《SHIN SO DAYA NE? (Complete)》PART 2:CHAPTER SEVEN
Advertisement
*💘
*INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION🖊*
*{ we give the reader's of ours the best out of the best's,, our inks are melodious And dropping a kinda light's to reader's}*
'''THE PEN OF LOVE 😘 HEART TORCHING ❤ TEARS OF SORROWS 😭 CURDLES 😊 GIGGLES 😁 AND MARRIAGE THINK 💑'''
*JUST GIVE US FOLLOW.....*✔
_*please kindly show me some love by voting & commenting to let me know dat u guys are really enjoying the novel*_
_"Allahumma la sahla illa ma ja'altahu sahla,wa anta taj alal hazna iza shi'ita sahla...... "_addu'ar da nake ta nanatawa kenan babu gaggautawa sabida wani irin radadi da naji xuciyata ke min.Ina addu'ar ina hadawa da dukan kofa,alokaci daya kuma ina meh rera kuka kamar raina ze fita.Xuciyata cike take da nadamar abinda ta aikata.
"Mahmood don Allah karka tuka mota da kanka acikin irin wannan halin daka fita,don Allah ka bari ni da kaina nazo na kaika asibiti,pls dear nah am really sorry forgive me...... "
Na sake rushewa da wani sabon kuka ina meh cike da jin haushin kaina na abinda na aikata.Ina jin sanda ya tada motarsa ya fice atsiyace daga gidan.
Shi kuwa Mal.Bello k'asa kunnuwa yayi yana sauraro don yaji kamar bugun k'ofar cikin gidan ake da k'arfin gaske kamar za'a ballata.Da hanxari yayi ciki yana fadin"Oh! ni Bello dan Abu wai meke faruwa ne? "
Koda Mal.Bello ya iso sae gani yayi an garkame k'ofar da k'aton kwado,windunan dama arurrufe suke ta ciki,kuma labulayen asauke suke,don haka duk wani kukan kuran da Fadima take ba'a jin komai.
Mal.Bello dai ya tabbatarwa kansa da lallai babu lafiya yau agidan,daga kawo sabuwar amarya kuma sae tashin hankali tun ba'a kwan ba?ina kuma uban gidan nashi zaya je acikin daren nan da har ya rufe wannan baiwar Allahn aciki sannan yayi ficewarsa cikin mota atsiyace kamar ze tashi sama? Toh kodai wani laifin ne ta masa da har ya kasa hak'uri har gari ya waye shine ya tafi kai k'ararta gidan iyayenta?
k'ara k'arfin girgiza k'ofar da tayi ne ya dawo dashi daga duniyar tunane-tunanen daya lula ciki.
Duk da cewar yasan ba wai jinsa zatayi ba,amma still ya daure yace"Hajiyata hak'uri fa zakiyi ya dawo ya bud'eki da kansa,addu'ata agareku shine Allah yayi muku tsari da shed'an,ya kauda fitina atsakaninku,sannan kuma ya baku zaman lafiya.... "
Ya juya ya koma bakin aikinsa yana d'an raye-rayen wakokinmu na gargajiya yana meh cike da al'ajabin wannan al'amarin.
Fadima meh kika aikata?kin kuwa san idan wani abin ya sameshi you will definitely be held responsible?meyasa ke bazaki rungumi kaddararki ba kamar yadda kowa keta baki shawarwari akan hakan?shi kansa idan kin lura dashi cike yake da nadamar hanyar daya bi ya sami auranki ba tare da saninki ba,amma duk da hakan ya yadda da kaddararsa,maganarsa gaskiyace dayace *'kenan wani baya tab'a auran matar wani,haka mah wata bata tab'a auran mijin wata se dai idan har Allah ya kaddara.
Toh ita wacece da har bazata rungumi kaddararta ba?wace 'ya macece mah da har zata ga *' bata ji sha'awar son ya kasance mijinta ba sabida haduwarsa da kuma iya tattalin mace?komansa ah ilimance yake yinsa,ji bi yadda yake ta ankarar da ita idan ta nemi k'auce hanya,kenan bayan ilimin boko,na arabi mah ya gama ratsashi?
