《ƘADDARAR RAYUWA》Page 4
Advertisement
QADDARAR RAYUWA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
Haske writers association💡
Zaynab bawa
Follow on
Page 4
Da asuba babansu da kansa yatashesu suyi sallah,
harda qananun yaran kowa sanda yatashi babansu yajasu sallah suka gabatar, addu'oi yaketa yimusu kala-kala akan Allah yakawo musu dauki cikin lamarinsu dakuma kariya cikin rayuwarsu, byan sun idarda salla sauran kuma suka koma d'aki itakuma tafito tafara share-share na gida da wanke-wanke da sauran ayyuka kafin mahaifiyarta tafito tagama komai halima tana tayata suka hade cikin gidansu tass,
Dama daii sukam ba daga nanba sunada talauci kam gashi gidannasu na talakawane kurmus amma sunada tsabtar gaske komai masu ataltale yake,
Duk rashin kyawu na gidan amma idan suka shareshi suka taltaleshi saiya baka sha'awa."
Mamansu tafito lokacin suna surfa gero wanda zasuyi kunun karyawa,
Sannu tayi musu suka gaidata sanna sukaci gabada aiki, kicin tawuce sun shareshi tass-tass sun daura ruwan zafi akan wuta,
Suna gama surfawa suka bushe suka wanke,
Barshi sukayi yadan bushe sannan suka dakeshi cikin qanqanin lokaci suka gama,
Aka dama kunu mamansu tabasu naira ashirun suka siyo sugar,
Dalam-dalam haka sugan tayiwa kunun amma ahakan sukasha domin rabonsu da samun karyawa mai kyau kamar hakama an d'an dauki lokaci,
Sai dai idan babansu yasamu ciniki mai kyau sannan ya siya musu koko da qosai na karyawa."
Da wuri mama tagama shirinta tsaff na fita anguwa da hindatu kawai tafita tabar sauran agida sanda taja kunnen sawwama akan takulada qannenta,
Sannan ta jaddada mata akan kada tabarsu da yunwa dukda tasan cewa bazata barsunba amma taqara tunasarda ita, akan ta dafa musu shinkafa,
Tana fita kuwa kamar jira sawwma takeyi tashiga dakinda babansu yake ajiye baronsa yadauko baqar leda,
Shinkafa ta gwada tiya biyu tafice, domin aiwatarda nufinta da takwana dashi cikin ranta,
Shago tatafi can ta aunar sannan ta auno mudun waken suya da duk wani abunda zata buqata tadawo gida,
Gyara waken tayi takai markad'e ta tace tadaura, wasu dan lokuta kadan tahad'e awaranta, tazauan ta soya, miyar jajjage tayi ta zuba akai ta juye a bokiti tafita,
Advertisement
Aqofar gida tazauna dake gidansu bakin titine hanyar wucewar jama'ane, kuma akwai shaguna agefen titin,
Lokaci kadan tadauka tafara ciniki, lokacinda baifi awa biyuna gefen gidansu akwai almajirai, haka sukayita siya mai goma mai biyar tana zaune anan harta siyar aqofar gida bata motsa ko'inaba,
Batayi zaton qarewarsa dawurina amma ganin yaqare yasanya,
Bata zaunaba takoma kasuwa ta auni wanda yafi nada yawa,
Abinci tafara daurawa qannenta domin gargadin mahaifiyarta tadace kada tabarsu da yunwa,
Dake tanada zafin nama wajan aiki, lokaci qalilan tadauka tagamawa qannenta abinci, sannan tafara aikin awara, har yamma taci mata bata gamaba,
Tunani tafaryi tasan har indai tayi tazuba cikin bokiti irinna datsu ba lallai tayi ciniki ba saboda yamma tayi, wata dabarace tafado mata dan haka tahad'a murhu aqofar gida tafara suya,
Abundai alhmdllh sai dai ace sam barka tafara ciniki dake wajen akwai karancin masu abun siyarwa, kuma akwai yawan shagunaan sana'a, har magrib ta risketa awajan tana suya tana cinikinta.
