《SHIN SO DAYA NE? (Complete)》CHAPTER THIRTY
Advertisement
💘SHIN SO DAYA NE?💝
TARE DA ALKALAMIN
📝
HAFSAT AL-MUSTAPHA
_Watpadd:Hafnancy_
_please manage diz chapter wlh am busy diz days_
🌼BABI NA TALATIN🌼
Page 140-145
"Agaskia 'yar Kareematu wannan Mubarak din ya kwanta min arai,na yaba da hankalinsa ba kadan ba,fatarmu dai Allah yasa yadda azahiri yake da halin kirkin nan yasa haka ma zuciyarsa mai k'yau ce...... "Cike da farin ciki nace"Amin Ummu Fadima,agaskia naji dadi sosai da kika yi na'am da Mubarak..... yanzu sauran mana Abba.... "Tace"Ga shawara idan zaki Karba.... Abbanku na dawowa ki tunkareshi da batun Mubarak din tun kafin lokaci ya k'ure miki...... "
Da sauri nace"No Umma am very scared....ban san ko taya Abba zai karbi zancen ba sabida yadda naga yake sona sosai tare da Haidar.... Ummu Fadima pls ki tayani yi masa magana yadda zai fahimta..... " girgiza kanta naga tayi tace"Not again babyna,har sai yaushe zan daina shige muku gaba ina tayaku fighting kan abubuwan daya shafi rayuwarku?har sai yaushe ne zan soma nannade hannuwa na zuba muku ido kuma na kyaleku ku kwaci 'yancin kanku? Ko baki san su kansu 'ya'ya suma suna da hakki akan iyayensu ba?" Ahankali nace"Eh! Suna dashi Umma
Ta cigaba"Good.... Toh ina son ki san cewar yadda mahaifinki keda hakki akanki haka zalika kema kina da hakki akansa.... yana daga cikin hakkin uba ya zabawa 'ya'yansa abokan rayuwa na gari,ku ya'yan zamanin nan ma ku godewa Allah yadda ake kyaleku kuke tsula tsiyarku son ranku,azamaninmu wallahi uba yake zabawa dansa ko 'yarsa abokin rayuwa don idan baki manta ba ni da mahaifinki ma auren hadi aka mana,amma azamanin nan sai kiga iyaye sun baiwa 'ya'yansu damar kawo duk wanda suke so sai ah aura musu zabinsu...... My daughter wat am trying to figure out to u is dat,karki sake kiyi wasa da wannan damar da mahaifinki ya baki na ki kawo zabinki,Mubarak kika ce kikeso kuma nima nayi na'am dashi,don haka Abbanki na dawowa ki tareshi da batunsa,ina son ki cire duk wani tsoro aranki,mahaifinki ne wanda ya tsugunna ya haifeki ba wani dodo ba,u don't hav to fear ur father at all... Ni kaina nasan yadda suka shaku da Alhaji Ahmad mahaifin Haidar,kuma nasan bazai so yaki baiwa dansa aurenki ba... Amma abinda nakeso ki gane shine,mahaifinki mai saukin kaine da kuma fahimta don haka nasan bazai miki dole ba,insha Allahu zaiyi na'am da zabinki idan har yayi bincike ya tabbatar da Lallai Mubarak nada halayen kirki.... Is dat taken 'yar Kareema?"
Cike da jin wani gwarin gwiwa nace"Insha Allah Umma na fahimceki kuma zan tuntubeshi da maganar Mubarak din da zarar ya dawo.... "
"'Yata kar kiyi tunanin kamar bana son tunkarensa da maganar ne da kaina,a'ah,bana son ne yaga kamar ni nake daure muku gindin yin abubuwa,for instance,zuwanku kano kwanakin baya ai nice na shigar da maganar wajensa tare da nemar muku izini,ko alokacin ma sai da yayi dan korafi akan meyasa bana kyaleku kuna tambayar abu agunsa sai dai kuta aikoni kamar wata 'yar aiki? Toh kinga abinda ya sanya nake son ke da kanki ki tunkareshi da maganar kenan,kuma ki hanzarta kada yazo ya bullo mana ta bayan gida..... "
"Umma wai meh kike nufi ne da bayan gidan nan da kullum kike fada? "Cike da rashin fahimta nayi mata wannan tambayar.