Wani irin zazzafar soyayyarsa ce taji ya soma kai mata cafka acikin xuciyarta,da sauri ta kai hannu ta danne daidai saitin xuciyarta,ahankali tace"Mahmood wallahi na haqura ka dawo wallahi xan gaya maka cewar na haqura xan xauna dakai,zan fada maka cewar na soma jin sonka araina,kuma xan gaya maka cewar am also fully ready to face any problem coming soon frm both Mubarak & the rest of ur family members....... "
Advertisement
Wani kuka ne naji ya kufce min,ina yi ina cigaba da sambatuna,kaina naji yayi min wani irin girma,ga wani ciwon da yake min alamun kukan da nake ne ya haifar min da hakan.Sassauta kukan nayi don kada na janyowa kaina wani sabon ciwon don ban gama warkewa ba.Idan naji wani motsi awaje saurin mik'ewa nake na nufi Kofa wai azatona ko Mahmood ne ya dawo.
Ji nayi kamar na sanya k'iran Umma na fada mata halin da nake ciki amma kuma se naga dare ya lula,ayanxu haka duk inda take tana tare da Abba,kuma bazanso yasan halin da nake ciki ba,yanke shawarar k'iran Ash nayi wacce ko dan flashing bata min ba tunda suka koma. (Dayake aranar da za'a kaita Abbanta ya maida mata da wayarta tare da zuba mata sabbin layuka biyu aciki).
Bugun farko akace min switched off,ba tare da b'ata lokaci ba na latso dayar layinta wanda acikin wata k'aramar wayarta ta saka wannan layin,shima switched off aka ce min.Ji nayi kamar na aza hannuwana duka biyun aka na kurma uban ihu,can baya ada,rayuwata nake cike da jindadi da walwala,sam ban san wata rayuwar kunci da damuwa ba,amma shigowar Dr.Mubarak Nakowa da kuma Engr.Mahmood Nakowa ya kawo min canjin rayuwa,suka sauya min rayuwa xuwa zallar damuwa da kuma kuncin rayuwa.
***
Ita kuwa Ash tasan tabbas Fadima ta riga tasan Mahmood shine mijinta tun kafin mah su baro kanon,kawai tasan taki tada wata rigima ne acikin jama'a,tafi son sae sun keb'e,toh tasan muddin idan suka rage su biyu dole Fadimar zata nemeta awaya,dalilin daya sanya ta kashe wayoyinta gabaki daya kenan tunda suka dira Zaria.
Zuciyarta cike yake da damuwa da kuma tsananin son tasan halin da Fatin tata ke ciki.
Ahankali ta furta"Yah Allah ka sanyaya xuciyar Fateenah aduk halin da xata tsinci kanta,kasa ta haqura ta rungumi *'ya Allah na rokeka,ka wanzar da zaman lafiya tsakanin Fadima,mijinta da kuma danginsa....... "
Haka de ta cigaba da kwararo addu'o'i wa Fadimar tata,daga bisani ta shafa,dama nafila raka'a biyu tayi,sannan ta zauna tana zubawa Fadima addu'ar samun zaman lafiya da mijinta da kuma danginsa.Can ta mike tana duban agogon dake manne asaman bango,taga 10:35pm,zuciyarta ce ta soma ingizata akan ta latso Fadima,amma sae ta danne taki kunna wayar,tabi lafiyar gado ta kwanta,ba'a dau wani tsawon lokaci ba,wani nannauyar bacci yayi awon gaba da ita.
_
Subhanallah!!... wai ni babban mutum meya ji maka wannan raunin ne haka? Wallahi karka so kaga yadda ciwon yayi rami sosae.... " Dr.Jabir ne yayi wannan maganar sanda yake wanke wa Mahmood rauninsa da spirit.
