《HASEENAH》PAGE 101&102
Advertisement
🌸 *HASEENAH*🌸
Story &written
By👇🏻
Aysher Abbakar (meerah)
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
#
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS- 08144932303
# http://
Follow me on Aysherabbakar
*101~102*
Jallabiya ya Sanya sannan ya d'au Key ya fice, agogon hanunshi ya kalla k'arfe 12:30 na dare, bai damu da lokaci ba, motar shi ya shige yayi horn me gadi Ya bud'e sannan ya fita aguje.
Zaga Garin kawai yake ba tare da yasan inda ya nufa ba, har wajan k'arfe 2 yana abu d'aya, ganin wajan shiru a dole ya juya ya dawo gida zuciyar shi cike da tunani.
Ji yayi cikin shi na murd'awa sai a lokacin ta tuna da tun breakfast har ynxu ba abinda yaci.
Kitchen ya shiga ya dafa Lipton sannan ya fito yana sha a hankali ba don yana jin dad'i ba.
Haka ya zaune har aka kira sallan asuba.
Alwala yayi ya fice zuwa Masallaci.
Seda gari ya fara wayewa sannan ya mik'e ya dawo gida yayi wanka sannan ya fita.
Ya rasa ya inda ze fara, duk wanda ya gani sai ya tare ya nuna mishi hoton haseenah amma baiyi sa'an sanin wanda ya santa ba.
Sallah ne kawai ke tsayar dashi yana yi kuwa zai ci gaba da yawo.
Da yamma mummy zuwaira ta Sanya haseenah suka tattaro kayan su suka fice a gidan, lokacin kuwa mummy ta fantama gari nema wa saratu maganin Sa'a akan haseen da kuma lalata auren haseenah.
Sai magrib ta dawo duk ta gaji, gashi gidan taji shuru babu su haseenah babu saratu ta fice yawo.
Tsuka ta ja sannan tace " an fita yawon iskanci kenan"
Sai bayan isha saratu ta dawo, mummy kuwa na zaman jiran dawowar haseenah,
Har wajan 10 ganin basu dawo ba ya sanya mum fita wajan idi me gadi.
Tanbayarshi take ko yasan inda haseenah ta tafi?
Girgiza mata kai yayi alamar a'a sannan yace" na dai ganta sun saka akwatina a mota sun fice dukan su ko tafiya sukayi oho"
Hankalin mummy ba k'aramin tashi yayi ba jin ya ambaci tafiya.
Da sauri ta juya ta shige cikin gida tun daga k'ofa ta fara k'walla ma saratu kira.
Da gudu ta fito a tunanin ta wani abun ne ya faru, ganin mum tsaye ya sanya ta cewa" haba mummy wlhy har kin razanani"
" Razana na gaba kuwa dan ubanki, Ni na fice naje can ina fad'i tashi dan ganin na mallaka miki abinda kike so kekuma kin k'ule d'aki hankalin ki kwance ko?'
Tura baki tayi sannan tace" to gani nan ai"
Duka mummy ta kai ma bakin saratu sannan tace" to dan ubanki haseenah bata gidan nan, idi yace min ya gansu da manyan akwatina sun fice basu gidan Dukansu.
Advertisement
Yamutsa fuska saratu tayi sanann tace" to Ni mummy meye damuwata da barin gidan, ai abun farin ciki ne"
Shuru mummy tayi maganganun saratu na k'ona mata zuciya sannan tace" ohhhh kin manta yau saura kwana 28 auren ta da haseen?"
Zabura saratu tayi ta dubi mum tace" yaushe aka saka ranan auren mummy?..
" Ban sani ba"
Tana fad'in haka ta juya ta bar saratu zaune a k'asa.
Kuka saratu ta saka tana birgima wai bazata yarda ba se ta kashe su duka...
Haushi da ya dad'a Kama mummy daga cikin d'aki tace" wlhy In baki tashi kin fice mun ba sena karya ki, banza shashasha kawai"
Kuka saratu take tana cewa mummy ta temake ta Amma ko kallon ta mummy Bata yiba.
Tashi saratu tayi ta shige d'aki, jakarta ta bud'e ta ciro kwalin sigarin ta da lighter ta shige toilet.
Zama tayi kan toilet ta kunna ta fara busawa, yana k'arewa zata sake kunna wani.
