《ƘADDARAR RAYUWA》Q page 18
Advertisement
*بسم الله الرحمن الرحيم*
Haske writers association💡
Writing by
Zaynab bawa
Follow on
Page 18
Wannan dare sawwama bata samu ta runtsa ba, kamar yanda taga rana haka taganshi har tsoron wayewar gari takai batayi bacci ba, gashi wani irin sauri da daren yayi mata, adaren sawwama taja Allah ya isa ma wanda ya aikata mata wanna abun yafi cikin kwando, baqin ciki da tashin hankali daya sanyata aciki kadai ya isa Allah ya saka mata, ta dalilinsane take cikin wannan fargaba da zullumi da tashin hankali, sake sakenda taringayi kenan har sanda taji kiran sallah,
Gani tayi Anyi saurin kiran sallah, daren yayi mata gajarta garin ya waye mata da wuri anata wajan, koda mama tazo tashinta ta sameta idonta biyu,
Mama batayi tunanin sawwama batayi bacci bane anata tunanin kiran sallah ne ya tasheta, da fargaba tatashi dan gani takeyi rabuwarsu ne yazo taje tayi alwala baba yajasu sallah, Addu'a kam kala-kala sawwama tayisu wasuma bata ta6a yiba amma yau sanda tayi."
Haka da gari ya waye ma gani takeyi komai sauri yakeyi mata,
Ba taso yamma tayi saboda ba taso sadam yazo har wannan magana tashiga tsakaninsu da mahaifinta ta tabbata daga wannan lokaci bazata sake sanyashi a kwayar idanuwanta ba,
Haka tawuni jiki duk a sanyaye mama da kanta ta fahimci hakan ta kirata tanata yimata nasiha akan tadauki qaddara ko wace irice,
Kuma koda ace wannan yatafi idan yaji abunda tafaru da ita Allah zai sake kawo mata wani,
Haka tayita lalla6ata."
Sai bayan anyi magrib kafinann sadam yazo, ayanda ya saba zama ya isa ya zauna,
Sawwama tana kallonsa jikinta yadauki rawa takasa gaisheshi tana addu'ar Allah yasa kar yazo sai kuma gashi yazo,
Gabantane yahau faduwa ta sunkuida kanta qasa har cikin ranta bataso zuwansaba,
Dakyar ta iya furta sannu da zuwa,
Amsawa yayi da fadin yawwa,
Daga nan dukansu sukayi shiru,
Har yanzu baki yanke shawaraba kenan?
Ya jefo mata tambaya,
Nisawa tayi cikin nutsuwa tafara magana da fadin yanzu yanke shawara yana wajan ka,
Kamar yaya awajena?
Ya tambaya amma kinsa nikam aii na sanar dake abunda yake zuciyata sannan kuma nabarki ki yanke hukunci,
Girgiza kai tayi sannan tace yanzu hukuncinka ne yarage ni nawa zakaji daga baya,
Cikin rashin fahimta yace kmar yaya? babana ne yakeson ganinka zaiyi magana dakai, ta katse zancen batareda tabashi amsa tambayarsa ba,
Toh sadam ya amsa
Ko d'ar sadam baiji ajikinsaba cewar mahaifinta yana nemnasa, yasan koda mahaifinta bai nemeshiba shi zai nemeshi, tunda yasan shi bada wasa yazoba,
Advertisement
D'agowa tayi taga yanayinsa amma sai taga babu ko alamar damuwa atattare dashi,
Alokacin ta qara tabbatarwa cewa da gaske yakeyi danta tabbata daba da gaske yakeyiba da tana ambatar mahaifinta yanayinsa zai canja,
Kallonta yayi yace baban yana inane?
Yana cikin gida tabashi amsa,
Ki sanar masada zuwana sadam ya umurci sawwama,
Jiki a sanyaye sawwama ta tashi tanufi gida tana tafiya tana kalloshi kamar wanda ya kasance kallonta na karshe dashi kenan,
Ta shiga cikin gida tasamu baba yana zaune abarandar qofar d'aki qarasawa tayi ta durkusa tana fadin sannu da dawowa baba,
Amsawa yayi yana fadin sannu sawwama,
Duqarda kanta qasa tayi tace" baba ya iso,
To madallah yana qofar gidane?
