《HASEENAH》PAGE 121&122
Advertisement
🌸 *HASEENAH*🌸
Story & written
By👇🏻
'''Aysher Abbakar ChuChu (Meerah)'''
® *Real Pure Moment of Life Writers* *P.M.L*💭💭💭
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
#
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
Follow me on Aysherabbakar
*121~122*
Gidan mummy zuwaira ya dad'a cika da mutane, yau saura kwana biyu a d'aura aure dan haka bak'i na nesa sun fara isowa.
Da safe masu aikin da mummy ta yo haya suka fara gyara gida masu abinci na yi.
Da wuri suka tashi suka shiga wanka nan suka zauna tare da su saratu da friends dinta dan yin breakfast.
Aaman ne ya shigo yana sanye Cikin English wears, Cikin Riga yellow colour anyi rubutu a gaban rigan da blue, wandon shi ma blue jeans ne se k'aramar sneakers a k'afarshi, hanun shi d'auke da k'aramar flask me feeder a jiki ko ba a tanbaya ba kasan custard ne a Ciki.
Ya dad'a wayo da kyau ga haske Kama suke sossai da haseenah.
Kai tsaye wajenta ya nufa itama ta mik'a hannu ta hugging d'inshi, rabon da ta rik'e shi a jikinta tun da aka fara hidimar binkin nan, sedai taga wucewar shi.
Zama yayi kan cinyarta yace" aunty ina kinje? "
Dariya tayi tace" babu ina nan Aaman Kaine de ka gudu"
Be san me ze cemata ba kasancewar ba wani magana sossai ya iya ba, mik'a mata feeder yayi dai dai bakinta yace" sha"
Kar6a tayi ta ajiye ta fara bashi kwai a baki.
Tunda ya shigo saratu take kallon shi, to wannan d'in waye? Tanbayar da ta kasa samun amsa kenan.
Kuma gashi yana Kama da haseenah ko dai d'an yayar umman haseenah ce?
Kasa hak'uri tayi Cikin murmushi tace" aunty haseenah wannan fine boy d'in fa babyn waye?"
Cikin mamaki haseenah tace"baki gane Aaman ba? "
Gyad'a kai saratu tayi alamar eh.
Haseenah tace" yaron Ummah nane fa Wanda aka haifeshi"
Xaro ido saratu tayi tace" shine ya girma haka? Ji kyau dan Allah, wlhy he's super handsome"
Advertisement
Dukansu dariya sukayi suka cigaba da breakfast, Aaman kuma na musu tad'i suna ta dariya.
Kasancewar yau juma'a ne ta Kama yau za'ayi walima washegari kuma a d'aura aure.
A gidan za'ayi shiyasa kafin wani lokaci an gama gyara ko ina.
An buga temples a ta bayan gidan an jera carpets da kujeru da tables.
Ko wani table kujera hud'u ne kewaye da shi.
Ta can gefe kuma chefs ne wato masu girke girke su hud'u kowacce da apron jikinta, gaban table d'in da suke kuma abinci ne jigbe Kala Kala da snacks.
An k'awata wajan se ya zamana kaman liyapa za'ayi.
Wajan k'arfe hud'u mutane sun fara cika.
Dan haka amare ma na ciki ana shiryasu.
Cikin lipaya aka shiryasu Maroon colour da yasha white stones a jiki.
Ba k'aramin kyau sukayi ba.
Ba tare da 6ata lokaci ba aka fara gudanar da walima.
Sossai aka fad'akar da su Wanda ya Sanya jikin su yin sanyi, haseenah ko tafi kowa kuka a Wajan, abun mamaki Harda Saratu a kuka dan ta tsorata sossai kuma ta k'udiri niyar canja rayuwarta.
Anci an sha anyi pictures da videos sannan aka watse.
Misalin k'arfe goma kuwa su saratu suna tare da su Haseenah a d'akin su.
Zama sukayi duka sunyi shuru an rasa me magana.
Can Umaimah ta kalli haseenah tace" sis gobe by this time bamu tare fa an raba mu"
Haseenah da idonta ya cika da hawaye ta rasa me zata ce ma.
Baby da yake itace k'aramar Cikin su seta fara kuka.
