《ƘADDARAR RAYUWA》Q page 15
Advertisement
*بسم الله الرحمن الرحيم*
Haske writers association💡
Writing by
Zaynab bawa
Follow on
Page 15
A hankali ta d'auke idanuwanta daga kansa gabanta yana tsananta faduwa, yayinda taji qirjinta yayi mata nauyi,
Shikam sadam bai dauke idanuwansa daga kantaba bai kuma qarasa wajanba,
Ahaka najeeb yaqaraso ya siya abunda zai siya jikinta duk yabi yayi sanyi tazuba ta miqa masa,
Kudin ya miqa mata ta girgiza kai alamun bazata kar6a6a
Da mamaki najeeb ya kalleta yana fad'in kudinkefa nake miqa miki zatonsa ko bata gane mai yake nufi ba, qara girgiza kanta tayi cikin sanyin murya tace eh nasani kabarshi kawai,
Babu yanda najeeb baiyi ta kar6aba amma fir taqi haka yataho yana mamakinta,
Yaqarasa wajan machine din yana fadawa sadam,
Sai alokacin sadam ya kauda idanuwansa daga gareta yadubi najeeb ya ta6e baki baice komaiba yahau kan machine d'insa,
Bin bayansa najeeb yayi shima yahau bai qara juyawa wajantaba ya tada mashin dinsa suka bar wajan,
Wasu hawaye masu d'umine suka zubo daga idanuwan sawwama,
Hannu ta sanya ta share hawayen fuskarta taci gabada aikinta,
Ko babu komai tadanji sanyi cikin ranta saboda ta tabbata yafara saukowane har yazo wajan dukda cewa bai qarasoba,
Koma dai yayane yau abunda takeji yadan ragu,
Share hawayen taqarayi daya qara zubowa,
Ita kad'ai tana aiki tasamu kanta da sakin murmushi,
Shikuwa sadam nasa wajan fess yakejin ransa sanyata a idanuwan dayayi kad'ai ta d'ebe masa kewarta dake addabarsa, barinma tsakanin jiya dayau, sosai ya kalli kewarsa akwance akan fuskarta,
Kamar yanda suka zo yana tuqi ahankali haka suka taho ahankali zuciyarsa gabaki daya tana cikeda annashuwa,
Sa'i-sa'i yake sakin murmushi,
Ta6oshi najeeb yayi yana fad'in lafiya kuwa?
Sadam baice masa komaiba saima qara maida masa murmushin yayi,
Ganin haka yasa najeeb yin shiru har suka isa babu wanda ya tankawa wani,
Ana shirin yin magrib sadam yakoma gida, agida yayi sallah,
Yana zaune hotonta ne kawai yake fado masa arai saiya lumshe ido yayi murmushi,
Duk da bawani magana ne ya hadasuba amma yau kam sadam yayi kwanan farin ciki,
Zafinda yakeji cikin ransa duk babu."
Itama sawwama nata wajan abubuwan da sauki yau kam,
Ko babu komai ta sanyashi a ido tasan yana cikin qoshin lafiya,
Sannan alamu yanuna yafara sauka,
Akowani irin lokaci zai iya saukowa gabaki d'aya."
Kafin weekend ya qare kullum sai sunzo amma shi daga gefe yake tsayawa sai najeeba ya qarasa,
Idan ya harde hannu akirji sai yahau aikin kallonta har sai najeeb yasiyo yadawo sannan sutafi, kuma har lokacin taqi kar6an kudinsu, ganin haka yasa najeeb idan bata kar6aba Sai kawai ya ajiye mata yatafi."
Advertisement
Ranar monday tareda najeeb suka koma school,
A school sadam yayi magrib,
Yakamo hanya, yau kam sadam da niyyarsa tazuwa wajanta koda sallama ce tashiga tsakaninsu,
Wajanta ya nufa lokacin yasameta tana tattare kayanta tagama sana'arta yaqare dawuri,
Nesa da ita ya ajiye mashin dinsa ya tattaki ya qaraso wajanda take,
Sallama yayi da sauri ta juyo jin muryarsa,
Bakinta yana rawa ta amsa sallamarda yayi mata, adan daburce ta daura da fadin ina wuni?