Dake baba shima yafita dawuri bai san mai yake faruwaba,
Yafice zuwa gidansu daga nan yabiwa mama yagaida nata mahaifan, sannan suka kamo hanya,
Ana kiran magriba mama da baba suka doso layinsu daga nesa suka hangi sawwama zaune bakin murhu da yara akanta suna jira azuba musu,
Ganinta haka mamaki ya kamasu babu wanda ya'iya magana acikinsu suka shige ciki,
Ita kama batama luradasuba kanta yayi zafi wajan saida awara,
Sanda taga anfito a sallah sannan tatura yaro yakira mata halima zata dawo yin sallah,
Halima tafito ta kar6eta, ita kuma tatashi tanugi gida da sallama tashiga gida kanta tsaye batareda wani tunaninba,
Aqofar d'aki ta samesu alamun sun idda sallah, gabantane yafadi ganinsu sun dawo dan batayi zatoba, ad'arare ta qarasa kusa dasu tana fad'in mama, baba sannunku da dawowa,
Sannu baba ya amsa, mama kuwa batama kulataba dauke kanta tayi daga kallonta, sawwama tana kallon yanayin mama jikinta yayi sanyi sosai, babane ya katseta da fadin je kiyi sallah kidawo zamuyi magana,
Miqewa tayi har tana tuntu6e ta dauki buta tashiga bayi tayi tsarki tafito tayi alwala ta gabatar da sallah,
Advertisement
Koda tadawo agefe tazauna cikin nutsuwa tace" baba gani"
Kallonta yayi cikin nutsuwa yace" mamana me nake gani?
Mamana tallan kika koma yi?
Mamana bakiga illar wannan tallar bane?"
Mamana talla tayiwa rayuwarki illa amma baki fahimci hakanba, mamana kinason qara jefa kanki cikin wani halinne?
Ko shawarata kona mahaifiyarki baki nemana lokacinda zaki fara wannan abun,
Mamana idan abunda nake kawo muku yagazane zan qara qoqari,
Nasan hakuri kawai kukeyi da duk wani abunda nake kawo muku,
Zan qara qoqari inakawo muku fiyeda na baya,
Mama wacce tunda baba yafara magana batayi maganaba sai yanzu tace"
Aiso take ta nuna cewa iyayenta sun gaza sun kasa daukar d'awainiyarta bari tafita itada kanta ta nema,
Mama taqarasa maganar cikin zafin raii,
Girgiza kai sawwama tahauyi hawaye na zuba a idanuwanta,
Cikin muryar kuka ta zakud'a kusada mahaifanta tafara fad'in,
Baba dan Allah kuyi hakuri wallhy ba nufinaba kenan,
Baba kokadan ban raina abunda kake kawo manaba,
Baba a kullum tausayinkane cikin raina jiya ban iya runtsawaba saboda tunanin halinda jiya kadawo aciki,
Baba banyi haka dan 6acin rankaba nayi hakane dan taimakonka,
Juyawa tayi wajan mama tace mama dan Allah ku yafemin,
tana fadin haka taqara sanya kuka bata ta6a tunanin cewa mahaifanta zasu dauki zancen hakaba da bata faraba, dan babu abunda taqi jini irin 6acin ransu,
Kukanda takene yasanya duka jikinsu yayi sanyi koda bata fadiba sun san halinta sun san halin d'iyarsu sunsan sawwama bazata ta6a yin haka danta nuna cewa mahaifanta sun qaza ba, tayi hakanne kawai danta taimaka musu, amma dole su nuna 6acin ransu saboda ta fahimci halinda takeson jefa kanta aciki,
Da halinda tafad'a abaya, sannan su sanya mata tsoron wanda zai faru nan gaba,
Jikinsu yayi sanyi sosai suka gaza magana
Ido kawai suka tsira mata tana kukanta babanta yarasa mai zai furta shidai yana tsoron yaqara barinta talla akaro na biyu,
Dakyar ya'iya daurewa yafara fadin naji na fahimceki mamana, ina gudun qara faruwar abunda yafaru abayane, saboda kowani mahaifi zaiso kare d'iyarsa kada wani abun yasameta, ni nagaza akaro na farko banso nakara bari wani abun yasameki, tunda kinga ni nakasa kareki kiyi haquri ki taimakeni wannan karon na kare rayuwarki,
Zuciyata bazata iya juran wani abun yaqara samunkiba."
Girgiza kai kawai sawwama takeyi,
saida tadan tsagaita kukan sannan tafara fadin mama baba kuyi hakuri dan Allah ku yafeni bazan sakeba,
Tausayintane yaqara kamasu,
Har cikin zuciyar mama take tausayin diyarta kuma tana sonta sosai akullum takalli d'iyarta ta tuna abunda yafaru da'ita takanji tausayinta da soyayyar diyarta cikin ranta,
Shikenan yawuce Allah yayi miki albarka, amin ta amsa da dishasshiyar muryarta."