Murmushi tayi kafin tace"Ina nufin kada ya aurar dake ga wani can wanda ba zab'inki ba.... "
Da sauri na dafe kirji nace"A'zubillahi!!! Insha Allah hakan ma bazata faru ba,babu wanda zai min auran dole sai wanda nakeso ko ummata? "
Advertisement
"Ni wacece da zanki idan har wanda ya fini iko dake ya zartar da hukuncin hakan? "
"No Ummu Fadima kar ku min hakan don Allah" na fadi hakan ina girgiza kaina kamar wacce aka fada mata cewar ai tuni ya riga da ya zartar da hukuncin hakan.
***
**Washegari,5:45pm***
"Abba oyoyo! Abba oyoyo!! "
Abinda naji kannena nata fada suka dad'a nanatawa kenan wanda hakan ya bani tabbacin lallai mahaifin namu ya dawo kenan.
"Fadima! Suhaima!!.... Kuna ina? duk ku fito nan immediately...... "
Hakan naji Abba ya fadi wanda tuni zuciyata ta hau dukan chalugude.Toh meh kuma mukayi wa Abba?daga dawowarsa ko hutawa beyi ba sai kwalla mana k'ira cikin b'acin rai abinda bai taba yi ba? Innalillahi kar dai ace Lee ya fallasa asirin? Because da Dad dinsa Abba yayi wannan tafiyar,so definitely idan har ya gayawa dad din nasa toh babu yadda za'ayi Alhaji Ahmad yaki tadantawa da mahaifin namu akan zancen.... Wayyo! Idan kuwa haka ne Leedar ko kadan be k'yauta min ba..... Am juz in trouble because my dad don't accept such shits,yana matukar daukar zafi ga duk wanda yayi masa k'arya ko kuma yai masa wasa da hankali.
"Wai baku ji abinda na fada bane?Fadima! Suhaima!! ko kuwa so kuke ni na biyoku da kaina?...... "
Haka naji ya Kara maimaitawa wanda tuni jikina ya hau rawar mazari,banko kofar dakina naji anyi wanda saura kiris! gabana ya tsinke sabida faduwar gaba.Ajiyar zuciya na saukar ganin Suhaima ce not Abba as I thought.Itama jikinta naga yana shaking wanda yafi nawa kuma ga dukkan alamu ihun Abban ne ya tasota daga bacci.
"Yaya Fadima kinji yadda Abba ke kiranmu kuwa muryarsa cike da b'acin rai? Am scared Allah dai yasa Haidar ba tona mana asiri yayi ba...... " cike da rawar murya take wannan maganar wanda bana jin zan iya amsata ahalin yanzu.
Da k'yar dai na daure nace"Kije kada yaji shirun yayi yawa yace mun rainashi.... Yanzu na fito wanka,bari na hanzarta saka kaya na biyo sahunki,pls Suhaima hurry up kada ya biyomu da kansa kin san abin bazai mana k'yau ba..... "
Da sauri ta juya ta fice wanda har zuwa wannan lokacin jikin nata be bar shaking ba.Gaban sif dina na tsaya,na hau hargitsa kaya ina nemar simple gown da zan sanya,abin mamaki ko doguwar riga daya banci karo da ita ba,kun san haka abin yake idan mutum yana sauri sai kaki ganin wasu abubuwa da kake nema alokacin don hankali ba kwance yake ba.Yanke shawarar saka rigar dake rike ahannuna nayi wanda nayi tunanin skirt & blouse ce.To my outmost suprise ashe wata gown ce.Da gudu na zura wanda ban lura ba ashe baya na sanya agaba,gaba kuma abaya.Ban damu ba nayi saurin zura hijab akai na fice,hijab din mah be zauna daidai akaina ba,kan hijabin ya karkace gefe wanda ya sanya nayi looking like a baby,shima din I don't care,burina kawai naje amsa kiran mahaifina,mutum mai muhimmanci arayuwata.
Zuciyata ce ta tsananta faduwar gaba ah sa'ilin da idanuwana suka sauka kan fuskar Abba wanda b'acin rai ne k'arara ya bayyana saman fuskar.wani irin mugun kallo naga yana aika min dashi tun kan na karaso inda suke tsaye dashi da Umma,sai kuma Suhaima wacce take durkushe agabansu jikin nan nata sai aikin kyarma yake tayi.Umma ce naga ta umarci su Lubna da Su tafi dakinsu sannan ta juya tana duban Abba.