"Kaga Jabir,idan har zaka wanke min abu toka maida hankali ka wanke bana son neman jin ba'asi,nace maka tsautsayi ce kawai ko kunnuwanka sun toshe ne? " yayi masa wannan tambayar cikin hargowa.
Kwantar da murya Dr.Jabir yayi yace"Allah ya huci xuciyarka abokina, ni damuwa nayi da wannan situation din naka amma tunda baka son tambaya,kayi haquri bazan sake ba.. "
Sae duk Mahmood yaji ba dadi,amma kuma kala bece masa ba har ya gama wankin,ya lik'a masa k'aton cotton wool awajen,sannan ya manna plaster asama don ya agaza ya rik'e wool din.
Yace"Allah sarki da'ace Dr.Mubarak nanan da shine ze k'arbi wannan aikin don nasan baze tab'a bari wani yayi in bashi ba.... "
Gaban Mahmood ne ya bada ras!! jin an ambaci sunan 'Mubarak'.
Axuciyarsa yace"Kode ze mah k'ara lalata abin? Kila mah ciwon ze dada caccakawa da kwalbar daga bisani ya aika dani barzau in har akan Fadima ne...... "
Advertisement
Azahiri kuma ignoring dinsa yayi,yace"Malam kana da damuwa wallahi ka cika hayaniya,pls nawa ne kudin aikinka? "
Dr.Jabir ya bushe da wani irin dariya yace"seriously yanzu sae na karbi kudi daga hannun babban mutum kamarka?haba idan nayi hakan ai na cika babban butulu mara tunani,kai dai jeka kawai fatana Allah ya baka lfy ya kuma kiyaye tsautsayin gaba.... "
*' sunan da Dr.Jabir ke kiransa dashi kenan,wai don Mahmood din akwai kirki sosae,tausayi,mutumci,iya mu'amala da mutane,da sauransu,shiyasa ya cancanci da ah kirashi da *' sae de ance dan'adam tara yake be cika goma ba,matsalar Mahmood daya,wato miskilin k'arshe ne na gidan gaba kuwa,sam baya wani cika son hayaniya,idan kaga ya zage yana hira,toh kuwa tabbas da Zeeynsa ce,gashi yanxu itama Fadima tana kokarin samin wannan matsayin na Zeey.gashi da shegen zurfin ciki,sam bashi da abokin shawara,kai tsaye yake aikata duk abinda ransa yaso,shiyasa acikin duka friends nashi mah babu wanda yasan ta yadda akai ya auri Fadima,su de kawai zancen auren ne suka ji daga bakinsa.
Murmushin jindadin xancen Dr.Jabir yayi,kana yace"Shikenan nagode Jabir,bari naje dare na k'ara lulawa,sae da safe.... "
Ya kwashi keys da kuma wayoyinsa daya xuba saman wani table,adaidai lokacin kuma Dr.Jabir ya mik'o masa wata 'yar farar leda.
Cike da rashin fahimta yace"And wat is in? "
"Maganin pain reliever ce ke aciki.... "
B'ata fuska yayi sosae yace"Amma kasan de tun ina karamina na tsani shan tablets ko? Shine don iskanci zaka wani xuba min aleda? Gaskia ka barshi bazan sha ba,tunda ka wanke raunin its okay kawai..... "
Babu yadda Dr.Jabir beyi da Mahmood ba,juyin duniya yaki karba don shi arayuwarsa ya tsani ace yasha magani,gara-gara na gargajiya yana iya sha,amma na bature sam baya sonta,haka mah idan baya da lafiya ya gwammace ayi masa allura da ace masa yasha magani.
Sallama yayi wa Dr.Jabir ya fice,shi kuma ya rakashi da"Ace wa amarya muna nan xuwa mu kwashi girki.... "
Ai! tuni ya b'ace masa amma ya tabbata yaji abinda ya fada.