Seda ta sha kwali d'aya sannan ta hak'ura, gaba d'aya wajan ya d'au hayak'i ba abinda kake gani.
Ji tayi kanta na juyawa da k'yar take iya bud'e idon ta, tashi tayi ta wuce bedroom d'inta ta zube kan gado had'e da dafe kai.
Bata san lokacin da bacci ya d'auke ta ba ba sallah ba salati.
Washe gari da yamma su haseenah suka shirya suka fice a motar ta ita da su baby, Umaimah da Aaman.
Dukan su dogayen riguna suka sanya amma kowa da colour nashi, haseenah dake sanye da bak'i ta rolling gyale ta Sanya glasses a fuskanta.
Shiga motar sukayi suka harba titi, kai tsaye wajan shak'wata suka nufa, nan ta ajiye motar ta suka fito.
Neman waje sukayi suka zauna aka kawo musu menu.
Kowa ordering abunda yake so yayi suka fara shan ice cream suna hira.
Umaimah na faman d'aukar su a hoto, nan suka 6ata lokaci ana k'ok'arin kiran magrib sannan suka mik'e sukayi ordering snacks suka fice.
Hold up ne ya rik'esu wajan traffic, tsuka haseenah tayi sannan tace" wannan zasu b'ata mana lokaci gashi mum tace kar muyi dare"
Farar motor ya hango dake d'an gaba da shi, kallon window motar yayi wajan zaman driver Amma bai ci sa'ar hango wanda ke driving d'in ba.
K'irjin shine ya fara dukan uku uku, gani yayi me motar ta sako hanunta ta window ta dafe kai.
Zoben da yagani hanunta ya sanya yaji ta burge shi, haka kawai yaji yana son ganin yarinyar..
Matsawa da motar shi yayi ya iso dai dai wajan da take, gaban shi ne ya bada sautin dammmm, ganin wanda ke cikin motar Ba k'aramin rikicewa yayi ba, k'ok'arin bud'e motar shi yayi dai dai lokacin traffic light ya Basu hannu.
Advertisement
Ganin zata 6ace mishi ya sanya ba ma motar wuta ya rufa mata baya.
Duk da ta mishi nisa amma yana iya hango motar su, wata kwana yaga ta shige nan shima ya bi, amma sedai me? Ba ita babu labarin ta, kalle kalle ya fara yi dan ganin hanya ya rabu biyu, ya rasa wanne tabi, dukan sitiyarin motar yayi yayi wata k'ara ya buga kanshi kan sitiyarin ya fitar da wani iska me zafi.
Dafe kanshi yayi da yaji na faman sara mishi, da k'arfi ya furta " Haseenah why?"
Yakai kusan minti talatin anan ya kasa motsawa, duk wanda ya gani se ya tsare ya tanbaya ko ya ga wata farar mota amma babu.
Komawa gefe yayi ya parking motar shi ya buga tagumi,Allah ya bashi ikon ganinta amma ta 6ace mishi, dafe kai yayi yana kiran sunayen Allah kan ya temake shi ya bayyana masa haseenah a karo na biyu.
Ganin har lokacin ba motor makamanciyar Tata ya Sanya shi ta da motar jiki a sanyaye ya bar wajan.
Saratu kuwa da mummy tayi a gaba tana kuka.
A dole ta saurare ta Nan ta nata alƙawarin zata aura haseen ko me ze faru.
Haka sameer ya rink'a yawon shi ya koma gida.
Bayan kwana biyu ya sake dawowa anguwan.
Tsayawa yayi daga nesa yana ta faman waige waige, wani yaro ya gani ya taho, da sauri ya fito a motar ya tsare shi, nan ya nuna mishi hoton haseenah.
Gyad'a mishi kai yaron yayi alamar ya gane ta.
Da sauri sameer ya dube shi yace "da gaske kake ka santa?"
" Eh na santa sunan ta Haseenah"
Wani sanyi ne haɗe da farin ciki ya kama shi.
Nan yace ma yaron "zaka iya kaini gidan su?"
Nan ya shiga motar suka kama hanya.
Tsayawa sukayi bakin gate d'in yana neman d'an aika.
Gani yayi an buɗe gate d'in, wata budurwar yarinya ce ta fito, sallama ya mata ta amsa sannan yace" dan Allah haseenah nake nema"
Shuru tayi sannan tace " to barina mata magana"
Tana shiga ta samu haseenah ta fito wanka tana shafa mai.
