《ƘADDARAR RAYUWA》Q page 13
Advertisement
*بسم الله الرحمن الرحيم*
Haske writers association💡
Writing by
Zaynab bawa
Follow on
Page 13
Gabaki d'aya sadam yadauke qafarasa daga wajan sawwama yadaina zuwa wajanta yadaina nemanta, ya yanke duk alqarsa da ita, duk wani hanya da zata iya sadashi da ganinta yakan gujewa faruwar hakan dama tun can sai yaje yake ganinta kokuma yabi hanyarda take sana'arta, qarfi da yaji ya cirewa kansa tunaninta ya rage tunaninta sosai koda tunanin yazo masa yakanyi qoqarin yakicewa,
Harkokin gabansa kawai yakeyi amma wani lokacin yakan tunata sa'i-sa'i,
Qoqaarinsa kawai ya fisge ya cireta acikin ransa,
Dukda yayi nasara ta wani fannin amma ta wani fannin yakasa,
Yarage tunaninta sosai amma kuma bawai yabari gabaki d'aya bane wani lokacin haka yakanyi tunaninta,
Afad'insa yace tunda batason alaqarsu shida ita batason ya ra6eta batason duk wani abunda zai hadasu shikennan yarabu da ita yabarta tayi farin ciki saboda yaga zuwansa wajanta yana sanyata cikin damuwa,
Bazai qara takura mataba kamar yanda take nunawa adik lokacinda yaje wajanta,
Hakan yasa kawai ya saka harkokin karatunsa agaba dama gashi test sukeyi hakan yaqara dauke hankalinsa daga gareta nasa wajan kenan."
————-
Sawwama kuwa anata wajan ta zuba idanuwa amma shiru yake babu shi babu alamunsa,
Akullum idan halima tafita wajan sana'ar sawwama taringa leqawa kenan koda zata ganshi, amma shiru,
Lokuta dayawa takan tambayi halima, halima ta shaida mata baizoba,
Ranarda ta qara tambayarta halima tadubeta tana fadin wai nikam sawwama wayeshi kullum kike tambayar wajansa?
Akwai wata alaqa tsakaninku ne,
Girgiza kai sawwama tayi tafara kame-kame tarasa amsarda zata bawa halima,
Sai can wani abu ya fado mata cikin ranta tayi saurin fadin A'a kawai yana bina bashine,
Inaso idan yazo nabashi kudin sane shiyasa nake tambaya,
Jijjiga kai halima tayi tace auu akan wannan nema, ai idan kudin sane zanbashi duk ranarda yazo idan kuma bai zoba Allah yabaki lafiya kici gabada sana'arki saiki bashi da kanki,
nunfashi mai dumi kawai sawwama ta furzar batareda tace komaiba, bata qara tadawa halima zancensaba bata qara tambayarta akansaba amman koda yaushe tana cikin tunaninsa ahaka harta warke tafara fita wajan sana'arta,
Ga dukkan alamu sawwama abun yafi zafi ta wajanta dan kuwa ita bata ko qoqarin mantawa dashi, akullum qara tunaninsa takeyi, bata bar tunaninsaba saboda data zauna zata hau aikin tunani, dan anata ganin it ace ta 6ata mata rai,
Sau dayawa mama takanyi mata magana akan yawan zaman tunanin,
Amma abun ya faskara hakan yasa mama take tunanun ko abunda yafaru da ita abayane yake damunta shine yake sanyata yawan tunani,
Advertisement
Idan tana tunanin mama takan fara kwantar matada hankali, kuma itama mama takan shiga damuwa hakan yasa yanzu take 6oye damuwarta gaban mahaifiyarta, lokuta da dama sai tashiga d'akine abun yafi damunta saboda acikin gida koyaya tazauna bazata rasa mai d'ebe mata kewaba,
Lokuta da dama sawwama takan zauna tayita neman dalilin wannan tunanin nasa datakeyi amma takasa,
Sawwama qaramar yarinyace mai rauni da sanyin hali rayuwarta tafi yawa ita kad'ai bawasu qawaye garetaba balle ace tafad'a musu damuwarta su bata ainihin amsar abunda yake damuntaba,
Ba kuma zata iya fadawa maman taba,
Haka tayita riqe abun acikin ranta
Amma mikin rashin ganin sadam yananan cikin ranta,
A kullum zuba ido takeyi da ganinsa , sanya rai takeyi da sake ganinsa amma kuma ko mai kamanninsa bata qara ganiba."