Matsowa kusa da su tayi ta shiga tsakiyansu ta rungumesu, kukan ta ya tsananta sossai, ba k'aramin shak'uwa sukayi ba, gashi zasu rabu lokaci d'aya.
Umaimah ma kukan ta fara yi, haseenah da yake itace babba ta daure ta share hawayenta sanann ta ce" haba mana kuyi hak'uri, dukanmu fa gari d'aya zamu zauna, when ever we felt like seeing each other we will"
Su saratu ko zuba musu ido sukayi suna ganin irin tsantsan kulawa da shak'uwa wajan su haseenah.
Dee ce tayi murmushi tace" kuyi hak'uri ku gode ma Allah, gwanda ku zakuyi auren ma mukam ai gamunan duk mutanen banza ke zuwa mana"
Advertisement
duban su haseenah tayi Cikin tausayawa tace" hakuri zakuyi ku gyara rayuwar ku, ku nutsu se kuga Allah ya tausaya muku Cikin k'ank'anin lokaci se kuga komai ya zama tarihi"
A tare suka had'a baki suka ce " in shaa Allah "
Haka suka cigaba da hirar su har Wajan 12 na dare, Aaman kam yayi bacci yana jikin haseenah, dan yau so take su kwanta tare dan tasan Daga gobe ganinshi ze mata wahala.
Dukan su a d'akin suka kwana dan su saratu ma basu tafi d'akin ba.
Washe gari yau kenan ya Kama asabar dan misalin k'arfe goma za'a d'aura aure.
Tun daren juma'a Haseen ya fara had'a kayan da ze tafi dashi abuja kai kace shine amaryar.
Mum ce ta shigo d'akin, ganin akwatina tayi a kan gado har uku, duban shi tayi tace " wannan kayan fa"
Sameer ya kwashe da dariya yace" mummy wai kayan da ze tafi dasu gidan aure ne"
Salati mum ta fara yi tana tafa hannu, girgiza kai tayi sanan tace" da alama wannan aure yana neman zautar da kai, Anya kuwa k'alau kake? "
Dariya ma yayi sanann yace" mum dan Allah bayan na tafi, incase in nayi mantuwa a biyoni dashi plx"
Kasa magana tayi kawai ta juya ta fice.
Duban agogo sukayi lokacin 8:30 ne.
Wanka suka shiga suna fitowa mum ta had'o musu breakfast, da k'yar Haseen ya nutsu yaci dan shi cewa yayi suyi sauri kar suyi latti.
Harara Sameer ya 6alla mishi yace" dalla malam in zaka nutsu ka nutsu yanxu fa ko 9 beyiba zaka bi ka d'aga ma mutane hankali".
Ganin masifan zeyi yawa ya sanya shi zama suka fara cin abincin.
Can su haseenah hankali ya fara tashi, kasa cin abincin ma tayi, idonta yayi tsuru-tsuru, tunanin ummanta kawai takeyi, Ji tayi komai ya koma mata sabo.
Zuciyanta zafi yake mata ta kasa yin komai.
Sun mata rarrashin duniya Amma tak'i.
Umaimah ce ta kira mummy ta sanar mata.
Nan mummy ta Sanya ta gaba seda ta shanye tea sannan ta barta.
Kowa na cire kayan da ze tafi dashi Amma Banda Haseenah.
Bayan Umaimah ta gama nata ne ta d'auko akwatinan Haseenah tace"wanne zaki tafi dashi"
Girgiza mata kai tayi, bata sake kulata ba ta bud'e, duk kayan da tasan sabi ne kuma haseenah tanaso ta had'a mata a akwati d'aya, inner wears da sauran tarkacen da zata buk'ata ta had'a suma a akwati guda.
Sauran kayan ta dubeta tace " sis kinada Wanda zaki basu ne? "
A hankali tace" ba ma su suratu su cire Wanda suke so sauran suyi kyauta dasu"
Aiko murna Wajan su saratu ba a magana ita da friends d'inta.
Wardrobe haseenah ta bud'e ta d'auko wata k'aramar jaka, jakanda ta baro gidan su Sameer da shi tunda ta ajiye bata sake bud'ewa ba.
Bud'e jakar tayi ta ciro set d'in English gold Wanda Sameer ya siya mata ta saka a jaka.
Ganin yanda yake walwali kasan ba k'aramin sark'a bane.