Suna zaune awajan sukaji kiran sallar isha'i hakan yayi dai-dai da shigowar halima,
Ta miqawa sawwama kudin cinikin da tayi tawuce domin yin alwala,
Daukan kudin sawwma tayi tamiqawa mahaifinta batareda tace komaiba tamiqe tana mai qara basu hakuri tashiga d'aki ta gabatarda sallar isha'i sannan tazauna tunani,
Abunda yafaru abaya yake tariyo mata tabbas tasan cewa dole hankalin mahaifanta yatashi sosai duk da cewa har yanzu bawani shekaru garetaba amma zuwa yanzu tafara gane illar da rayuwarta take ciki,
Abunda yafaru abaya ne yake tariyo mata lallai ta tabbata wannan mutumi ko wanene shi babu d'igon imani cikin zuciyarsa, idan akayi la'akari da shekarunta a wancan lokacin,
Nisawa tayi afili ta furta kalmar Allah ya'isa wanda tun lokacin data fahimci illar yayi mata take furtawa,
Akullum yafad'o mata sai tayi masa Allah ya'isa,
Kuma tanada yaqinin ako'ina yake wata rana Allah zai amsa addu'arta yayi mata sakayya akan abunda yayi mata,
Ta tabbata idan Allah yatashi kamashi sakayyarda zaiyi masa sai yafi wanda yayi mata munin gaske,
Hawaye taji yana zuba akan kumatunta ta share afili taqara furta ya Allah kamar yanda ya sanyani da mahaifana kuka,
Ya Allah ka sakamun,
Jingunuwa tayi da bango haka har bacci yadauketa azaune,
Sai da kannenta suka shigo sannan suka tasheta tagyara kwanciyarta takwanta saboda gajiya nan da nan bacci yaqara dauketa."
Asuba tagari
Lockdown🔐
To be continued
Zaynab Alabura
✔️ote
Comment
Share
Follow
💞💕
Advertisement
- In Serial69 Chapters
Afterlife Quest: Theodore Saga
This is Afterlife Quest: Theodore Saga. Book 1 is chapter 1-27 and Book 2 continues the story. Book 1: The Denial of Theodore Theodore is a young man taken from this world too soon. He is in the first stage of grief over his own death, but he is fighting this truth as much as he is fighting the monsters that populate his current plane of existence. Where is he exactly? Why is he here? Will he gain the required skills and grow strong enough to stay "alive"? Book 2: The Stain of Guilt Theodore continues his journey after many triumphs and foibles. He is dealing with the guilt of leaving his beloved behind after the choice he made. This is a LitRPG set in the afterlife. Follow Theodore as he adventures in the great beyond.
8 126 - In Serial18 Chapters
The Torch
Tanaka Manyika was a Zimbabwean form 4 student in his 2nd term of study, and like every other kid his age, he wanted to pass his end of year exams and move on with his life. However on one particular night his parents and his sister were brutally murdered by two strange men. This was only the beginning to a horrific nightmare; the coming of the apocalypse of infinite darkness was upon him. In that despondent world where everyone in the dark is subjected to despicable mutilation by the creatures of the unknown, Tanaka only has a torch as his arsenal, the only tangible form of light in a world consumed by darkness. Can he survive the end of the world and be the haven of others in despair or will he eventually fall prey to the hopelessness of the world?
8 177 - In Serial29 Chapters
Twenty Fifty-Six
"I can't let fear get in the way. I know that I am a strong person, and I will do this."It is the year 2056, and Canada is a different country. Every odd year, the government requires each of the thirteen provinces and territories to send in a fourteen year old boy, and the next year, on the even year, a fifteen year old girl is required. What becomes of these teens, no one knows. But Amber Matlock is determined to find out. Even if it means becoming one of the teens owned by the government, and crushing her mother. Amber will do anything to find out.cover made by @hayleymonroe
8 117 - In Serial40 Chapters
Heretic Immortal
If the world has no feelings and is cruel, then why do you accept it the way it is? If power, is what you need, then take it. If enemies are in your way, remove them. If a monster you have to be, then just become one.
8 62 - In Serial17 Chapters
random Dave and Bambi incorrect quotes and other stuff (I guess) (+12)
Mostly incorrect quotes lmao. I don't even know if I'm going to do other stuff.
8 67 - In Serial32 Chapters
New Life [Itachi x Reader]
[Completed]She had a feeling that something big was going to happen.To both of them.Disclaimer : I do not own Naruto.Was #1 in itachixreader and #2 in uchihaitachi🖤
8 476