Lafiya ya amsa yabude baki zaiyi magana kafin ya qarasa yaji siririyar muryarta ta daki dodon kunnuwansa da fadin ya qare, ita azatonta awarar yazo siya,
Toh kawai ya amsa atakaice baibar wajanda yakeba bai kuma juyawaba yana tsaye,
Itama shiru tayi takasa aikata komai."
Tsugunnawa yayi a gabanta nan gabanta yahau dukan uku-uku
Cikin sanyin murya yace" nayi miki tambaya na nemi alfarma wajanki amma ban samu koda guda d'aya cikin abunda na buqataba,
Dafarko na dauki fushi sosai akan abunda yafaru, daga baya nazo nayi realinzing kowani mutum da irin yadda yake tafiyarda rayuwarsa,
Kowani dan adam akwai abubuwan acikin rayuwarsa,
Duk wanda kaga ya aikata wani abun na tabbata akwai dalilin aikatawa,
Bazan tilastakiba bazan takuraki akan saikin fadamin dalilinki ba,
Amma inaso kisani wallhy banida niyyar cutar dake, banida mugun nufi akanki,
Wanima bazan iya cutarwaba balle ke da haka kawai nake ganin kimarki da girmanki a idona,
Nasan akwai abubuwa arayuwa wanda suka zama sirrin mune, kokadan bazamuso wani yasaniba, balle daya kasance har yau bakisan koni wayeba, nasan wannan abune mai wuya kisake jiki da mutuminda bakisanshiba, awancan lokacin yakamata na fahimci hakan,
Amma nagaza fahimtar hakan,
Dole zanci wani iri har indai da gaske nake na damu dake iringa kallonki ahaka baki zuwa makaranta,
Bance sana'arki ko neman na kanki yazama aibuba nasan kowa da matsayinda ubangiji ya ajiyeshi,
Lokuta da dama zuciyata takan nusar dani akan narabuda ke nadaina shiga duk wani harkokinki saboda bakyason hakan amma na gaza,
Zuciyata atsarkake take akanki,
Bansan daliliba bansan mai ubangiji yake nufiba Allah yagani shine yahada jinina dake, magana bawani shiga tsakanina dake takeyiba amma Allah yasanyaki cikin mutane masu mahimmanci arayuwata kuma bazan iya cewa ga daliliba,
Kamar qanwata haka nake jinki bazanso aikata mugun abu akankiba,
Dan Allah kiyi hakuri kidaina nuna wannan tsoron nawa kokuma rashin yarda afili hakan zaisa nayi nesa dake koda banso hakanba,
Saboda duk yanda naso in kyautata miki idan naga hakan zai cutar dake dole zanja jikina,
Advertisement
Shiru sawwama tayi tana sauraron kalamansa zuciyarta take tayi mata zullumi shin da gaske yakeyi tana daya daga cikin mutane masu muhimmanci arayuwarsa? Har cikin zuciyarsa yayi wannan maganar kokuma dai kawai ya fadetane?