Tace"Wai Abba lafiya kuwa? dawowarka kenan daga doguwar tafiya ko hutawa baka yi ba ka hau kwallawa yara k'ira cikin b'acin rai? ai ko wani laifi dai suka maka yaci ace ka bari ka huta tukun before anything....don Allah ina rokanka ko menene pls ka sasauta zuciyarka kabi ahankali..... "
Advertisement
Inaaa! wanda yayi nisa baya jin kira,ga dukkan alamu karatun da Umma ta karanto masa ko daya be shiga kwakwalwar Abba ba don daga mata hannu yayi alamun ta meh shiru sannan ya juyo zuwa gareni yana nuna ni da 'yar yatsa.
"Fadima u betrayed d trust I have for u,na yadda dake fiye da tsammaninki ashe ke raina min hankali kike tayi babu wata batun soyayya tsakaninki da Haidar,all diz while yawo kuke ta mana da hankali....Toh ayau asirinku ya tonu,shi Haidar din da kansa ya sanarwa mahaifinsa ayayin da shi kuma mahaifin nashi ya sameni da maganar,I was so much surprised don har naso na k'aryata hakan akan cewa ni 'yata bazata taba min hakan ba sai kuma nayi tunanin Alhaji Ahmad babban mutum ne,toh meh zai amfana dashi idan yai min k'arya? Sai kuma nayi tunanin cewa 'ya'yan zamanin nan ka haifesu ne amma baka haifi halinsu ba.....yanzu so nake ki fada min tsakaninki da Allah da gaske din ne wai game kuke ta playing akan Suhaima? "
Gabana ne ya hau bugawa da sauri da sauri,kallona nakai ga Suhaima wacce naci sa'a itama ni din take kallo.
"Wai bake nake tambaya ba kin min shiru? Iyyeh?"
mukut!! kakeji na hadiyi wani miyau wanda har wani daci-daci nake jinsa ah mak'ogorona,da rawar murya nace"Eh.....ha..kane Ab..ba don Allah kayi hakuri...... "
Kallon Umma yayi ya kwashe labarin komai ya fada mata na soyayyar dake tsakanin Leedar da Suhaima da kuma shiga tsakaninsu da Rukky tayi har kawo nemar gafarar da suka zo nema da kuma bayyana mana gaskiyar al'amari da sukayi,sai dai banji yayi batun wata aljanu ba wanda hakan na nufin Leedar bai fada musu wannan ba kenan.
Umma kuwa sai tafa hannaye take tana fadin"Ikon Allah kenan!... "
Abba ya watsawa Suhaima wani mugun kallo kana yace"Ke kuma back to you.... Kin bani mamaki sosai da aka fada min cewar tun SS1 dinki kika soma soyayya abinda nayi muku hani dashi na kuma gindaya muku sharad'in har sai kun kammala secondary level dinku kafin ku soma tsayawa sauraren wani saurayi da sunan wata soyayya... Ke kuma kika take wannan umarnin nawa kika nuna min halinku ta 'ya'yan zamani kika bi son ranki... Koda yake ni naki be wani zafeni sosai ba kamar na 'yar'uwarki da suka raina mana hankali,suka maida mu kananan yara irinsu,suka maida mu sa'anninsu na wasa ta hanyar sakamu akwana sunata yawo mana da hankali son ransu abinda ni Sa'adu na tsana arayuwata kenan amai dani shashasha.... "
Maida kallonsa gareni yayi,da sauri na saddar da kai kasa ayayin da nake jin yadda zuciyata ke mugun dukan chalugude.
"Toh! ku bud'e kunnuwanku da k'yau ku saurari hukuncin da zan yanke koma nace hukuncin dana riga na yanke...... Yanzu ku saurari yadda tawa game din zata kasance....."
Da sauri na dago kai na kalleshi cike da fargabar jin kalaman da suka fito daga bakinsa.
Ya cigaba"Ke! Fadima atunaninki kinyi nasarar gyara k'yakk'yawar alak'ar dake tsakanin 'yar'uwarki da Haidar ko?.... Toh! Ina son ki san cewar su sunyi winning ayayin da ke kuma kinyi failing..... "
"Abba failing kuma? How? " Na fadi hakan cike da mamaki.