Girgiza kai tayi tace A'a yana wajan canne,
Maza je kice masa ya qaraso zuwa qofar gida,
Miqewa sawwama tayi cikin nustuwa tafice baiji zuwantaba ya nutsa cikin tunani saida tayi sallama da siririyar muryarta,
D'agowa yayi ya amsa cikin nutsuwa,
Qasa tayi da kanta tafara wasada yatsun hannunta a hankali ta furta wai inji baba ka qarasa zuwa qofar gida,
Miqewa yayi yace muje cikin nutsuwa tafara tafiya yana binta abaya,
Yarinyace qarama amma komai nata anutse take yinsa har yanda take taka qafafunta cikin nutsuwa komai nata atsare yake,
Nutsuwarta tana d'aya daga cikin abunda yake fisgarsa yakejin kullum tana qara shiga ransa,
Sanda suka kai qofar gidan sannan tatsaya tace barina shiga nayi masa magana,
Kai ya gyada tashiga ciki ta sanarawa baba qarasowarsa,
Baba bai dauki lokaciba yafice,
Atsaye yasameshi sadam yana kallonsa ya tsugunna qasa cikin girmamawa yana gaidashi,
Amsawa baba yayi cikin sakin fuska,
Yana fadin madallah mamana ta sanar dani abunda yake tafe da kai, to shine nace mata inaso mudan zanta ni da kai sai naji ta bakinka,
Waqa bakin mai ita tafi dadi, yanzu saika yimun bayani inaji duk da tayimun bayani amma zanfison ji daga bakinka,
Cikin jin kunya sadam ya sanarwa baba abunda yake tafe dashi,
Baba yace toh yanzu aina kake sannan kuma inason sanin sunan mahaifinka dakuma yanda kuke zama,
Ko d'ar babu sadam ya sanar dashi abubuwanda ya kamata ya sani gamedashi,,
Jijjiga kai baba yayi yace toh banqi takaba sadam amma baka ganin cewa kai din ba sa'an aurenta bane? Ina nufin kwarya tabi kwarya tanemi dan uwanta talaka marar galihu irinta baka ganin hakan zaifi, duba da yanda ya kasance cewa kai qaramin yarone, idan kai kagani kanaso kana ganin wajan mahaifanka baza'a samu matsala ba?
Girgiza kai sadam yayi yace baba nikam tunda ni na ganta ina sonta ai babu komai, dama kuma yanzu ina karatune baifi saura shekara daya da rabi nagama ba,
Advertisement
Idan nagama nasan lokacin bazan samu matsala daga wajansu ba amma yanzu koda naje musu da zancen ban rigada nagama makaranta ba bazasu amincewaba,
Jijjjiga kai baba yayi yace naji dad'i daka fito ka fadmin gaskiyarka,
Hakanne yasa nima yanzu zan fito nafad'a maka iya gaskiyata,
Abunda nakeso kasani shine ita Qaddara abace marar tabbas zata iya zuwa maka mai kyau kokuma marar kyau,
Qaddara bata wuce kan kowaba sannan kuma ita rayuwa daka gani kowa da irin tasa Qaddarar,
Qaddarar rayuwa mafi yawanci kowa saiya fuskanceta wasu ta kasance musu mai kyau wasu asakin haka,
Babban abun shine muyi imani akanta mai kyau ko marar kyau,
Mu sanya aranmu cewa ubangijine yake daurowa bawansa kaddarar,
Jarabawace ya jarrabeka,
Tabbas akwai qaddara mai muni data faruda mamana,
D'agowa sadam yayi yana dubansa gabaki d'aya jikinsa yayi sanyi ya qagu yaji mai akeson fada masa,
Nisawa baba yayi sannan yaci gabada cewa ba ita ta za6awa kanta hakanba, bakuma ita tadaura kanta hakanba ubangijine ya sanya wannan Qaddara ta fad'o cikin rayuwarta,
Sadam Shekarun baya da suka wuce babban al'amari yafaru da sawwama nisawa baba yayi sannan ya saukarda numfashi sannan ya furzarda iska mai zafi ga dukkan alamu abunda yakeson fadi yayi masa nauyi,
Cikin sanyin jiki sadam yake dubansa gabaki daya yanzu yashiga wani yanayi, zuciyarsace ta hau bugawa fargabarsa d'aya kada baba ya furta masa bazai iya bashi auren sawwama ba,
Baba ne yaci gabada magana, anta6a yiwa sawwama fyade shekarun baya da suka wuce,
Runtse ido sadam yayi jin yanda maganar ta dukesi,
Bai bude idonsaba yaji baba yaci gaba da fad'in,
Sawwama bata cuci kowaba kuma bata zalinci kowaba amma ita anyi mata zalinci mafi muni,
An 6ata mata rayuwarta,
Hawayene suka taru tabb a idon sadam cikin jin zafin abunda yafaru da sawwama yace baba kuma ba'a dauki mataki ba?
Babu matakin da aka dauka. Saboda koda zamu dauki mataki bamusan wayeba, koda munsan waye bamuda halin yin shari'a dashi,
Baba yadubeshi yace" sawwama tnada tarbiya tanada hankali sosai,
Tanajin zafin abunda yafaru da ita fiyeda kowa aduniyarnan, sawwama tanada kyawawan halaye d'abi'unta masu kyaune, bawai danna kasance mahaifin sawwama ba A'a duk wanda yake tareda ita zai fad'i kyakkyawan halinta."