————
Sadam yadawo wani irin mutum mai zafin rai ko qannensa lokuta dayawa abu ba abuba sai yhausu da masifa,
Balle najeeb da suke wuni zubur tare akan abu qarami yake sauke zafin ransa,
Najeeb kuwa yanzu tun yana fushi da sabon halin sadam harya hakura yadaina,
Idan yayi masa wani abun kawai sai dai ya maida wasa kokuma ya share wani lokacin ya maida masa idanna maidawane,
Saudayawa sai bayan sadam yayi abun daga baya sai yazo yaga rashin dacewar abunda yayi,
Mummy kuwa anata wajan koda yana yiwa qannensa masifa bata cewa komai karshema saita hau kansu da fad'a tana fadin aii laifinsune saboda ita har indai sadam zaiyi karatu toh bata ta6a barin wani abun ya takurashi,
Kaffa-kaffa takeyi dashi tana lalla6ashi har indai yana karatu,
Hakan yasa suma qannesaa dasuka lura suka daina shiga sabgoginsa sai dai idan mummy ne ta aikesu sukai masa wani abun shima hakan suna kai masa zasu juya abunsu."
——————
Najeeb keta kiran wayan sadam yaqi dagawa saura 5minute su shiga test amma sadam bai qarasowa hakan yad'agawa najeeb hankali yakira wayarsa kuma sai tayi ringing harta katse amma bai dauka,
Iska mai zafi najeeb ba furzar baison mai yake damun sadam ba gabaki d'aya yanzu yadawo wani iri abunda yaga dama shi yakeyi
Bai gama ida tunaninsaba saiga sadam ya iso, cikin zafin rai najeeb ya nufeshi yana fadin sadam amma kaga time kuwa?
Yanzu saura 3minute ashiga amma sai yanzu kake isowa?
Ko kulashi sadam baiyiba yawuce ciki abunsa dasuari najeeb yabishi yana fad'in sadam na dadefa anan ina jiranka amma shine daka iso ko kallo ban ishekaba zaka wuce sannan kuma nasan kaga kirana kaki d'agawa,
Advertisement
Tsaki sadam yaja yana fadin wai kai ina ruwankane?
Wai kai nake yiwa karatun kowa kaina?
Idan naga kiranka saime? banyi niyyar dagawa bane yafad'i sannan yashige ybar najeeb awajan da mamaki,
Gabaki daya yanzu sadam ya canja,
Baison mai yake damunsaba,
Yanzu duk jiransa da yayi wulakancin da zai saka masa dashi kenan?
Can ciki sadam yawuce ya zauna alamun bayaso kowa yazo wajanda yake,
Ganin haka yasa najeeb shima ya naimi waje nesa dashi yazauna,
Ahaka har aka shirya test din aka yi aka fiffito,
Bayan angama najeeb yatashi yafice bai ko kalli wajanda sadam yakeba,
Kusan 2hours sadam yana zaune babu najeeb gabaki daya sai yaji wani iri duk jikinsa yabi yayi sanyi yasan abunda yayiwa najeeb bai kyautaba,
Shikansa yasani idan aka cire mahaifiyarsa babu mai nuna kulawa akan lamarinsa fiyeda najeeb,
Kifa kansa yayi jikin table wani iri yakeji cikin ransa shi kansa baison mai yake damunsaba yarasa mai yasa yake nuna zafin rai akan kowa,
Wanda canda bahaka yakeba baisan dalilin dayasa yanzu abu kadan yake 6ata masa raiba,
D'ago kansa yayi yana duba cikin class din koda zaiga najeeb amma bai ciki,
Fushi najeeb yayi ransa ya raya masa, tafin hannunsa biyu ya sanya ya rufe fuskarsa yana fadin ya Allah🥺 shi kansa yasan halin najeeb yasan wanene najeeb, kwata-kwata bai iya fushiba duk zamanda zakayi dashi idan kace kaga fushinsa to kayi masa karya,
Tunda yau njeeb yayi fushi yasan ba qaramin 6aci ransa yayiba, gabaki daya saiya dawo yanajin haushin kansa, yana cikin wannan tunanin yaji anzauna kusa dashi,
Bud'e idanuwansa yayi ya saukesu akan najeeb,
Murmushi najeeb ya aika masa hadeda miqa masa wata y'ar bag yana fadin nasan bakayi breakfast ba natafi nema maka abinda zaka karya dashi kuma sai yanzu nasamu layi yayi yawa,
Najeeb yana maganane kamar babu wani abunda yafaru,
Da kallo kawai sadam yake binsa cikin ransa yana ayyanawa inama dashine da zuciya irinta najeeb,
Yadade baiga mutum mai sauqin kai irin najeeba ba,
Daga masa kai najeeb yayi yana fadin malam wannan kallon fa?