Murmushi naga ya saki wanda nake tunanin kila na takaici ne,kana yace"Yes! I repeat,Fadima Sa'ad kinyi failing.... Adalilin yawo da hankalina da kikayi shiyasa na yanke hukuncin ita Suhaimar zata auri Haidar din,ayayin da ke kuma na riga nayi miki miji don haka bazan bari ki auri zab'inki ba duk da cewar ban sani ba ko kina wanda kikeso or not wannan be dameni ba,amma ki sani nan da sati biyu za'a kawo gaisuwanku duka,gaisuwa da sadaki atake arana daya, ke infact! na tsayar da lokacin auranku nan da wata daya cur! babu ragi babu kuma k'ari................. "
Ihu na sanya iya k'arfina ina fadin"Wayyyo! Abbbbbbbbbbaaaaanaaa! don Allah kayi hakuri wannan hukuncin yayi min tsauri da yawa,wlh Abba na tuba bazan sake ba.. Allah Abba ina da wanda nakeso pls kada ka aura min wanda ko saninshi banyi ba,wlh bana sonsa gobe insha Allah zan turo maka Mubarak shi nakeso please......... " kuka nake sosai kamar raina zai fita ina zuba sambatun nan.Da sauri naja kaina zuwa inda Umma ke tsaye duk jinkinta ya mace da jin hukuncin da Abba ya yanke.
Kama kafafuwanta nayi nace"Mahifiyata please ki saka baki acikin wannan maganar don Allah ki roka min Abba daya taimaka ya min rangwame wlhy bazan sake raina masa hankali ba..... "
Kallon Abba Umma tayi,cike da tausayin yarta da take ji tace"Abbaa.......... "
Da sauri ya daga mata hannu"Karma kice komai,kinji nace wallahi don babu wanda ke bina bashi rantsuwa na riga na zartar da wannan hukuncin,idan kuwa har kika ga Fadima bata auri wannan yaron ba,toh sai idan har shi yace ya fasa auranta ko kuma idan bana raye.........sai dai kuma idan guduwa tayi wanda aranar da kuwa ta sanya kafafuwanta tabar gidan nan da sunan guduwar,toh ta sani aranar na cireta daga cikin list din 'ya'yana......"
Jin abinda ya fada ya sanya na sake sakin wata sabuwar shafin kukan ina rok'ansa,amma abin mamaki sai naga kawai ya kada kansa yayi waje wanda nake tunanin kila masallaci zashi don har an soma k'iraye-k'irayen sallar magrib.Suhaima mah kuka take sosai sai naji kamar na kwasheta da wawan mari don duk ta sanadiyyarta hakan ta faru,amma ai kuma bata aikeni taimaka matan ba.
Zaman 'yan bori nayi ak'asa tare da sanya hannu aka kamar mai shirin zaucewa,toh kila na zaucen ne ban sani ba.Wani tunani naji ya fad'o min arai,ai kuwa da azama na mik'e nayi dakina ina jin Umma na k'irana amma ko tankata banyi ba don sosai itama taban haushi da taki tabuk'a komai.Zaro wayata dake chargy nayi,da rawar hannu na nemo lambar Mubeen nayi dialing,cikin rashin sa'a akace min switched off.Ji nayi kamar na sanya hannu aka na kurma wawan ihu da zai iya fasa gidan da muke ciki.
Engr.Mahmood ne ya fad'o min arai,da sauri na binciko lambarsa,cikin sa'a kuwa naji k'iran ta shiga,can sai kuma naji tune din 'number busy' alamun ya yanke call din.Dama nasan ah rina,don so da yawa hakan yake min idan na kirashi sai kaga ya yanke call din sai shi ya k'ira,acewarsa baya son ya cinye min kati.
Dakatawa nayi ina jiran call dinsa,ai kuwa babu wani b'ata lokaci naga k'iran ya shigo.Da sauri na danna 'receive'.
Ina jinsa yace"Hello! my dear sister inlaw........ " kamar jira nake naji muryarsa na fashe da kuka.Kuka sosai nake mai daga hankali.