Nafada maka wannan abunne saboda har indai neman aurenne dagaske tabbas ya kamata kasani, sirrinane nida iyalaina,
Kaje ka yankewa kanka hukunci,
Ka yanke duk wani abunda zuciyarka ta ayyana maka bazan hanaka ba zan fahimceka,
Saboda ba kowa bane zai iya daukan wannan al'amariba,
Idan ka yanke shawarar ci gabada nemanta Alhamdulillah sai muyi muku addu'a idan kuma ka yanke shawarar rabuwa da ita dan Allah ina roqonka daka dauke kafa daga wajanta dan Allah kayimun wannan alfarmar banason ganinta cikin wani hali,
Ganinka zai iya sanyata cikin wani hali,
Sannan ina neman alfarma d'aya har indai ya kasance zaka rabu da ita ina roqonka daka rufamun sirrina,
Duk duniya idan kacire ita da mahaifiyarta dani babu wanda yasan wannan zancen sai kai dana fadawa,
Inba ace yakamata kasaniba bakina bazai iya furtawa kowa wannan zacenba,
Dan Allah ka rufamin sirrina wanda ya rufa asirin wani Allah zai rufa masa nasa,
Har indai kabud'e duniya tasani kowa da irin kallonda zaiyi mata, wani bazai dauki hakan matsayin Qaddara ba, kowa da irin fahimtarda zaiyiwa lamarin,
Sadam bai iya cewa komaiba har baba yayi masa sallama yakoma ciki,
Sadam ya dade awajan dakyar ya iya d'aga kafarsa yabar wajan."
Baba bayan ya shiga gida yakira sawwama zuwa d'akinsu,
Itada mama yabasu labarin duk abunda yafaru sannan yadaura da fadin mamana inaso ki sanyawa ranki samu da rashi na Allah ne banaso kishiga damuwa ga duk wani irin hukunci dazai yanke inaso kidauka rubutaccen al'amarine duk abunda Allah ya rubuta saiya faru,
Kina zaune mijinki zai riskeki, idan kuma Allah ya rubuta cewa mijinkine babu makawa kota wani irin hali saiya zama mijinki,
A gaskiya na yaba d hankalin yaron sosai yanada nutsuwa irin mijinda nakeyi miki fata kenan akoda yaushe,
Amma idan hakan bai yiwuba inaso ki sanyawa ranki salama. Allah shi yafimu sanin abunda yafi dacewa damu,
Jijjiga kai sawwama tayi kalaman mahaifinta yasa taji sanyi cikin ranta,
Godiya tayiwa babansu sannan ta miqe tatafi,
Bayan ya fita mama tadubi baba tace duk wanda ya aikatawa sawwama wannan aiki Allah bazai barshiba.
Sai Allah yayi mana sakayya mai muni shi ya cuci rayuwarta shine yasamu cikin wannan zullumi da taraddadi,
Shine ya jefe rayuwarmu cikin tunanin zai yiwu ko bazai yiwuba. Amma babu komai Allah yana ganinsa kuma zaiyi mana sakayya,
Nisawa baba yayi sannan yace wannan haka yake, koma wayeneshi bai kyautatawa rayuwarmuba bai duba irin halinda muke cikiba ya qara jefamu cikin wani halin amma babu komai da sanin Allah."
✔️ote
Comment
Share
Follow
To be continued
Zaynab Alabura
Advertisement
- In Serial39 Chapters
Gadgeteer (The Crisis Nemeses Book 1)
On the night of July 29th of the year 2059, Vermillion Blue city was in mayhem. The Bastion of Heroism saw its most significant victory and defeat at the hands of one super-villain: Herttz. Ever since the night he publicly announced his retirement, The City and The Heroes' Operation Center (HOC) stood in a fragile line between order and chaos, and it has been like this for the next four years. However, change is bound to happen, a change that will turn the city upside down. And it all started when Shindo East's actions in a hostage situation set a chain of events in motion that completely alters his entire life. Shindo is forced to take an undeniable offer, causing the gadgetsmith to take on the alias Wattz, his life starting anew as a hero. ***Disclaimer***This story is intended for a young adult audience since some chapters will contain certain topics and descriptions related to PTSD, Violent Language, and blood. Although I'm writing with the intent of keeping it PG-16 by not writing these topics in extreme detail, I do recognize that some people can be either offended or triggered by this. Proceed at your own discretion.