Kallon ta tayi sanann tace" Aunty kinyi bak'o"
Da sauri ta dubi baby tace" Ni Kuma?"
" Eh"
" Bana nan"
Nan baby ta fara magiya tana bata hak'uri amma ko kulata batayi ba.
Daga waje taji muryan mummy na cewa" jeki bud'e mishi guest palour tana zuwa"
Tura baki haseenah tayi a shagwab'e tace" mummy Dan Allah wlhy...
" Ki tashi ki shirya kije ki sallame shi"
Harara ta daka ma baby tayi k'wafa.
Umaimah dake kitchen Bata San abinda ake ba.
Nan baby ta fita ta k'arasa dashi palour sanann ta fice..
Kusan 30mns haseenah bata fito ba, seda mummy ta koro ta sanann ta fice sanye da atampa dogon riga.
Gaban ta ne taji na fad'uwa saboda jin warin turaren da tayi, kuma ta rasa a ina tasan me irin turaren.
A hankali tayi sallama ta shiga.
Ba tare da ta d'ago kai ba ta shiga ciki ta zauna nesa dashi.
Tunda ta shigo ya zuba mata ido har ta zauna amma bata d'ago ba.
Jin Muryar shi tayi ya doki kunnenta jin an ambaci sunanta.
A razane ta d'ago da sauri tana son gasgata me Muryar.
Zaro ido tayi bakin ta na rawa ta mik'e tsaye tanuna nuna shi.
Kasa furta komai tayi sai hawaye.
Mik'ewa shima yayi ya k'araso ya zube kan gwiwar sa ya fara magana cikin wata irin murya ya fara cewa" haseenah mesa Zaki gujemu? Me muka miki? Kinsan halin da kika samu ciki? Kinsan me kika bari me ya faru bayan tafiyar ki? Kinsan halin da Ammi ta shiga da Ni kaina dalilin ki?"
Shuru yayi jin ta tsananta kuka, Muryar ta ba k'aramin k'ona mishi zuciya yayi ba, banda sautin kukan ta ba abinda ke tashi.
Nan ya cigaba da cewa" gidan mu ya zama kaman gidan mutuwa, ga Mahmud can ba lafiya dalilinki"
Toshe kunnenta tayi da duka hanunta biyu tana kuka.
Shima hawayen yake yi yana mata magiya yana fad'in" ki temakeni ki temaki rayuwar 'yan uwana ki dawo cikin rayuwar mu"
Shuru duka sukayi.
Nan ya cigaba da cewa" haseenah ki temakeni ki aure Ni na miki alk'awari zan miki duk abinda kike so, plxxxx haseenah"
Ya k'arashe maganar had'e da zubewa gabanta shima kukan yakeyi..
Ji tayi jiri na neman zubar da ita ga kanta dake faman juyawa.
Da gudu ta fice daga palour ta nufa hanyar shiga gida lokacin Abban su baby na parking.
Ganin halin da take ciki ya sanya shi kallon inda ta fito.
Fitowa yayi a motar sannan ya nufa yanda Sameer yake.
Ganin shi yayi durk'ushe ya rik'e kai yana kuka kaman k'aramin yaro.
Hakan ya tabbatar ma Abba akwai wani babban al amari...
Kama hanun shi kawai Abba yayi ya mik'ar dashi tsaye.
Hanyar palour shi suka nufa ya zaunar dashi.
Ruwa ya d'auko a fridge da cup ya zuba ya mik'a mishi.
Ba musu ya amsa hanun shi na rawa , da k'yar ya iya kur6a sau d'aya sannan ya ajiye.
D'aki Abba ya wuce ya canja kaya sannan ya dawo ya zauna ya fuskanci Sameer sannan ya fara cewa....
Cikin gida kuwa haseenah d'aki ta shige ta kulle k'ofa ta fad'a kan gado ta saki kuka me k'arfi.
Abba ne yace" ka nutsu ka fad'amun me yake faruwa?"
Da k'yar Sameer ya fara da .....