Cike da tashin hankali naji yace"innalillahi wa'inna ilaihi raji'un...mamana lafiya kike kuwa?meya faru?meh aka miki?... Pls stop crying & talk to me wallahi har cikin zuciyata nake jin kukan nan,Zahra dear please speak out..... "
Alokaci d'aya na sami kaina da yin yadda yace,wato tsayar da kukan.
Nace"Abba ne wai shi zai aurar dani ga wani ba Mubarak ba,kuma wai nan da sati biyu za'a kawo gaisuwata,sannan wata d'aya cur! ya tsaida lokacin bikin..... " fashewa da kuka na sakeyi nace"Sir! I don't know wat to do na rokeshi yace wallahi his decision is final,gashi inata trying layin Mubeen yaki shiga,pls brother help me out kasan duk yadda zakayi kuyi get intouch with each other ka fad'a masa abinda ke going yanzun nan................. "
"Miko min wayar nan........ " hakan naji an fad'a da k'arfin gaske wanda kiris! ya rage na kurma uban ihu don tsananin firgitar da nayi.Juyawa nayi da sauri ina kallon Abba daya shigo dakina,yanayinsa kamar wani Zakin da yaga abokin gabansa yana shirin kai masa farmaki.Beyi wata-wata ba ya iso inda nake ya warce wayar,ina ji ina gani Abba ya zare sim-cards dina,ya babballasu gutsi-gutsi kana ya watsar akasa.Hawaye sai bulbulowa suke asaman kumatuna amma na kasa furta komai agareshi don lamarin mahaifin nawa ya soma bani tsoro,ban taba tunanin Abba nada mugun zuciya haka ba,koda yake ance ka guji b'acin ran shiru-shirun mutum.
Nuno ni yayi da 'yar yatsa yana fadin"As from today,I have restricted ur movement,ba shiga ba fita,God's so kind mah kuna cikin hutu don haka baza kice zaki fita zuwa makaranta ba,in that case,idan har kika ga kin saka kafa kin fita cikin gidan nan toh sai ranar da zan sallameki ki tafi d'akin mijinki,idan har kuwa kika kuskura kika tsallake wannan umarnin nawa kika fita da gangan,toh karki kuskura ki dawo cikin gidan nan don daga ranar zan cireki ah list d'in 'ya'yana..... Kuma koda gangan karki kuskura ki ari wayar wani acikin gidan nan ki kira wani,ko Kuma wani yazo nemanki ki fita ki sameshi,wallahi kinji dai na fad'a miki bada yawuna ba......... "
Sai ayanzu na sami damar magana nace"Haba Abba! meh yayi zafi haka? meyasa kake nemar tarwatsa min zuciya ne?meyasa kake k'ok'arin jefa 'yarka cikin kogin damuwa ne? Why are trying to make things hard for me? Abba ka tuna fa Allah madaukakin sarki yace acikin al'qur'aninsa mai girma................. "
Da sauri naga ya daga min hannu yace"Malama dakata ba wa'azi nazo ki min ba,ina san ki sani,ni mahaifinki ne mai sonki Kuma bazan so na ganki cikin damuwa ko Kuma nayi k'ok'arin cutar dake ba,am juz trying to punish you for wat you did don abinda kuka mana rashin k'unya ce don be kamata ace kun saka iyaye acikin shirmeku ba wanda ko kadan banji dadin hakan ba don ni sam na tsani mara gaskiya da kuma kawo wasa cikin al'amari mai k'arfi... Ko kuwa kin manta sunana ne? 'Adalin alk'ali' ko Kuma ace'Alk'ali mai gaskiya ko mai nasara', don haka nakeson Kuma kuyi koyi dani ba wai kuyi koyi da shirme ba............ "
Yana kawo nan da jawabinsa naga ya juya ya fice daga d'akin.Hawayen idanuwana sun kafe sunki zuba,nabi karyayyun sim-cards dina dake watse akasa da kallo ina tunanin yadda za'ayi na sake ganawa da Mubeen d'ina kafin nan da sati biyun da za'a kawo so called gaisuwata,gaskia I really nid to speak to him don mu nemi mafitar wannan al'amarin,kai infact! ko guduwa ne sai muyi idan muka ga abin bana wasa bane,da sauri na soma istigfari ganin ina nemar b'ace hanya.