8 138 - In Serial42 Chapters
Yagacore: The Dungeon that Walks Like a Man
The Dungeon System is breaking. Now the mutant cores will rise. Zaria was just a normal woman, living a simple life, right up until demons burst down her door and ate her heart. Normally that would be the end of the story, but Zaria was reborn as a dungeon core. Except nothing is normal for her. Due to instability throughout the universe, Dungeon Core generation is experiencing some unique bugs and glitches. Most of these mutant cores just explode after only a few hours of life. Zaria is one of those cores. Luckily for her, there’s a way to prevent her detonation - she must find and form a bond with a human witch to create a striga. Only then will she be stable enough to survive. Normally, this would be a death sentence anyway, but Zaria’s mutation gives her an ability no other dungeon core has had before: Legs. Now a walking house, Zaria sets off to find her striga, fight demons and monsters, build up a dungeon worthy of being run by the greatest heroes in the lands…and feed the insatiable appetite of her mimic mobs. Life sure isn’t simple anymore.From the author of Dinosaur Dungeon, Factory of the Gods, and others! Plus part of the same universe as those books as well as Roots and Steel and Block Dungeon!
8 462 - In Serial27 Chapters
Bone And Amber: The Inside Story On The Return Of The Dinosaurs
A miracle has been achieved: non-avian, Mesozoic dinosaurs have been brought back to life - not by a technical university or a government programme, but by a venture capitalist concern, for reasons of profit. The social, economic, and political ripples of this development will do much more than enable the simple launch of a theme park for the rich: they will change the world. FAQ: Do I need to know anything about the Jurassic Park franchise to enjoy this? No. This story is not exactly a Jurassic Park fanfic - it is a story about the de-extinction of Mesozoic dinosaurs. While the story begins with some of the events depicted in the Jurassic Park universe, it is very much its own creature, and designed for readers with no prior knowledge of the franchise. It will begin to diverge quite quickly, as well: the dramatic focus will not be on people running around tropical islands trying to be eaten. The whole point of the exercise is to explore the profound consequences and ripples an event like the mass-cloning of extinct animals would generate.Do I need to know anything about dinosaurs to enjoy this? Also no! Sensing a theme yet? Although, if I’ve done my homework correctly, a newbie to the subject will be able to pick up something - not just about the animals themselves, but about their role as a vehicle to better understand the history of life on Earth, and the application of the scientific method to a sadly fragmentary puzzle.Without further ado, please enjoy!
8 76 - In Serial33 Chapters
Camiare: An Isekai
Dominic Miller lived an average and simple life until he was suddenly reborn as Nathaniel Armis into a strange world. Dominic, now Nathaniel, soon comes to accept his isekai situation and works hard to become strong like any other isekai protagonists. However, he soon comes to learn the harsh reality that blindly climbing upward will only cause one to fall, hard. Meanwhile, an ancient prophecy surrounding Nathaniel's best friend looms in the horizon, along with signs of a massive demon invasion from the south. Not only that, conspiracies haunt the very structure of Camiare. At the same time, Nathaniel must figure out the mystery behind the Ortus Project, the only hint he has about his mysterious rebirth. Enjoy! (comment any ideas or thoughts, I would love to get some feedback!)
8 91 - In Serial24 Chapters
Ashen Ghost
Gravelroy, the last free city, giant metropolis. All ethnicities, cultures, and religions can be found there. Merchants, sailors, criminals, everyone is welcome inside its walls. Everyone but a king, the free citizens don't kneel. But some rulers on the continent would like for this to change... A country bumpkin coming to the Big City. Raised by the wilderness as much as the war. Turned criminal by necessity. A wounded and insane woman. A monster lurks in her prison. She struggles to regain her memories and dreams of escape. A tiny, insignificant meeting. It will send ripples through the world. Given time, ripples can become waves. With enough luck, once in a very long while, a wave will turn into a storm. Slaves, commoners, and soldiers. Bishops too, kings even. Perhaps the Emperor himself. Everyone will feel it. But for now, the stubborn little rock has yet to fall into the waters. He has quite a long way to go in fact. Let's give him a little nudge, shall we? With chance, something might happen. Life can be unpredictable. Especially when we consider the adventures of a crazy girl and a weird lad. Things might get dramatic as the prelude suggested, or they might decide to do as they want and go nuts. Maybe a bit of both. The girl will fight against her own mind, her prison, and her fate. Who imprisoned her and why? But maybe she has imagined everything. She is mad after all. To save someone dear, the boy fights hunger and city guards. Sometimes pigeons as well. Well, this city is cracked anyway. Cover art by Paul Lerouvillois.
8 190 - In Serial22 Chapters
IDK (I Don't Know) || Jensoo
Kim Jisoo, the most respected and feared person in the entire campus. School council president, Running for College honors, Head cheerleader and even a volunteer in the animal shelter, can't get away from the clingy innocent childish, Jennie Kim.-Funny fluffy story.Jensoo convertedOriginal story by ©KBLin0708
8 146