Amma kuma alamu yanuna mata daga qasan zuciyarsa maganar take fitowa,
Hawaye taji yafara gangara akan fuskarta,
Ganin hawaye akan fuskarta ya sanyashi runtse idanuwa yana fad'in subhanallahi wani zafi yaji acikin zuciyarsa ganin hawayenta dai-dai yakeda tarwatsa duk wani farin cikinsa, cikin sanyin jiki yace dan Allah kibar wannan kukan idan nine nayi alqawari bazan qara takura mikiba,
Girgiza kai tayi tace ni baka takuramin ba, hasalima ban dauka zam sami muhimmanci arayuwar wani irin hakaba,
Kamar yanda kafada kowani bawa da tasa qaddarar kowani dan adam da jarabawarda ubangiji yake aiko kasa,
Ni tawa Qaddarar kenna,
Zuwana makaranta bazai zama maslaha a halinda muke cikiba,
Baka takuramin kuma baka ta6a takuramin ba,
Nidai kawai banaso karinga sanya kanka cikin al'amurana dayawa, rayuwa tana da sirri, kowani dan adam yanada sirri, bai dace ace nafada maka sirinaba,
Nisawa yayi sannan yace idan bakyso nabari bazan ringa qoqarin sanya kainaba,
Amma dole in damu da halinda kike ciki,
Jijjiga kai tayi sannan tace nagode da kulawa Allah ya biyaka da mafificin alkhairi,
Amin ya amsa sannan yace har yanzu bansan sunanki,
Qasa tayi da kanta tace hafsatu sawwama,
Ma sha Allah kawai ya furta,
Ni zan tafi zan iya dawowa gobe? Ya tambaya,
Dasauri sawwama tad'aga masa kai,
Murmusawa yayi sannan yace nagode sawwama, kanta yana qasa kawai tayi murmushi,
Sallama yayi mata yatafi yayinda ran kowannensu yake cike fall da farin ciki,
Awannan ranar dukda cewa cikinsu babu wanda yasan mai yakeji gameda d'an uwansa amma dai sun san sunyi kwanan farin ciki,
Sadam koda yazo school tunanin maganganu sawwama najiya kawai yakeyi, da nutsuwa sosai atattare da yarinyar maganganunta akwai hankali aciki,
Idanta furta kalma idan kaduba zaka samesu a mazauni yanda yakamata a ajiyesu,
Najeeb ne ya qaraso lokacin sadam yayi nisa cikin tunani har yazauna baisanda isowarsaba,
Saida ya ta6ashi sannan yadawo daga tunanin yajuya ya dubeshi,
Kai najeeb ya d'aga masa yace lafiya?
Babu komai sadam yabashi amsa atakaice,
Ehem dama nasan amsar kenna babu komai babu komai,
Kullum dai zancen kennan,
Wai sadam har yanzu bamu kai matsayinda yakamata ka fadamin sirrinka bane?
Nayi shiru koda zata fadamin amma shiru kaki fada kuma nasan abun yana damunka,
Barin kashi aciki baya maganin yunwa,
Daka furtamin wata qila na iya sama maka mafita,
Kasanni sadam kasan halina bana boye maka al'amurana idan ina neman shawara kai nake fara tinkara,
Yanda na daukeka sadam ba haka ka daukeniba amtsayin dan uwa na ajiyeka wanda zan iya sharing damuwata dashi amma kai ba hakaba,
Iska sadam ya furzar sannan yace me kakeso nace maka najeeb,
Kace komai inajinka, najeeb yafad'a,
Najeeb ni kaina bansan mai yake damunaba,
Wata yarinyace
Zaro ido😳 najeeb yayi yace yarinya?
Eh lallai yace sai kuma yahau dariya,
Bata rai sadam yayi nan da nan zuciyarsa tahaura sama,
Banson rashin mutumci najeeb ina ga irinta nan kace nafad'a maka damuwtaa nafara fadi kahau yimun dariyar iskanci,
Mtseww yaja tsaki,
Dakewa najeeb yayi yace" kayi hakuri nabari,
Bata rai yayi yace shikenan ai yawuce,
Cin serious najeeb yayi yace dan Allah kayi hakuri Allah nabari,
Sanda yadan dauki lokaci kafin yaci gabada fad'in,
Wata yarinyace najeeb wallhy tausayinta nakeji tana cikin wani irin hali da zaran na ganta cikin damuwa kokuma wani abun bacci kauracewa idanuwana yakeyi
Banida aiki sai tunaninta da halinda take ciki,
Kowacce magana tafad'i takan tsaya min arai,
Nadade banji mutuminda tunaninsa ya zamanmin jikiba irinta,
Najeeb koda abun 6acin rai tayimun 6acin ran yakan shafi kowa da kowa,
Nakanji zafin kowa abu kadan akaimim zan farajin haushin mutum,
Ta dalilin son ganinta yasa nake skipping lactures,
Ranar sanda nayiwa mummy qaryan test akanta,
Nan yaringa yiwa najeeb expressing abubuwanda yakeji akanta, sannan yadaura da fadin najeeb bansan mai yake damunaba,
Bansan dalilin duk wannan damuwarba,
Jijjiga kai najeeb yayi yace wato duk wannan tarin dalilin daka lissafomin bakasan menene dalilin hakanba?