Murmusawa yayi yace"Kai Mahmood wallahi wani irin bahagon mutum ne meh dan wuyar sha'ani,idan baka xauna ka fahimci rayuwarsa ba,kana iya zaton ko sam baya ganin darajar dan'adam,amma abin ba haka yake ba,he's juz too simple but difficult to understand..... "
✨✨✨✨
Wata k'awar mominsu Mahmood wacce take zaune unguwa d'aya dasu Baba Mu'azzam ce ta k'ira ita Momin awaya take kala mata xancen auren Mahmood wanda shi Baba Mu'azzamun ne ya shige masa gaba.
Wata irin zabura ce Momi tayi kamar wacce aka manna mata shocking tare da dafe k'irji da k'arfi,tace"Dakata Rabi..... wannan wacce, irin xancen banza ce kike min haka?taya za'ai Mahmooda nah yayi aure ba tare da sanina ba?taya mah za'ai Mu'azzam ya shige masa gaba ba tare da nemar izinina ba?"
Haj.Rabi tace"Haba Binta meh zan tsinta acikin k'arya face zubda girma,daraja da kuma mutunci?kin tuna da wannan kawar tawa Haj.Nera?"
"Eh eh na ganeta...... " momi ta fada tana meh daga kai da sauri-sauri kamar Haj.Rabin na gabanta ne.
"Toh ai k'awar haj. Fa'iza matar Mu'azzamun ce,aminai ne sosae,kuma komai na haj.Fa'iza ita Haj.Nera ta sani,toh ita Neran ce tazo har gidana take fada min donni ban mah sani ba,wai daga wurin walimar auran take wanda akai acikin gidan Alh.Mu'azzam,toh anan take kala min gashi-gashi,wlh da farko na k'aryata xancen akan cewa babu ta yadda za'ai ah b'oye miki xancen auran,rantse-rantsen da take tayi ne ya sanya na yadda da ita don Haj.Nera idan har kaga ta kuke da rantse-rantse toh kuwa xancen gaskiyace take gaya maka,shine nace bara na k'iraki na d'an fesa miki zancen,amma don Allah karkice ah bakina kika ji............. "
Da hanxari Momi ta tari numfashinta"Dalla can rufemin baki anan,munafukai kawai masu bacci da ido daya,ana ruwan sama suna k'irgawa,'yan adawa da kuma hana ruwa gudu,wato yadda kuke ganin d'ana ke samun cigaba arayuwarsa shine kuke bakin ciki,kuke masa hadassa da k'yashi,soyayyar dake tsakanina da dana shine kuke bakin ciki,kuke kokarin so ku shiga tsakaninmu,toh kuwa da sakel,Haj.Rabi kin shayar dani madaran mamaki,da har kika shiga sahun masu mini hassada..... "
Cike da mamaki haj.Rabi tace"Haba Binta wannan wacce irin maganace kike haka?taya zan shiga tsakaninki da danki?taya zan masa hassada kan cigaban da yake ta samu arayuwarsa? Nifa na gaya miki babu abinda zan tsinta acikin k'arya face zubda girma da daraja,idan har baki yadda ba toh kiyi bincike,Haj.Fa'iza tace zasuyi kusan sati uku agidansa nanan kanon kafin su koma Zaria inda yake aiki,ita kuma take karatunta,don haka kije kiyi bincike da kanki,amma don Allah idan har kika ga zancena ya tabbata gaskia,na hadaki da Allah karkice ah bakina kika ji...... "
Bata jira taji ta cewarta ba tayi saurin datse call din cike da jin haushin zazzafar kalaman da Haj.Binta ta jefeta dasu.
Haj.Rabi kenan akwai shegen gulmace-gulmace nakin karawa kuwa,sae da Haj.Nera ta rok'eta akan tayi shiru da bakinta,har ta dau mata alqawarin cewar babu wanda ze ji zancen,har da ce mata ah inda ta gaya mata toh anan wurin zata watsar da batun.Taso din tabar wa cikinta zancen,amma dayake meh hali baya fasa halinsa,zancen har tsingulinta yake tayi shiyasa ta yanke shawarar fesawa Haj.Binta.
