《ƘADDARAR RAYUWA》Page 3
Advertisement
*QADDARAR RAYUWA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
Haske writers association💡
Zaynab bawa
Follow on
Page 3
Haka rayuwa taci gabada tafiya har hafsa tagama junior secoundry school dinta, amma daga nan sai karatun ya qaqare yatsaya saboda dama can yau ajene gobe ba'ajeba,
Tana gama junior kuwa sai abun ya gagara daga nan sai aka ajiye karatun agefe, saboda rashin kudinda za'a dauki d'awainiyar karatun,
Dake yarinyace mai fahimta ta fahimci halinda suke ciki hakan yasa bata wani d'aga hankalintaba, dama da dad'e da sanyawa cikin ranta cewa wata rana dole zata bar karatunnan kodan qannenta suma su samu suyi nasu karatun."
Haka aka ajiye rayuwar karatunta agefe aka cigaba da fuskantar yanda rayuwa take zuwa."
Kamar kullum haka baba hamisu yake fita arana yayi tallah yayi buga-buga yasamo musu abunda zasu rufawa kansu asiri aranar,
Ayau kam abun yaci tura baba hamisu ya zagaya amma babu wani ciniki gashi rana tadukeshi har wani jiri-jiri yake gani badon yasoba yasamu waje haka yazauna domin hutawa yahuta tsawon minti talatin sannan yatashi yunwa yakeji sosai amma gani yakeyi bazai iya cire kudi yasiya abu yaciba saboda yasan halinda yabar iyalinsa aciki da ikon Allah cikin wasu awanni aka samu ciniki agwalumarda yake turawa abaro duka yaqare godiya yayga ubangiji yazauna yadan huta daga nan saiya dauki hanyar kasuwa yasiya musu abun buqata daganan saiya wuce gida,
Yana zama wata y'ar gindin bishiya yazauna bai dade da zama ba baccin gajiya yadaukeshi, yashari kusan 40minute yana bacci wanda ba hakan yasoba, yaso yahuta na kaman 20minute ne yakama hanyar gida saboda yabar yara da yunwa, salati yayi yamiqe ganin lokaci yadanja agurguje yayi alwala yashiga masallaci ya gabatarda sallan la'asar, ya iddar yafito yakama hanyar kasuwa, domin aunan abinci, sanda yaje shago yagama lissafi abubuwanda za'a kawo masa sannan ya sanya hannu zai dauki kud'i amma wayam kudin yace d'aukeni ahankali babu komai cikin aljihunsa, wani irin baqin ciki da tuquqin takaicine yakamashi ga dukkan alamu yana bacci aka lalume aljihunsa,
Advertisement
Hakuri yabawa mai shagon sannan yajuya yaja baronsa wani tuquqi yakeji cikin ransa lallai ya tabbata wannan duniya cike takeda rashin imani, amma idanba rashin imaniba ko kallonsa a ido kayi zaka fahimci irin talauci da wahala dayake ciki, yanayin kayan jikinsama kawai zai nuna maka irin talauci dayake ciki amma rashin imani har yakaiga anyi masa sata,
Yana tafiya yana tunani sam hankalinsa baya kan hanya sai jinsa yayi yafada cikin kwalbati dake bakin titi,
Subhanallhi kawai kakeji mutanen wajan suka dau salati, gabaki daya suka yiyo kansa taimaka masa sukayi yafito aciki yad'an kururje sanna kuma ya bugu,
Haka suka taimaka masa ya'isa zuwa famfo ya wanke jikinsa, godiya yayi musu sannan yakama hanyar gida amma rad'ad'in zuciyarsa dayakeji yafi masa na jikinsa,
Koda ya'isa qofar gida yadauki lokaci kafin ya'iya takawa ya qarasa cikin gidan da sallama,
Zama yayi can gefe mama wacce take kitchen jin shigowarsa yasanya tataso tafito ganinsa cikin wani yanayin yasa hankalinta yatashi, qarasowa tayi tana fadin baban hafsa lpy kuwa??