Ajiyar zuciya sadam yasauke sannan yace" dama ba fushi kayiba?
Zaro ido najeeb yayi yace fushi kuma😳 sannan yanuna kansa yace ni? A'a nikam ba fushi nayiba,
Nayi fushi kuma awani dalili?
A dalilin cewa na 6ata maka rai sadam yabashi amsa,
Murmushi najeeb yayi sannan yace eh tabbas datsu ka 6atamin rai kuma naji babu dadi amma yanzu yawuce,
Ni bazanyi fushi dakaiba sadam a kullum nakan baka uzuri komai dan adam yayi arayuwa kafin kayi fushi ko daukan wani mataki kayi tunanin dalilinsa na aikata wannan abun,
A kullum nakan bawa mutuminda nake tare dashi uzuri saboda wani lokacin bazaka ta6a fahimtar halinda wani yake cikiba idan ba yafada makaba, bazaka ta6a fahimtar mai yasanya ya aikata abunda ya aikataba, wasu abubuwan idan ba kaine amtsayin mutumba bazaka ta6a fahimtar halinda yake cikiba, bakowani abu bane ake aikatashi babu daliliba, dole inbaka uzuri sannan in sake baka uzuri har indai bazan baka uzuriba akan kayimun abu ba dai-dai ba menene amfanin zaman taren sadam?
Nasan cewa ba haka halinka yakeba dole wani abu yake damunka yasanya ka canja wanda bakason fadansa idan bazan takuraka ka fadamin damuwarkaba kaga ai bazan gaza wajan hakuri da abunda zakayiminba,
Kaga ko kadanne nima nadamu da damuwarda take damunka,
Da ido kawai sadam ya tsareshi, gabansa yana wani mummunan faduwa kalaman najeeb keyi masa yawo a dodon kunnensa, ji yakeyi kamar najeeb da biyu yake maganarnan,
Uzuri! Ya maimaita a fili,
D'an dukan kafadansa najeeb yayi yace ehem uzuri nama mutumina,
Sau dayawa idan zaka yiwa wanda kake tare dashi uzuri zaka samu koda damuwace ba lallai ka shigeta sosaiba, bana yanke hukunci batareda nasan dalilin dayasa aka aitakata wani abuba,
Wani irin sanyi jikin sadam yayi sosai bai iya cewa komaiba sai rungume najeeb dayayi,
Nisawa najeeb yyi ya tabbata sadam yana cikin damuwa amma bazai takura masa akan saiya fada masa damuwarsaba zaiyi addu'ar Allah ya yaye masa sannan kuma zai jira har lokacinda zaizo ya fada masa da kansa,
Sakeshi sadam yayi yadauki bag dinda najeeb yakawo masa yace sutafi
wucewa sukayi hostel acan sadam yayi breakfast amma hankalinsa gabaki d'aya yana kan maganganun sadam,
Sai yanzu yake ganin rashin dacewar abunda ya aikata shi kansa yasan baiyi dai-dai ba, awancan lokacin daya bata uzuri akan halayyarta yabata uzuri akan maganaganunsa duk haka bata faruba,
Wani Gauron numfashi ya sauke, juyowa najeeb yayi yana dubansa yana kwance idanuwansa suna lumshe amma ba bacci yakeyiba saboda yanata jijiiga qafafunsa,
Lafiya? Najeeb ya tambaya, sanda sadam yadauki dan lokaci sannan yace lafiya qlau,
Kai kawai najeeb ya gyada ya maida kansa yaci gabada damuwarsa shikuwa sadam yaci gaba shima da aikin tunaninsa,
Yana kwance kamar wanda aka tsikarashi ya miqe tsaye zumbur."
