I don't restrict the way the story can go if that makes sense. So don't go immediately expecting sex, if we get there we get there.
8 154 - In Serial16 Chapters
Reincarnated Monarch
An ordinary office worker. That was who Kim Dongsoo was, a Bachelor of Engineering. Until he got killed due to a accident on his way home. A noble heir. That was who Vincent Sutton was. Heir to the Viscounty of Northwind. Until he woke up with memories of Kim Dongsoo, and his whole world changed. A story of excitement, adventure and, of course, monarchy. Cover image from Pintrest: https://www.pinterest.com/pin/672866000562624092/
8 100 - In Serial16 Chapters
Devious Dungeon [Dropped]
A man seeks his own path, deviating from the norms. For his own goals and desires, he seeks a path uncharted. For the sake of satiating his curiosity, he sought to tresspass in the domain of the divines. Achieving something none had before, he transcended his limits. Denied was he from fruits of his labor, cheated and cast away to be forgotten. Yet he was given a chance, a gamble to reclaim what was lost. Did he lose more than he gained, or did he stumble upon a yet another path untrodden? Hiya, first story I started to write. This story has no definite goal as of yet, as I'm using it to improve my writing skills as english isn't my native language. Main theme is going to be dungeon building. Is the theme cliché? Well yes, yes it is. And I don't care, as I'm going to try add some new twists and turns while experimenting with my writing. In the future, story will contain more mature content, you have been warned. Thus speaking, constructive criticism is welcomed, random bashers and weeaboos are promptly ignored. Updates are sporadic in nature, happening when inspiration strikes. I do not own the copyrights of the cover. These rights belong to the respective artist.
8 142 - In Serial4 Chapters
There was a girl named serenity Walter who Moved from Chicago because of her drunk mother who always had sex with other man and was abusive. She moved and had a stepmother and made new friends. But then found David Reyes.
8 89 - In Serial26 Chapters
,,Fan"
TAEHYUNG POV.What are you doing here? - I asked. Can I come in first? - Jungkook asked as I nodded and let him inside, closing the door behind him. Kookie took off his mask and hat then looked at me.Are you okay? - He asked......As Jungkook posted photo on instagram he looked back at Taehyung.Muffin, I think that I can't to control myself anymore. - Jungkook said.Then don't control it. - Taehyung said.
8 138