Kallonta yayi cikin damuwa amma yakasa furta komai, durqusawa tayi agabansa cikin nuna kulawa tafara fadin dan Allah baban hafsa kafadamin mai yake faruwa zan shiga wani halin idan kayi shiru haka,
Fitowar hindatu yasanyashi juyawa yana dubanta alokacin yaji wani hawaye ya zubo a fuskarsa, runtse ido yayi ya fidda huci sannan yadubi mama yace" ummi ban samo komaiba" ban dawo manada komaiba ummii" bansan yaya zanyi da way'annan yaranba bansan mai zan basu suciba,
Zaunawa tayi gefensa cikin yanayin kwantarda hankali tace kada ka tada hankalinka, Allah bazai hanamu abunda zamuciba,
Kada ka d'aga hankalinka kana iya qoqarinka wajan ganin ka biya mana buqatarmu, wuni zubur kakeyi cikin rana dan ganin ka nemo mana abunda zamu sanya abakinmu, iya tsawon rayuwarka jin dadinka da komai da sadaukar akanmune,
Na rana daya dan baga samuba bazamuji zafin kaba, Allah yaga zuciyarka ya aiko manada abunda zamu rufawa kanmu asiri
Advertisement
Yanzu hakama babu yunwa ajikinmu, fitarka keda wuya yaya zakari ya aiko manada shinkafa takai tiya goma, cikin amfamin gonarsa harda gero tiya uku,
Sanyi yaji sosai aransa jin cewa iyalansa sun samu abunda suka sanya acikinsu, hamdala ya dingayi yana godewa Allah sannan kuma yana godewa yaya zakari,
Miqewa tayi tadauko masa ruwa cikin kofi tamiqa masa sannan tawuce zuwa kitchen ta dauko kwanan abincinsa ta ajiye agabansa,
Sai alokacin ta lurada kayan jikinsa yanda ya kurkurje amma dayake yafara cin abinci yasanya bata tambayeshiba sanda yagama,
Tambayarshi tayi maiya faru nan yake shaida mata akan kudin cinikinsa aka kwashe yana tafiya yana tunani kuma sai yafada cikn kwalbati,
Sosai ta tausawa masa, sannan taci gabada yimasa magana akan yadaina sanya damuwa cikin ransa shi kadai dayake kallon kansa shine kawai yarage musu madogara idan kuma wani abun yasameshi wani hali yake tunanin zasu shiga?
Yanzuma haka yana raye kenan balle bbu ransa,
Tashi tayi tahada masa ruwan wanka mai zafin gaske yashiga ya duma jikinsa,
Kafin yafito tadauki kayanda yacire ta zuba cikin ruwa tafara gogawa amma kuma bbu omo dan haka tadauki kanwa tazuba cikin ruwan ta wankesu iya yanda zata iya fiddasu tashanya,
Duk wannan abunda yake faruwa sawwma tana tsaye bakin labule tana jinsu, hawaye ke zuba a idanuwanta wani irin tausayin kansune yake tsurga mata, suna cikin wani irin hali wanda yakamata dole atausaya musu,
Suna cikin halin qangin rayuwa, QADDARAR RAYUWA ta afka musu, a iya saninta tasan mahaifinta iya qoqarinsa yanayi wajan ganin ya biya buqatarsu amma abun yafi qarfinsa,
Zama tayi tana tunane-tunane tana tausayawa rayuwarsu, batasan sanda kuka ya kwace mataba hafsa tanada qarancin shekaru amma kuma tanada tunani mai zurfi, tanada hankalin gaske batada hayaniya, Allah ya sanya mata son mahaifanta da tausayinsu sosai cikin ranta,
Tana zaune ahaka har jikinta yayi sanyi bata samu tafita ko sannuda zuwa tayiwa mahaifintaba.
Shikuwa baba yana fitowa awanka ya canja kaya yafito dubansa mama tayi tana fadin ina kuma zakaje?
Zanje yiwa yaya zakari godiya!
Miqewa tayi tace kadan bari mana kahuta akira sallar magriba idan kayi zuwa isha'i saika tafi,
Baiqi tataba saboda yasan tafadi hakanne dan tanason yahuta,
Komawa yayi yanemi waje yazauna yajira har aka kira magrib aikuwa yadan samu hutu dan shima yadanji dadin jikinsa,
Alola yayi sannan yafice masallaci,
Sai alokacin sawwama tafito ad'aki, dake duhu yadan shiga yasanya mahaifiyarta bata fahimci yanda tayi kuka jikin tayi sanyi sosaiba.
Cikin gida suka zauna, suka jira dawowar mahaifinsu,
Sanda yadawo suka dan ta6a hira sannan yaran suk shiga suka kwanta itama mama suga shiga,
Kafinsu kwanta take tambayarsa cewa gobe tanason zuwa gida tagaida mahaifanta,
Amsa mata yayi da fadin Allah yakaimu goben da rai da lpy,
Zuwa yamma ko magriba saina biyo miki mudawo saboda nima na kwana biyu banje na gaidasuba,
Allah yakaimu suka fadi sannan sukayi addu'a suka kwanta bacci."