Haj.Binta kuwa jiki ah sab'ule ta koma da baya ta zauna agefen gado,alokaci d'aya ta rasa abinda ke mata dadi acikin duniyarta.Taya mah za'ai Mahmood yaje kai tsaye yayi auransa ba tare da saninta ba? Taya kuma za'ai Baba Mu'azzam ya shige masa gaba ba tare da an nemi izini daga gareta amatsayin mahaifiyarsa meh kuma iko akansa ba? Idan kuwa zancen Haj.Rabi ya kasance gaskia,tabbas zataso jin dalilin b'oye mata zancen auran kafin ta dauki duk wani mataki daga baya.Taso latso Mahmood din taji daga bakinsa amma kuma tafi son taje masa abazata ta gano gaskiyar lamari da ganta.
Da rawar hannu ta lalub'o wayarta ta latso babbar d'iyarta Maryam (Meema).Ta kora mata zancen nasu da Haj.Rabi.
Dama duk acikin 'ya'yanta Meema tafisu sanyi da kuma kauda kai kan abubuwan da basu taka k'ara sun k'arya ba.
Cikin sanyinta tace"Hajiyata nasan idan mah hakan ta kasance gaskia,toh tabbas Yah Mahmo bazai tab'a rasa dalilin b'oye miki ba,don Allah hajiyata ki masa uzuri ki kuma fahimci dalilinsa if dat happened to be true..... "
"Ke dallah rufe min baki marasa tunani kawai,ai duk daga ke har shi din halinku daya,matacciyar xuciya gareku sam bakwa da kawa zucina kamar yadda nake dashi akanku,har ke kin isa kice kada na dauki mataki idan har hakan ta kasance gaskiya? Toh! sannu Haj.Hafsatu uwata.... "
"Haba! Hajiyata ki baiwa zancen nawa k'yakk'yawar fahimta..... "
Da sauri tace"Saurara min nan kafin inci ubanki,gobe k'arfe bakwai ta muku anan gidan sannan mu dunguma xuwa gidan nasa muje mu ganowa idanuwan namu,kuma kada wata ta sake acikinku ta k'irashi ko baba Mu'azzam din har se munje mun ganowa idanuwanmu,kina jina ko? "
"Ehh! naji bayananki duka.... "
Bata sake wata magana ba ta katse call din,kai tsaye ta latso autarta Khairat ta kora mata zancen itama.
Dama Khairat sam bata haquri kamar zawo take,duk acikinsu tafisu d'aukar Zafi da abu sosae.
Cewa tayi"Kan babban burauba,Momi shine baki soma ci mana ubanta awaya ba kafin ku had'e?Fisabilillahi Momi taya za'ai Yah Mahmo yayi aure ba tare da saninmu ba har Babansu Zali ya shige masa gaba duk bamu sani ba? Kawai so ake ashiga tsakaninmu dashi,karki damu gobe kafin bakwai mah na iso gidan sae muje mu binciko kamar yadda tace,amma idan har zancenta ya kasance k'arya ne toh wlh Momi har gida zamuje muci mata mutunci....."
Cike da farin cikin zancen 'yar tata tace"Nagode 'yata nasan ke da Labeebah ne kawai zaku iya goyar min baya..... "
Haka ta k'ira Labeebah,itama din kamar Khairat din tayi,ta lailayowa wani uban ashar ta gundumawa Haj.Rabi,tare da tabbatarwa Momin da cewar itama din kafin bakwai tana family house.
Sae kai komo kawai momi ke tayi adakin baccinta,kallon agogo tayi taga 10:45pm,ji tayi kamar ta sanya hannu ta tura sandar agogon xuwa karfe bakwai na safe............. 📝
A/N
Ghen!Ghen!!Ghen!!!.... Nakowa's family fire on the mountain in a bit🔥🔥🔥
Can't wait.
*wait! Karku ce min har kun manta da batunsu mal.Gaddafi? Jinns din Rukky Lema?
