《UQUBAR UWAR MIJINA》Part 30/31
Advertisement
UQUBAR UWAR MIJINA
(Based On True Life Story)(Full Of Sorrow)
https://www.facebook.com/groups/
1569379426621615/
*~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION
~*
*_~ We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain~_*
Story Nd Written By
Khadeejaht Hydar
Young Novelist.
Dedicated to my
Beloved Baby Fatima Sulaiman Allah ya rayamin ke.
(30)&(31)
To bayan naje border na shiga niger daganan nayi abidjan don sayo kaya,to Alhamduliilah nakai lafiya kuma nasiyo kaya na abinda yakai miliyan hud'u,
To abinda yafaru dani bazan tab'a mantawa dashi ba,shine silar rugujewar rayuwata.
Bayan nabaro Abidjan nazo border dake tsakaninta da Niger custom suka tsayar damu,suka k'arbe duka kayayyakinmu.
Tashin hankali Wanda ba'asa masa rana na shiga,don mafarkin danayi ne ya fad'omin.
Kuka na fashe dashi don ganin basuda niyyar bamu kayanmu,mun kwashe tsawon awa hud'u amma babbansu yak'i kulamu.
Hak'ura mukayi gaba d'aya muka bargun,zuciyata duk ta cunk'ushe don bak'in ciki.
Gabanane ya fad'i tuno da mafarkina,subhanallah na furto tare da karanta innalillahi wainna ilaihirraji'un Allah ajirni fil musibati haza wakhalifni khairun minha,wannan addu'ar ita yakamata mutum yana karantawa aduk lokacin dawani abun yasameka bawai mutum yana ihu ba,Allah yasa mu dace Amin.
Bayan nazo Lagos se wannan matar ta fad'omin,k'iranta nayi tasanar dani inda take,nacemata ganinan zuwa,tace"...se nazo."
Cikin mota ne nake tunanin abinda ke faruwa ga rayuwata,bangama tunani ba wayata tafara ringing,ganin wata y'ar uwarmuce yasa na d'aga,bayan mun gaisa takecemin Fatima yanzu haka ina gida wata mata daga kano takawo gawar y'arki Fatima,ido na zare cikeda fargaba nace"...shikenan narasata na rasa Fatima mafarkina yazama gaskiya,kawai sena saka kaina tsakanin cinyoyina ina kuka mai tsuma rai dasaka tausayi ga duk mai sauraronta,haka har muka iso unguwar.
Advertisement
Unguwace mai kyaun gaske kunsan de yadda Lagos yake da gina ginan manyan gidaje ga kyau da tsari,unguwar gaba da baya gate ne,bayan Na sauk'a nak'irata tamin kwatance har na iso.
Da fara'arta ta tarbeni tana mini sannu da zuwa,bayan mun gaisa tace"... yanzu har kin kai kayanne ko kinbadane?,kuka na fashe dashi nan na fad'amata abinda yake faruwa,hak'uri tabani kan cewa nayi hak'uri Allah yana tare da ni."
Na k'ara dace mata ina hanya aka k'irani aka sanar dani rasuwar y'ata, tace"... Dama kina da y'a?,nace".. Eh inada yara biyu,nan nabata labarin rayuwata ina kuka tana kuka,nima nayi kuka lokacin da take bada labarinta na rayuwa,ba'aiyawa mutum ko kad'an,wasu burinsu su lalata rayuwar jama'a to Allah ya karemu da mugun ji da mugun gani Amin.
Kuka naci gaba dayi saboda rasa Fatima danayi,haka matar tadinga bani hak'uri har nasamu na d'an tsagaita.
Tace"....toh Yanzu zakije yobe d'inne ko yaya?,nace"...inason naje amma ina tsoron kar akamani a kano saboda dukiyar Hajiya."
Tace"....insha Allah bazasu kamakiba kiyita addu'a,to bayan sati uku a gidan Matar nakama hanyar kano a sace a tsorace don tsoron kar'akamani a d'aure ni.
Bayan naje yobe ne natadda gidanmu yananan yanda yake,iyayena naganina suka fashe da kuka,Rungumesu nayi ina kuka suna kuka.
Mama tace"....Fatima haka Allah yaso sa rayuwarki zamuci gaba da miki addu'a,Allah yajik'an Fatima ya gafarta mata,magana ma kasawa nayi se kuka.