Itakuwa sawwama tadad'e batayi bacciba tana saqe-saqe cikin ranta ta yanda zata 6ullowa lamarin,
Abu dayane yakeyi mata kaikawo cikinta ranta wanda hakan kawai take ganin shine mata mafita, domin wanann lamarinsu idanba sun tashi sun nemi mafitaba rayuwarsu tana cikin hadari sosai,
Hakan tasanyawa ranta shiyasa take ganin daren yayi mata tsawo, Allah-Allah takeyi gari yawaye tagama ayyukanta tatafi aiwatarda abunda yake cikin ranta,
Da wannan tunanin bacci yayi awon gaba da ita."
To be continued
Zaynab Alabura
✔️ote
Comment
share
Follow
💞
Advertisement
- In Serial9 Chapters
Another Day, Another Quest
Lifetimes ago, a young woman named Vin was summoned from another world to defeat a Demon Lord and the Great Calamity that birthed him. After successfully saving that world by subduing the Demon Lord, she lived out her life there as a celebrated Hero. At her death, the Pantheon, a collection of all of the patron deities of all the many worlds, offered her a place among them. She accepted and thus, she created her own world to watch and protect, and named it Xael. Xael, a world of magic and swords, flourished for centuries, but now... Now, there are signs of a Great Calamity approaching, much like the one that caused her to be pulled her away from her father and sisters so many years before. Unwilling to see her world fall, Goddess Yvinne decides to do the one thing that she can to save her creation, and even herself. Summon a Hero from another world. However, the Summoning did not work quite correctly, and the "Hero" she got? Well...let's just say he's not exactly what she hoped for. This is a story of a nobody becoming somebody, and a goddess remembering what it was like to be a human.
8 194 - In Serial14 Chapters
SHAKKA, a Goblina's Pet Werewolf
Bought off the market by a bubbly goblina, a young werewolf launches into an epic quest to save monsterkind from a mysterious order’s genocidal plans. [participant in the Royal Road Writathon challenge]
8 261 - In Serial16 Chapters
The Godborn Chronicles (dropped)
More than a century has passed, since the Anabasis occurred, bringing with it the recurrence of magic, the return of the figures of myth, and the significant upheaval of the political, geographical, natural state of the world. Now, another change seeks to be known...Meanwhile, Juan Xavier Lee is just your not-so average, non-magical human hunter, who suddenly finds himself, caught up in a plot that is way beyond his league.
8 108 - In Serial170 Chapters
Slime Girl
Slimes are stupid!Annoying little pests that don't think about anything.How would they? They don't even have a brain.They don't even think about what they do, dissolving anything in their reach.That's worse than a beast acting on instinct, that's just following a program.A plague of mindless balls of goo.If it were up to me they should all get eradicated.At least that’s what I thought.Until my life was turned into a mess. Stupid slimes!
8 644 - In Serial33 Chapters
Color Me Crázy [Completed]
Zimmoni is a beautiful young girl who always finds trouble, or more like trouble always finds her. One night she runs into the worst kind of trouble named Kaere also known as Lonelle ( Lonnie as well). Zimmoni is brave, but was she being too brave? Although trouble always finds her she is a very kind hearted person, who was taught how to respect her elders and have manners.Kaere (Lonelle aka Lonnie) is ruthless & reckless. He is feared by almost everyone in the hood and state's. Even people out of state's. Basically you could say he's somewhat a drug lord. Kaere, like his name doesn't really match his personality. When it comes to his son, he is another person. What happens when Kaere & Zimmoni cross pathway's? Is it going to be beautiful or nasty and horrid? Is he going to ruin her? Is she going to ruin him? Are they going to balance each other out or does fate have a different thing for them?⚠Warning: There is mental abuse and a lot of confrontations. Zimmoni's not the one to be playing with, but then again neither is Kaere
8 206 - In Serial41 Chapters
Fixing Each Other
They both have broken pasts that used to shine with the love they felt, now though now it is different the only thing they feel is pain, sadness, and the torment of lost love. Bridget the only existing female alpha haunted by the ghosts of her past tries to move on from the death of her mate all hope she had to restore the love she had lost had been shoved down deep inside her buried with the fragments of her broken heart. Her continuing fling with her Beta leaves him screaming with jealousy when Jerome Morton transfers to their pack only to discover Bridget is his second chance at love and he hers.Jerome Morton. He had been betrayed by the two people who were supposed to love him like no other; his mate and his brother. Three years he watched them fall deeper and deeper in love with each other whilst he was feeling the pain of his mate's rejection. He finally gives up hope of winning back her heart when they announce they are expecting.So when Bridget meets Jerome and the sparks fly both of them are thrown into confusion whilst figuring out how to defeat a new breed of hunters together and along the way feelings are developed between the two broken souls.Will these two push aside their egos and let themselves be happy or will their pasts prove to difficult to DISCLAIMER: THIS STORY IS UNEDITED!
8 171