*Ina labarin daren Farkon *Suhaileedar?*
*Ina labarin Mubeen mijin Hauwa'u Jiddoh?
step-by-step zamu bisu,ku dai ku cigaba da kasancewa dani.
*
,
Advertisement
- In Serial31 Chapters
Skill Overdose
Set in a modern world, Liam Keene, a person who had witnessed his parents killed, changed the way of living his life entirety when he decided to take revenge on the people who murdered his parents while also discovering another dark part of society as he tries to realize where his 'system' came from. _______ ___ __ _ Longer Synopsis: Witnessing his parents being killed in front of him, Liam unknowingly changed the way he thought about the world, while still having the thought of making the killers pay for what they had done to completely messed up his life. But time still passes as well as the emotions and beliefs that one had felt before... Unless something happened that made them want to remember that tragic moment. Exactly 5 years later after that day, Liam suddenly saw a window floating in front of him. A system. The one thing he thought that could change his life. Oddly enough, several minutes after that, his friend came to him with men from a dangerous organization on his trail. And later, he learned that this organization was the same one that ordered people to kill his parents. "Starting today until the day you die. We will be chasing you and we will try to kill you with our own hands whatever it takes." Just like the man said to him, since that day, as he kept walking forwards, he would just go deeper and deeper into the filth and danger of the world his living in. His once-peaceful life became a chaotic mess that he would have to fix with nothing but his blood and sweat. And the system. _______ ___ __ _ C-Come join the autho-... L-Liam to his journey to make the story... uh... his life good... or uh... better? _______ ___ __ _ (Note: Chapters are currently in an editing process. Expect that some parts of the story written in the unedited chapters have variation from what the author originally imagined.) Disclaimer: I do not own the cover art of this novel and I'll take it down as soon as the original creator says so.
8 180 - In Serial24 Chapters
Kate Emerson: Reborn-A LitRPG Apocalypse Adventure
Kate Emerson paralyzed veteran and former war fighter is recruited to take on a new mission, to protect the mining interests of Vision Dynamics. As a mega- international corporation they have the Nano-technology to help her walk again, and once more find her role as the soldier she always wanted to be. Her Nano-effective inlays and War Frame will make her, bigger, stronger and faster than she ever dreamed of being, and being reunited with her oldest friend, Rooker, seems like a Dream come true.But The City of Ur isn't even on the world she expected, the enemy isn't clearly defined, and for some reason there is a voice in her head that's doing its best to help her level up if she is going to survive this strange new world.
8 155 - In Serial44 Chapters
Letting go...
insight on the things left unseen.
8 109 - In Serial6 Chapters
I'm not supposed to love you
Even though he was scared to admit it, Texas was scared of his soulmate mark. He was scared of who's would match. He was scared it would be someone he is not supposed to love. When he finds out California is his soulmate what can he do, he is not supposed to love him. Based off of Ben Brainards Statehouse and The Table sieries. I don't own the Charactures just the plot. Ben please don't read this.
8 99 - In Serial75 Chapters
(TinCan) I Hate U.
Tin - you hate me? For what's the reason? Can stopped walking and turned to him. So confused as to why he sounded so broken all of a sudden.Can - why are you asking such stupid questions?Tin - you're being unfair. I told you my reason why I hate you, you should tell me yours.Can - we're enemies.Tin- enemies? (Turned to Can) tell me... tell me why do I feel this pain whenever you says something like that? (Punched his heart) it hurts... a lot right here. (Punched his heart a couple more as he started to weep.) Can...Can, why?Author's note:Hello everyone! I'm new to this and my grammer is suck big time but I am a fan of these lovely bl romance so I am writing a story of my own. Read if you like and also please support me! It would really help encourage me. Hehe!
8 126 - In Serial28 Chapters
SUMMER CAMP || NAMJIN✔️
"I'm not gay." "Neither am I. Now let's fuck." One night at summer camp will change these two males lives forever...;Ranked #2 in #kimnamjoon Ranked #3 under #joonRanked #7 under #namjinCOVER BY @yoonienetflix
8 130