Gyada kai sadam yayi,
Miqewa najeeb yayi yana kallon zancen sadam ma rainin hankaline,
Aishi ba qaramin yaronda har zai kasa gane mai yake damunsa bane,
Kallonsa sadam yayi yana fadin ina kuma zakaje na tambayeka maimakon ka bani amsa shine zaka fice,
6ata rai najeeb yayi yace Allah sadam abunnaka harda tsantsan rainin hankali yanzu kacemun bakasan abunda yake damunkaba?
Gyada kai sadam yayi yace wallhy babu rainin hankali awannan lamarin najeeb dagaske nakeyi,
Tsantsar gaskiya najeeb ya hango a idon sadam hakan yasa ya koma ya zauna,
Yadubi sadam yace" sadam son yarinyarnan kakeyi,
Zaro ido sadam yayi atsorace yace so kuma?
Kai ina A'a."
✔️ote
Comment
Share
Follow
To be continued
Zaynab Alabura
Advertisement
- In Serial331 Chapters
God Rank Upgrade System
“As long as I level up another 10 times, I will be able to activate the Gene Lock. At that time, I will be able to destroy this celestial body!” After transmigrating into the body of a trash in a future where zombies and intellectual beasts existed, Lin Xiu accidentally obtained an upgrade system to transcend human limitations and devour the heavens!
8 4298 - In Serial47 Chapters
Kneel: A Guide to Demonic Ascension
Reais, a fractured abyss ruled by thousands of contesting Demon Lords no stranger to chaos happens to be the birth place of a new chaos, a new threat. Punished for disbelief in a mortal life, a soul curses Deities for its unfair imprisonment and psychological torture. Set free by witless demons, this soul sees an opportunity for vengeance. Do these Deities see this new chaos? Do they fear the incoming reprisals? Do they have the strength to stop this soul? Do they have the strength to resist the incursion, the subjugation, and annihilation? The answer is simply, Nil.
8 587 - In Serial46 Chapters
Intertwined Destinies
Malak Elsan always thought he was ordinary. Along with his twin, he was raised by his loving parents and attended school with his friends. But when he turned eighteen, he crossed a man he had never met; yet a man who felt familiar. With danger approaching and memories regained, Malak will once again have to fight a thousand-year-old war alongside his beloved, in a world filled with bizarre creatures and magic. The story starts slowly and may seem plain, but I promise it'll get more interesting over time. The action, fantasy, and magic will be at the rendezvous!
8 212 - In Serial8 Chapters
Kingdoms Fall, Heroes Rise
The kingdom of Exaul is falling. A nation one thousand years in the making is coming to an end. Villages and towns vanish by the day, destroyed by monsters, bandits, and the undead. While many refuse to accept this, those who can read the writing on the wall can only resign themselves to an approaching dark age and prepare for the long night to come. A few, however, believe in the legend of how Tiago, the great hero who vanquished the Dark Lord two centuries ago, will return to save the kingdom in its darkest hour. He's not coming. However, three young women will do everything they can to give the kingdom the hero it needs to give hope in these dark times... even if they have to build him from the ground up.
8 64 - In Serial42 Chapters
That Guy Is Boring
Welcome dear Players!Those lucky enough to hear this message will now be transported to the Chessboard. Try to survive and reach the end of the game unharmed. As a gift from the Administration, you will not have to worry about the dangers of the Game for the first two days. Remember, The System of the Ancients was not meant to be fair, so expect to find injustice.Have fun and try not to die too quickly! [before reading] -> This novel is the English version of an Italian one. Some details may have been lost in translation.
8 158 - In Serial9 Chapters
The Forgotten Extra
The Forgotten Extra A boy at the age of 20 named Joseph Fox used to be a kind, sweet-hearted kid but ever since his Sister's death, Mother's suicide, Father's death, and catching his girlfriend cheating on him with his best friend Blake. He became Cynical, Lonely, Depressed, and down on his luck. After getting Fired for the worst reasons. After stealing a very strange yet intriguing book, He gets transported to a new yet mysterious fantasy-like world and being the Forgotten extra
8 183