For comments 08144932303
Advertisement
- In Serial34 Chapters
Avatar: The Wild Lands (A Medieval 'Avatar: The Last Airbender' Fiction)
Stormy clouds hover over the Wild Lands. The Raiders of the North Sea, in the name of the Spirits of the Deep, ravage the misty shores. The Empire of the Holy Flame’s serfs hide in the fiefs of Fire Knights and guard themselves against the Dark Spirits that roam the wilds. The Caliph in the East, leading his Holy Army, heads towards the hopeless Heaven's Shrine. There, the beleaguered monks listen as the Voice of the Wind predicts the coming of a saviour. The saviour who will teach harmony to a world that has forgotten peace. This savior is the Avatar, the ancient embodiment of balance: the one who wields the Four Elements to establish unity among the Four Nations, as well as between humankind and spirits. (This is a non-profit fan-fiction. Avatar: The Last Airbender & Avatar: The Legend of Korra are a property of Nickelodeon, Michael Dante DiMartino and Bryan Konietzk. We support the official release)
8 212 - In Serial48 Chapters
Kingmaker
It has been fifteen years since Thael left the Wraith Order, one of legend of the Arcadian Empire only spoken in whispers. His self exile is interrupted by his past when he finds one of his fellow Wraiths, Verena, in his home. The Prince of the Arch King has been taken from the capital itself by rebel Wraiths, and they would need the mortal man who made the impossible possible to rescue the Prince before he is sacrificed for the Prophecy of the Black Sun, where it is foretold the spilling of royal blood would allow mortalborn to reach Magehood. For fans of Grimdark Fantasies such as authors John Gwynne, Mark Lawrence and Joe Abercrombie!
8 194 - In Serial25 Chapters
A Quest in Egypt ( A Story Of Jinns And Witches Book 1 )
What do a 13 years old witch and a 13 years old Jinn have in common besides their age? Usually nothing except for a horde of evil creatures chasing them, the discovery of powers they never knew they had, sharing the same hotel in Egypt, discovering a group of frightening human traffickers plus their victims and last but not least an unshakable bond of friendship.
8 77 - In Serial27 Chapters
ADOBEA
ADOBEA is a true life story of a young girl whose parents died when she was just a week old. They had a fatal motor accident on their way to name the child. The accident occurred just few kilometers away from the Church. Her parents perished. Their child mysteriously survived. Her poor grandmother named her ADOBEA. Due to lack of funds her grand mother took her to an orphanage.Her suffering became endless. She was raped at age ten in the very orphanage that was supposed to protect her. Adobea was arrested and jailed. Her innocence saved her from a bigger demon to a lesser one. Mystery, faith, acrimony, suspense all brewed in one pot. Would she ever find that happiness after realising that her parents were killed by her Uncle to inherit the Father's estates? The uncle had all these while thought Adobea had died with the parents. He realises Adobea was still alive....His quest was now simple...to kill ADOBEA...The true life story of ADOBEA is filled life's stories. The suspense is UNPREDICTABLE...
8 103 - In Serial17 Chapters
Greyskin
Warning, this is a mature fiction. Darker than Beast fiend, more ruthless and bloody. Slavery, incest and rape present amongst other things. Be warned.In the world of Imilaris, different forces all live in relative peace. The thirteen gods strive for power, hoping to collect enough to prove their worth to others. Their patrons live in this world, full of magic and monsters. And it is as beautiful as it is dangerous. Demons came to the world long ago, they fought, they conquered and they were defeated. Confined in their corner of the world, they slither, waiting for their time.Within that territory, in a cave, a boy is born. He is a descendant of a powerful empire, destroyed years ago, carrying blood of a goddess and he is also a demon, a foul thing full of the scourge, the fel energy all demons carry. He is now set loose on the world, to tip the scales however he wishes.
8 213 - In Serial23 Chapters
The Past, The Present And The Future Shadow Weaver × Reader
basically you are replacing mara in the story and after the ship crashed you didn't die instead you were frozen for 1000 years and adora has found you so there is 2 she ras and your love interest is shadow weaver in this story you also will be able to do sorcery pls no hate cause this the first story I'm writing and I'll try to update as quick as I can and I will also try to stick closely to the story line My writing is also a weee bit wonky And it would be lovely to get some feed backShe ra is owned by DreamWorks but this is my own storySome of the main characters may not be mentioned as often because the story revolves around you and ShadowPS if you are NB or a He/Him or unlabeled reader you will have to insert your own pronouns I'm so sorry
8 216