Baby ce ta furta" Wow sis wanann golds d'in fa"
Murmushi kawai tayi tace" nawa ne"
A jakar ta saka sannan aka saka key aka rufe.
Mum ce ta lek'o tace su shiga wanka dan ana d'aura aure zasu wuce dan tsakanin kano da Abuja akwai d'an tafiya.
Jiki a sanyaye suka shiga wanka.
Tun a toilet haseenah ta fara aikin kuka, su umaimah da baby duk sun fito har an fara shiryasu Amma bata fito ba.
D'aya Daga Cikin sisters d'in mummy ne ta shigo tana gud'a tana fad'in aure ya tabbata.
Cak haseenah taji numfashinta ya d'auke na wasu lokuta.
Sulalewa tayi a Cikin toilet d'in ta fad'i.
Jin k'arar fad'uwan abu ya Sanya su nufan hanyar toilet d'in da gudu.
Allah ya temaka bata saka key ba.
Ganinta sukayi zube a k'asa d'aure da towel da alamu tana shirin fitowa haka ta faru.
Da gudu suka shiga suka fara jijjigata.
Ganin bata motsi ya sanya baby k'walla ihu ta fita tana kiran sunan mummy.
For comments 08144932303
Advertisement
- In Serial50 Chapters
Re:Lovely
One day Noel finds out that there is indeed an afterlife, she's also given a second chance. While keeping her eye on the prize our heroine journeys through this strange new world causing various minor shenanigans and chaos, enjoy!Based off of and inspired by Re:Monster, I will be taking liberties as I please. By that I mean this is not completely accurate, enjoy.... I hope someone enjoys this... please don't hate me... I love you guys!Rating: M 18+ Strong Language, Innuendos, and cookies...*cough* Sexual Content *cough*Edit: Some guy said I should point out that there is lesbian sex in here. Basically, if you don't like seeing that sort of thing, don't read on. I'm completely fine with people who just don't want to read that. I am not fine with people who are homophobic, seriously, go away if you are. I don't want you here.
8 246 - In Serial11 Chapters
Gilded
A child experiences the unknown during his awakening, exposing him to the cosmic truth. He spends the next seven years designing, hiding, waiting for the perfect time to start his plans. Now nineteen, he sets his schemes in motion, doing anything to achieve his goals. On hiatus atm
8 94 - In Serial7 Chapters
ZombieMart
ZombieMart is a story about three teenagers surviving a zombie outbreak in the Appalachian region of the United States.
8 242 - In Serial7 Chapters
The power of scrolls
Devan a man who is considered a NEET on Earth has been transported to another world called Alia.A world filled with magic and monstrous creatures.Devan was born as the third child of Eric Clovis the Baron of the Digrave Key an ancient battlefield in the ancient era. Plotted by one of his older siblings he was left for dead in the outskirts valley in the Wretched forest. Picture used in the cover is not mine. Courtesy of pngtree https://www.pinterest.co.uk/pin/564568503287542826/
8 120 - In Serial14 Chapters
Legacy of Blood
Ao Ruang lives in a village isolated from the outside world. Due to a tragic fate he finds himself far away from his home on the brink of death. Only to be entrusted with the legacy of a near extinct race.A Legacy he must embrace.A Legacy that fills humanity with suspicion and hate.A Legacy written in blood. Hello Author here!I hope you all are enjoying my take on a cultivation story. I wanted to take elements I enjoy from cultivation novels while avoiding some of the tropes and insane power creep. I want to keep things as grounded as possible. The story is a bit quick paced in the start, but you will find that it slows down to a decent pace later on. The romance is going to be a slow burn and I want to keep it a bit of a surprise. While our protagonist Ao Ruang is the main man of the story their were will be times other characters will get some love also.Lastly, there will be occasional goals from latest chapter if those goals are reached I will release a bonus side chapter that focuses on other characters we have met before and I'm considering having polls to decide who the side chapter will be on.Please consider supporting me in anyway you can. For now I'm just looking for people to review, suggest to others, and interact.Respectfully,Joseon Walking
8 159 - In Serial17 Chapters
Envy
Are memories what make us human? Or is it something else? Follow our protagonist as she travels to another world just after she has recovered from an accident that left her barely alive and with no memories. She only survived, because of an experimental treatment that she had undergone, but something went wrong, something that changed her forever.
8 73

