《ƘADDARAR RAYUWA》Page 3
Advertisement
*QADDARAR RAYUWA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
Haske writers association💡
Zaynab bawa
Follow on
Page 3
Haka rayuwa taci gabada tafiya har hafsa tagama junior secoundry school dinta, amma daga nan sai karatun ya qaqare yatsaya saboda dama can yau ajene gobe ba'ajeba,
Tana gama junior kuwa sai abun ya gagara daga nan sai aka ajiye karatun agefe, saboda rashin kudinda za'a dauki d'awainiyar karatun,
Dake yarinyace mai fahimta ta fahimci halinda suke ciki hakan yasa bata wani d'aga hankalintaba, dama da dad'e da sanyawa cikin ranta cewa wata rana dole zata bar karatunnan kodan qannenta suma su samu suyi nasu karatun."
Haka aka ajiye rayuwar karatunta agefe aka cigaba da fuskantar yanda rayuwa take zuwa."
Kamar kullum haka baba hamisu yake fita arana yayi tallah yayi buga-buga yasamo musu abunda zasu rufawa kansu asiri aranar,
Ayau kam abun yaci tura baba hamisu ya zagaya amma babu wani ciniki gashi rana tadukeshi har wani jiri-jiri yake gani badon yasoba yasamu waje haka yazauna domin hutawa yahuta tsawon minti talatin sannan yatashi yunwa yakeji sosai amma gani yakeyi bazai iya cire kudi yasiya abu yaciba saboda yasan halinda yabar iyalinsa aciki da ikon Allah cikin wasu awanni aka samu ciniki agwalumarda yake turawa abaro duka yaqare godiya yayga ubangiji yazauna yadan huta daga nan saiya dauki hanyar kasuwa yasiya musu abun buqata daganan saiya wuce gida,
Yana zama wata y'ar gindin bishiya yazauna bai dade da zama ba baccin gajiya yadaukeshi, yashari kusan 40minute yana bacci wanda ba hakan yasoba, yaso yahuta na kaman 20minute ne yakama hanyar gida saboda yabar yara da yunwa, salati yayi yamiqe ganin lokaci yadanja agurguje yayi alwala yashiga masallaci ya gabatarda sallan la'asar, ya iddar yafito yakama hanyar kasuwa, domin aunan abinci, sanda yaje shago yagama lissafi abubuwanda za'a kawo masa sannan ya sanya hannu zai dauki kud'i amma wayam kudin yace d'aukeni ahankali babu komai cikin aljihunsa, wani irin baqin ciki da tuquqin takaicine yakamashi ga dukkan alamu yana bacci aka lalume aljihunsa,
Advertisement
Hakuri yabawa mai shagon sannan yajuya yaja baronsa wani tuquqi yakeji cikin ransa lallai ya tabbata wannan duniya cike takeda rashin imani, amma idanba rashin imaniba ko kallonsa a ido kayi zaka fahimci irin talauci da wahala dayake ciki, yanayin kayan jikinsama kawai zai nuna maka irin talauci dayake ciki amma rashin imani har yakaiga anyi masa sata,
Yana tafiya yana tunani sam hankalinsa baya kan hanya sai jinsa yayi yafada cikin kwalbati dake bakin titi,
Subhanallhi kawai kakeji mutanen wajan suka dau salati, gabaki daya suka yiyo kansa taimaka masa sukayi yafito aciki yad'an kururje sanna kuma ya bugu,
Haka suka taimaka masa ya'isa zuwa famfo ya wanke jikinsa, godiya yayi musu sannan yakama hanyar gida amma rad'ad'in zuciyarsa dayakeji yafi masa na jikinsa,
Koda ya'isa qofar gida yadauki lokaci kafin ya'iya takawa ya qarasa cikin gidan da sallama,
Zama yayi can gefe mama wacce take kitchen jin shigowarsa yasanya tataso tafito ganinsa cikin wani yanayin yasa hankalinta yatashi, qarasowa tayi tana fadin baban hafsa lpy kuwa??