(gareku 'yan mata masu tunanin guduwa idan akayi kakorin lika musu wanda basa so,sam ba shawara ce mai k'yau ba Kuma alamace ta rashin ilimi,don idan da'ace mutum nada wadatacciyar ilimi toh bazai yi tunanin yin hakan ba,ku sani idan har kuka amince da wannan zabin tabbas kunyi biyayya Kuma zaku ga wannan auren tana iya yiwa wani alheri ne agareku duka.... Allah yasa mu dace).
Suhaima ce naga ta shigo dakin sum-sum kamar wata mara gaskia,yo! ai kusan kamar mara gaskiyar ce.Zata soma magana nace"Suhaima pls juz get out,allow me to be alone with my thoughts and sorrows.... Don Allah ki tafi kawai bazaki iya magance min komai ba.... Ina tayaki farin cikin samun masoyinki amatsayin mijin da zaki aura,Hak'ika burinku ya kusan cika,congrats..... " Araina nace"Ni Kuma meh zancewa kaina?Ina jajantawa kaina or wat? "
Da k'yar na iya jan kafafuwana zuwa bandaki don d'auro alwala.Ina nan kan sallaya har aka soma k'iraye-kirayen sallar isha'i,na tashi na sauketa sannan na d'ora da shafa'i da wutiri.Addu'o'i sosai na shiga zubawa babu gaggautawa ina yi ina hadawa da kuka cikin k'aramin sauti.Ina jin sanda aka shigo d'akina aka zauna saman gado,amma ko ajikina ban damu nace nabar kwararo addu'o'in da nake afili ba,illa k'ara bada himma da nayi.
Sai da nayi mai isata sannan na mike ina nannad'e sallaya,na juyo ina fuskantar Umma wacce itace ta shigo ta zauna tana jiran iddarwata.
"'Yata zo ki zauna muyi magana" Da sauri na isa gareta,instead na zauna kamar yadda ta umarta,a'ah sai kawai na fada jikinta tare da rushewa da kuka.
"Fadimaaaa!! "Kiran Sunana naji tayi wanda kusan zan iya cewa tunda nake da ita ban taba jin ta k'irawo ainihin sunana ba sai 'yar Kareematu (kun san fulani da kunyar dan fari).
Tsagaita kukan nawa nayi,na mike daga jikinta na zauna saman gado tare da ruk'o hannayenta,cike da tausayin kaina nace"Ummu Fadima ji hirar da mukayi jiya yana neman rikid'ewa ya zamo gaskia.....Ko dai Umma kin san da batun bada ni ga wani da Abba ke kokarin yi ne shiyasa kika yi min wannan hirar jiya?kawai fada min gaskiyar lamari ne kika kasa? "
Da sauri naga ta girgiza kanta tana fadin"A'ah 'yata ko kadan bani da masaniya akan wannan zance kuma har ga Allah ni ban ma san yaron ba haka kuma ban ban ko dan gidan wanene ba... Ke infact! nima sai yau din nan nake jin wannan kudirin na mahaifinku akanku duka.......... "
Advertisement
- In Serial38 Chapters
The Mansion in the Woods
In a world of mystery with dozens of races, known and unknown, the young Priestess Glissandi sets out into the world, acccepting her sacred task as a missionary. The young, intelligent woman is accompanied by the wise and careful Paladin Lissa, the young, experienced and reclusive Knight Trista and the two over-eager and talented Squires Mira and Mina as she sets forth on a grand adventure, only to quickly run into what seems to be a deep conspiracy, stretching back to one enigmatic person. Determined to bring him to Light and justice in the Lord's name, she ignores the warnings all around her and goes chasing after a being who everyone fears, but is she really prepared for the truths she will encounter on her journey? Sanguilia, Guide extraordinaire and strange woman all around, is accompanying a trade caravan when disaster strikes. At first glance she is no more than a Guide, which is no lowborn title itself, as it represents individuals who are capable of traversing the unknown wilds and are well versed in the languages of the land and its inhabitants. As she enters a city on her way home, a new, massive problem rears its head. Accompanied by a bar wench, who is far more than she seems, the mercenary Orc, Daenan and his tiny, flying companion, Faen, all with their own plans and agendas, they seek to tackle a monster in the shape of a man who controls the city. In the depths of the woods, far away from what humanity sees as the centre of civilisation, the lone, independent city of Lanas prepares itself for war, for the Kingdom of Maldora has set its eyes on them and their wealth. A cry for help goes out and bonds long faded into obscurity are renewed. And the world quakes when their calls are answered. Melena, once a slave girl, resides happily in the Mansion and is slowly getting used to her new life, where equality seems to rule. Until a noble's son decides that her very attractive body is something he should own. When the enigmatic master of the Mansion decides to personally deal with the rulebreaker, her world is turned upside down as she stumbles upon ancient mysteries that threaten to overwhelm her. Luckily she finds support in her once-liberator, now turned friend, the happy-go-lucky Evon, who carefully hides his past, the ghost-like Khrast, Kreya and many others. It is a tale of adventure, of lies and deceit, of love lost and found, of bravery and cowardice and where every one of our heroes and villains alike strive to find the answer to the same question: who is the being behind the Mansion of the Woods?