Mama tace"....satin dayawue ina zaune a gd ni k'adai naji sallama,bayan nafito naga wata mata mai kud'i ga babbar mota. "
Bayan mun gaisa ko ruwa batashaba,tafara mini bayanin abinda yakawota, tace"...kinzauna a gunta tunda kikabar gida,to bayan tafiyarki Abidjan Fatima ta fara k'enda Wanda hakan yayi sanadin rasuwarta"
Advertisement
Tazomana da gawar Fatima,kuma na tambayeta shin meyasa bata binneta acan ba?,setacemin ita mutum ce Wanda Allah yabawa arziki tana tsoron ranar da zaki waiwayeta ki tambayi Y'arki kinga batada hujjar gamsar dake cewa Y'arki ta rasu kar jama'a su d'auka nayi tsafi ko kud'i da'ita, to wannan dalilin ne yasata kawomana ita.
Kuka nake na jinjina hali irinna Hajiya,mutum ce mai amana kwarai da gaske,nima nan nafad'a musu abinda yasameni,Mama tace"...Uhm Fatima haka Allah yaso da rayuwarki ,inamiki fatan alkhairi a rayuwarki,kuma Hajiya ta tabbatar mana da cewa ita ta yafemiki duniya da lahira gashi Y'arki ta rasu a hannunta.
Taku a kullum Young Novelist.
Royal Blood Typing
Alk'alamin Auta
Advertisement
- In Serial40 Chapters
The Chronicle of the Ex-God of War Who's Given a Second Chance
Takazaki Ryu is one of a human who has successfully achieved the 4th tier, the so-called God Tier. To be specific, He's the first man to take the alias of Ares, the God of War.He also successfully reach the top of Babel tower, the core of all dungeons by going solo. This is all for him to take revenge for the death of his family, friends, and most importantly, lover.Although, when he's finally able to confront the one who's held responsible for the Dungeon creation, he simply gets played around and utterly destroyed without even able to land a hit on her.Prepared to die, his nemesis suddenly announced that she will give him a second chance before sending him back to when he's still 14 years old. What's actually her motivation behind those actions?
8 188 - In Serial10 Chapters
Twisted Creation – Wicked World
In the beginning there was pain; unending and unbelievable pain. Tough there were also happy memories mixed together with the pain. Memories of her only friend and caretaker happily laughing at her misery. When he stopped visiting her in her small dark room, she decided to search and explore the outside world, trusting that she will reunite with him again.This is the story of a twisted, wicked girl and her very first steps in a new world.
8 114 - In Serial38 Chapters
Deity's Fragments [Paused]
[participant in the Royal Road Writathon challenge] After a spatial distortion, the planet Earth awakens, causing changes in its surface and its living beings. This awakening allowed humans to gain powers and fight against the animals that evolved. But this was not the only thing humans would have to face. After the awakening, the earth opened up to the universe allowing humans to contact other races and dimensions. Zack is a boy who awakens his power and pursues his dream, even if that means destroying others' dreams.---------------------------------------------- Hi, this is my first novel; I'm using translation and grammatically to do this novel because my language is Spanish, so if you see any mistakes, please tell me. I am still gaining inspiration so that the update will be a bit slow. I would appreciate any support and suggestions on the novel! The image is not mine. It is free from copyright but credits to its author either way.
8 188 - In Serial6 Chapters
Heather Duke x Ram Sweeney!
Heather Duke and Ram Sweeney. A ship that would never happen but I like it :DThis is based on the film Heathers, made in 1989.There isn't anything dirty that goes on, although there are mentions of sex.TW for bulimia, eating disorders, abuse, etc.
8 153 - In Serial55 Chapters
Make It Right || kσσkv
Kim Taehyung has been a friend of Jeon Jia for quite some while now but had no idea she had an older brother. The older brother being twenty year old Jeon Jungkook. A boy who was kicked out when he was fourteen and 'forgotten' from the family tree. Until Jia and Taehyung's graduation when Jungkook comes home for the summer and stays longer than expected. - - - - - - - 06.20.21 - 12.24.21✔️TAEHYUNG X JUNGKOOKREAD FIRST CHAPT FOR MORE INFO ABOUT STORY ! © whoresome_rat
8 164 - In Serial26 Chapters
Guitar Cry: A Cody Simpson Love Story
He looks at her as his best friend.She looks at him as the boy that she is in love with.The world looks at them as Hollywood's youngest couple.
8 200