Kallonta yayi cikin damuwa amma yakasa furta komai, durqusawa tayi agabansa cikin nuna kulawa tafara fadin dan Allah baban hafsa kafadamin mai yake faruwa zan shiga wani halin idan kayi shiru haka,
Fitowar hindatu yasanyashi juyawa yana dubanta alokacin yaji wani hawaye ya zubo a fuskarsa, runtse ido yayi ya fidda huci sannan yadubi mama yace" ummi ban samo komaiba" ban dawo manada komaiba ummii" bansan yaya zanyi da way'annan yaranba bansan mai zan basu suciba,
Zaunawa tayi gefensa cikin yanayin kwantarda hankali tace kada ka tada hankalinka, Allah bazai hanamu abunda zamuciba,
Kada ka d'aga hankalinka kana iya qoqarinka wajan ganin ka biya mana buqatarmu, wuni zubur kakeyi cikin rana dan ganin ka nemo mana abunda zamu sanya abakinmu, iya tsawon rayuwarka jin dadinka da komai da sadaukar akanmune,
Na rana daya dan baga samuba bazamuji zafin kaba, Allah yaga zuciyarka ya aiko manada abunda zamu rufawa kanmu asiri
Advertisement
Yanzu hakama babu yunwa ajikinmu, fitarka keda wuya yaya zakari ya aiko manada shinkafa takai tiya goma, cikin amfamin gonarsa harda gero tiya uku,
Sanyi yaji sosai aransa jin cewa iyalansa sun samu abunda suka sanya acikinsu, hamdala ya dingayi yana godewa Allah sannan kuma yana godewa yaya zakari,
Miqewa tayi tadauko masa ruwa cikin kofi tamiqa masa sannan tawuce zuwa kitchen ta dauko kwanan abincinsa ta ajiye agabansa,
Sai alokacin ta lurada kayan jikinsa yanda ya kurkurje amma dayake yafara cin abinci yasanya bata tambayeshiba sanda yagama,
Tambayarshi tayi maiya faru nan yake shaida mata akan kudin cinikinsa aka kwashe yana tafiya yana tunani kuma sai yafada cikn kwalbati,
Sosai ta tausawa masa, sannan taci gabada yimasa magana akan yadaina sanya damuwa cikin ransa shi kadai dayake kallon kansa shine kawai yarage musu madogara idan kuma wani abun yasameshi wani hali yake tunanin zasu shiga?
Yanzuma haka yana raye kenan balle bbu ransa,
Tashi tayi tahada masa ruwan wanka mai zafin gaske yashiga ya duma jikinsa,
Kafin yafito tadauki kayanda yacire ta zuba cikin ruwa tafara gogawa amma kuma bbu omo dan haka tadauki kanwa tazuba cikin ruwan ta wankesu iya yanda zata iya fiddasu tashanya,
Duk wannan abunda yake faruwa sawwma tana tsaye bakin labule tana jinsu, hawaye ke zuba a idanuwanta wani irin tausayin kansune yake tsurga mata, suna cikin wani irin hali wanda yakamata dole atausaya musu,
Suna cikin halin qangin rayuwa, QADDARAR RAYUWA ta afka musu, a iya saninta tasan mahaifinta iya qoqarinsa yanayi wajan ganin ya biya buqatarsu amma abun yafi qarfinsa,
Zama tayi tana tunane-tunane tana tausayawa rayuwarsu, batasan sanda kuka ya kwace mataba hafsa tanada qarancin shekaru amma kuma tanada tunani mai zurfi, tanada hankalin gaske batada hayaniya, Allah ya sanya mata son mahaifanta da tausayinsu sosai cikin ranta,
Tana zaune ahaka har jikinta yayi sanyi bata samu tafita ko sannuda zuwa tayiwa mahaifintaba.
Shikuwa baba yana fitowa awanka ya canja kaya yafito dubansa mama tayi tana fadin ina kuma zakaje?
Zanje yiwa yaya zakari godiya!
Miqewa tayi tace kadan bari mana kahuta akira sallar magriba idan kayi zuwa isha'i saika tafi,
Baiqi tataba saboda yasan tafadi hakanne dan tanason yahuta,
Komawa yayi yanemi waje yazauna yajira har aka kira magrib aikuwa yadan samu hutu dan shima yadanji dadin jikinsa,
Alola yayi sannan yafice masallaci,
Sai alokacin sawwama tafito ad'aki, dake duhu yadan shiga yasanya mahaifiyarta bata fahimci yanda tayi kuka jikin tayi sanyi sosaiba.
Cikin gida suka zauna, suka jira dawowar mahaifinsu,
Sanda yadawo suka dan ta6a hira sannan yaran suk shiga suka kwanta itama mama suga shiga,
Kafinsu kwanta take tambayarsa cewa gobe tanason zuwa gida tagaida mahaifanta,
Amsa mata yayi da fadin Allah yakaimu goben da rai da lpy,
Zuwa yamma ko magriba saina biyo miki mudawo saboda nima na kwana biyu banje na gaidasuba,
Allah yakaimu suka fadi sannan sukayi addu'a suka kwanta bacci."
Itakuwa sawwama tadad'e batayi bacciba tana saqe-saqe cikin ranta ta yanda zata 6ullowa lamarin,
Abu dayane yakeyi mata kaikawo cikinta ranta wanda hakan kawai take ganin shine mata mafita, domin wanann lamarinsu idanba sun tashi sun nemi mafitaba rayuwarsu tana cikin hadari sosai,
Hakan tasanyawa ranta shiyasa take ganin daren yayi mata tsawo, Allah-Allah takeyi gari yawaye tagama ayyukanta tatafi aiwatarda abunda yake cikin ranta,
Da wannan tunanin bacci yayi awon gaba da ita."