✔️ote
Comment
Share
Follow
To be continued
Zaynab Alabura
Advertisement
- In Serial22 Chapters
(Dropped)The God Of Apocalypse
Do you like Overlord? Do you like (Insert fantasy universe here) then this is for you my friend! YGGDRASIL MK2 has come and our little guy is going places. Follow him going to several fantasy universes that you all know and love! See him stomp all opposition because he is The God Of APOCALYPSE Scary... (This is nothing serious. Take everything with a grain of salt.)
8 173 - In Serial38 Chapters
Tower of Redemption
Kauss Mellow was born on the first floor of the Regal Tower. Since childhood, his life has been centered on survival. Yet even in a world of kill or be killed, he manages to build some normalcy for himself, with his girlfriend and close (though odd) friend. But the tower has never been a place to allow long term peace.Now, Kauss and his friends must climb.The top of the tower awaits them, and along the way, they will find new allies, make dangerous enemies, and discover things previously unknown.
8 90 - In Serial8 Chapters
Megane Saga
Shizuka Kurokawa was a normal highschool girl, until she was summoned to another world with three other students. She and the other three were summoned to fight against the evil demon race, and of course they were given unique abilities to accomplish that. No, the other three did get their own abilities, but Shizuka got none.Little did everyone know, she was already summoned as a hero before and still has the ability she got from that. She may not have any talent in magic and she might not have gotten an ability this time, but that’s not really a problem when she has already reincarnated a hundred times, due to her heroic ability, and has gained a lot of bonuses from it.
8 182 - In Serial10 Chapters
Wings and Cages
Among the people of Andalia, Princess Odetta Valdnrosa is rumored to be as beautiful as seafoam. As the only princess left alive in the royal family, it is assumed that she is one of the few siblings within King Casrian's good graces ever since he slaughtered most of their family. However, to her, the palace is nothing more than a prison... a cage created by her three wicked brothers.But the more Odetta learns about her family, both dead and alive, the more she gets drawn to them. Her yearning for a family has lied within her all her life, and that only festers along with her fear of the Valdnrosas.Perhaps in the end, Odetta is more of a true Valdnrosa than she thinks she is.
8 70 - In Serial16 Chapters
The wisher
In a black world, that gives a feeling of emptiness, stood a man. After killing the final boss in the game. The world around him went black, and a girl came out of nowhere.she was like an angel. White-eyes, hair, and skin.She looked at the man with eyes devoted of feelings and asked him ""what's your wish?"".the man lowered his head and began to think.Thinking about his life, about how his parents died in the war and he never felt their love, how he was an outcast that no one wanted to get close to, throughout his life, he felt lonely.The only exception to his loneliness was his friend. he never met her in person. she was lively. he liked her if he was more honest with himself, he loved her. He already knew what he wanted as a wish, But she will hate him for that, he was sure of it.He looked up, straight at the eyes of the girl and said ""any wish?"".She answered with a nod.After a moment of silence, the man said with a hint of anticipation “then... Make this world and the real world into one. I want this kind of life to become reality. Give me a chance to live in the real world.""
8 168 - In Serial8 Chapters
Crimson Prison Of Black Domination {Discontinued}
Issei finds out the truth about his reincarnation as a devil. See what will issei become and what course of action he takes. This story is similar to 'path of supremacy or Road to domination'Btw I don't own highschool dxd or akame ga kill or any anime references to the anime.
8 65