8 87 - In Serial46 Chapters
Smoke and Murders
Ilden grows colder with each passing year, as smoke and smog cool the city, but no one cares about that, it is just the way things are.Three people, a teacher, a company's heir and a low life, who should have never met become entangled in each other's lives, have no choice but to work together, for change various “way things are”.Alhough, it may not even matter, at this point.__________________This work may feature very strong language and potentially triggering content as mild as it may start. A simmering slow burn is my intentions with this so be forwarned. I would provide a warning in advance in the chapters themselves. Contains art work every chapter all done by me which includes the cover amoung other art pieces
8 116 - In Serial6 Chapters
Princess Aria and the Gem of immortality
This is the story of Brynhilde Von Aria who lost her parents at an early age and has lived on her own for a very long time. she one day finds out there is gem of power that can help here so sets out to find. along the way finds friends to help her in her search. the tale of princess Aria starts here.
8 109 - In Serial108 Chapters
Displacement
or, Deux Navires Passant dans la Nuit If you wake up in a new world, with only your memories of home to guide you, you have to trust the first people you meet. The first people Leah meets seem to know her - but not her. Leah is thrust into a fighter's role that does not quite suit her, and those who 'rescued' her do their best to help her fit in. They hint at a world that Leah can only vaguely understand without serious research and exploration, but how to do that research, when everyone believes her to be a local of this place, and too many questions might draw unwanted attention? And what about home? The more Leah learns about this world, the less she believes that she woke up on the right side of the bed - or more accurately, on the right side of the conflict. With magic being strictly regulated in her current "home," maybe it's time to uproot and look for a new set of allies... -- Displacement is a queer / lgbt bodyswap isekai: Leah Armande falls out of a Quebecois city into an unfamiliar fantasy world, and Leah Talesh falls out of her adventuring party's homeland and into an unfamiliar industrial world. The story follows both women as they navigate their new surroundings, trying at times to find a way home, at times just to pass for a local, and at times to actually make a life for themselves in their new world. Expect in-depth politics and worldbuilding, sapphic moments, foibles, and far too much time spent either in libraries or convalescing (or sometimes both).
8 199 - In Serial32 Chapters
Through Blood We Grow
Monsters come in many shapes. Men, animals, spirits, dreams, feelings. Sometimes it feels as if this world is a monster, simply waiting to devour you and all you hold dear. Grim knows this feeling better than most. Like many he was happy with his life, friends aplenty, a loving mother, a stable home, and a bright future. Like many that life was taken from him. But unlike many that wasn’t the end of him. He wasn’t devoured by the world, he was given a second chance and new name. With that name comes new people, new dangers, and a new outlook. This monster of a world wouldn’t consume him, he would grow. He would grow beyond the nightmares, beyond the weakness, and beyond his past. And the only way he can do that, is through blood.
8 204 - In Serial44 Chapters
The mafia vs the psychopath
when a dangerous mafia has to work with one of his father's friends daughter, he's old time best friend how would he survive the crazy psychopath. she's always angry when things doesn't go her way, she is smart but very stubborn. everyone is terrified of her and doesn't want her trouble except the most dangerous mafia there is. Jace Norman. She is seductive she is hot she is everyman's dream girl. How would the dangerous mafia cope with her trouble.
8 169