To be continued
Zaynab Alabura
✔️ote
Comment
share
Follow
💞
Advertisement
- In Serial16 Chapters
A world with two moons
Ever been in love? well I know I weren't at first except... I met them 1 by 1 with different circumstance's and situations. I did not even know that we were meant to be together. hell I did not know it was still possible for me to learn what is love. and to actually fall in love. with all the crazy things that happened I though that I would forget all about love and such. but I was wrong. at the end of things it came to me. not just one, not two. but A lot of them came to me, chased me and showed me how much they love and cared for me.It all started when I met her, she was my very first love. she was my everything and now she is part of my everything. I lost her then I found her again this time I shall not let her go and so the others that love and cared for me.I really am glad that I manage to came to this planet. I have a harem*cough* I never knew life could be so wonderful if we just have to live it fully and enjoy it while we can.----------------------------------------------------------------------------------------------------------------------------------------------WARNING- this FF will contain Mature content as I update this,* Sexual *Gore *Foul language's---------------------------------------------------------------------------------------------------------------------------------------------(I warned you guys, now enjoy yourself and have fun reading my FF)
8 177 - In Serial27 Chapters
The Grey Realm, an Erebus Story.
Written by: Staugroan and The Inklets. Edited by: Claudia Adams. In the beginning there was a god, who watched over and made one world his own. Soon after the god grew restless, but happened to stumble on a small world filled with life. This world was named Erebus by its peoples; humanity. The god was so fascinated with this new world that he started to copy it back home, creating oceans, forests, deserts, and so forth. Then the god created life and eventually his favored creations who would be immortals and be the better of mankind in every way-the elves. So often the god had traveled to Erebus that the two worlds became linked by magic and their inhabitants could cross at will. Relations between the races flourished, and a great empire was born in the Grey Realm, home of the elves. But the god once again grew restless, and set loose great beasts that stood at the top of any food chain, the apex. At first the elves met the challenge and fought them head on. But mankind was not so lucky, they died in droves to push back even a single apex. Something had to be done. Elves and man worked together to begin sealing off the worlds to protect mankind, to limit the ways in and out to better fight the apex off and keep their fellows safe. The ritual had adverse effects the likes of which neither the elves nor man could predict; the sealing of the worlds started slow, but the magic had never been done before, and in their ignorance it spread to completely cut the two worlds off from one another. It ejected the apex, and other magical being back into the Grey Realm, saving Erebus. At first the elves were content, they would find a way back once the apex were dead and gone. But the seal had done more than keep Erebus locked away. The powersource of the seal was magic itself, from both worlds, and it consumed it all greedily. The elves, weakened without their magic, crumbled into ruin, and the apex were free to hunt the other races of the Grey Realm. Two-thousand years later a strange phenomena is occurring and magic is slowly returning to the Grey Realm, and tears open that allow passage to Erebus. Thu'lain and a few elves must make the journey to fallen kingdom of the elves Anosora, in the hopes of reclaiming what was once theirs. They must face their nemesis the apex, and survive not only the species that have turned against them, but a terrible being left behind by the god to kill even the apex. Uch'l'thein, the faceless terror.
8 202 - In Serial32 Chapters
Claim Me Alpha(Editing)
When I walked into the school people look at me. I was walking to my locker and I smelled the sweetest smell ever. Mate!!! Go get mate's Reign was yelling and howling.Looking around, my eye a landed on the one person who I didn't want to see and he was staring right back at me.Cole Black.His eyes looked through mine and Reign was howling with joy.I stood there shocked not able to move.Except when he stood up and started walking towards me, I did the one thing that I would have never thought I'd do.I ran.Just as I got into the parking lot and to my car, warm arms wrapped around my arm and I knew exactly who it was.Cole turned me around to where I was facing him and growled" Mine""No, no, no, not yours!!!" I said in disbelief.His grip tightened around my waist and he growled. "You are mine. No one else's. You will not touch another male and you will not talk to another male. You are mine. Mate." He said before putting his head in the crook of my neck and inhaling.
8 239 - In Serial61 Chapters
Terror Explored (a terror infinity fanfic)
Josh and Lance were just simple high school students before finding themselves thrown into a realm of eternal horror and danger. Now the two of them have to work with the veterans of the realm and the other newbies to create a team that can survive and defeat God's realm. A fanfic inspired by Terror Infinity.
8 228 - In Serial7 Chapters
Pictures of You
Tiva One-Shots//Each update is a separate Tiva quick fic. They'll probably mostly be based on OTP story prompts.
8 180 - In Serial15 Chapters
قومارباز Jikook
jikook
8 138

