《ƘADDARAR RAYUWA》Q page 19
Advertisement
*بسم الله الرحمن الرحيم*
Haske writers association💡
Writing by
Zaynab bawa
Follow on
Page 19
Haka sadam yatafi gida jiki duk amace,
Yarasa mai yake masa dad'i tunda yake arayuwarsa bai ta6ajin tausayin wani mahaluki kamar yanda yakejin tausayin sawwama a yanzu ba,
Tabbas dole sawwama taringa gwada rashin yarda qiri-qiri dole sawwama taringa nuna tsoronsa a fili, dole taqi aminta dashi alokacinda yazo matada batun taimako dakuma lokacinda yazo matada batun soyayya,
Wutarda ta qoneka bazakaso tasake qonarka ba,
Abaya yayi kuskure na daukan fushi da yayi da sawwama akan abunda takeda gaskiya akai,
Tabbas yanzu yaqara yarda idan ba kaine amtsayin mutum ba kokuma yafada maka abunda yake faruba dashi ba, kada ka ta6a daukan fushi da yanayin mu'amalarsa dakai,
Zancen baba yakasa fita aransa zancenne yake dawo masa yanajin wani irin zafi da quna cikin ransa, shekarun baya da suke wuce an ta6a yiwa sawwama fyade!
Shekarun baya da suka wuce hakan yana nufin sawwama tana qaramar yarinya kenan,
Inbanda wasu mutanen da rashin imani da tausayina menene har zakaji ajikin qaramar yarinya,
Ko yanzu sawwama bawani gama cika tayiba balle shekarun baya, yaqraa tabbatarwa rashin imani na mutane yayi yawa,
Yarassa ta yanda zai fassara wanna abun,
Haka ya kwana zuciyarsa cike da dumbin tausayin sawwama hadeda zugi da radad'i
Yanajin zafi aransa kamar ma qanwarsa aka aikatawa hakan,
Haka a school ya wuni jiki babu kwari, najeeb yaso sanin mai yake damusan shima sadam da farko yaso gaya masa amma sai yaga rashin dacewar hakan saboda shima kansa wannan abun yanzu yadawo sirrinsa ba sirrinta ita kadaiba idan yafadawa najeeb koba yanzuba zaiyita kallonta da wannan abunne,
Shikuma bazai ta6oso ayiwa matarsa wani kallo ba,
Haka ya shanye abun cikin ransa,
Duk da yaso yabi wajanta yau amma bai samu damaba,
Saboda yanda abun yake damunsa cikin jiki zuwa zuciyarsa,
Sawwama batayi mamakin rashin ganinsaba saboda dama tasa ranta da faruwar hakan,
Koda babanta yadawo ya tambayeta ko yadawo ta shaida masa bai dawoba,
Advertisement
Jijjiga kai baba yayi sannan yace nasan za'ayi haka shikenan ai Allah ya za6a miki mafi alkhairi kici gaba da addu'a,
Amin sawwama ta amsa,
bayan sun shiga d'aki itada qannenta da shirya musu wajan kwanciya kamar yanda ta saba itama ta kwanta amma me har qannenta sukayi bacci idanuwanta babu alamun bacci,
Saida dare ya tsala sannan sawwama tasamu damar yin kuka, awannan dare sawwama tayi kuka kamar ranta zai fita ta jawa wannan mutumi daya aikata mata Allah ya isa yafi cikin kwando."
Duk wata addu'arda tazo bakinta yi masa takeyi ta tabbata bazata ta6a yafe masaba, kuma ta tabbata komai daren dadewa sai Allah yayi mata sakayya akan wannan mummunan aikin da yayi mata."
Mama anata wajanma hakane har sanda baba yayi bacci ya farka ya ganta a zaune tambayarta yayi kafiya batayi bacciba,
Cikin damuwa tace baban sawwama tunanina wannan yaro gashi kafad'a masa komai kuma bai dawoba ina tsoro abunda zai biyo baya ba lallai ya iya riqe bakinsaba zaije yayita fadawa mutane har azo abu ya bazu bamusan wani irin kallo mutane zasuyi manaba.
In sha Allah haka bazata faruba baba yafara kwnatar matada hankali, nayi magana dashi na roqi wanna alfarmar yarufa mana sirrinmu,
Kayya baban sawwama ba kowa keda wannan alqawarinba saboda mutane yanzu sun 6aci kowa jira yake yaji taka yaya yayataka,
Da wannan dan wannan baba yafadi sannan yadaura da cewa nasan da haka amma yanada kyau mu kyautata masa zato in sha Allah haka bazata faruba,
Allah yayarda mama tace baba ya amsa da amin sai alokacin mama tadanji sanyi tasamu ta kwanta."
Bayan magrib kawai sai ga sadam yazo sawwama tana zaune hancinta yafara jiyo mata kamshin turarensa,
Bata d'agoba saboda tasan zuciyarta ke yaudararta tarigada ta cire rai da sake ganinsa, tasan bazai ta6a dawowaba,
Gabanta ya tsananta faduwa tashiga wani yanayi aduk lokacinda sadam zaizo saida tsinci kanta cikin wannan yanayin,
Aikinda takeyi takasa cigaba, jikinta yadauki rawa, jiki babu kwari tajuya ta kalli gefe, aikuwa ga mamakinta idanuwanta suka sauka akansa yazo daff da ita baqaramin mamaki sawwama tayiba mamakinta har ya gaza 6oyuwa sanda ya nuna akan fuskarta,
Advertisement
Qarasowa sadam yayi yana sakin mata qayataccen murmushi wanda ya qarawa fuskarsa annuri,
Zama yayi gefe dan kusada ita kadan sawwama takasa dauke kanta daga ganinsa,
Mamaki qarara akan fuskarta, wani murmushin sadam yaqara jefanta dashi sannan yace"
Mamakin me kikeyi? Daburburcewa tayi cikin rawar jiki tace
Mamaki kuma? Tafada tanason kauda zancen, gyada kai yayi yace" eh mamaki! saboda fuskarki tanuna hakan,
Jijjiga kai tayi yana kawai tayi tarasa mai yasa yake saurin gano halinda take ciki,
Bakiyi zaton sake ganina bane?
Taji ya jefo mata tambaya,
Gyada kai tayi hadeda fadin abunda yabani mamakin kennan nadauka katafi kenan bazan sake ganinkaba,
Girgiza kai yayi yace Akan wani dalili zan bar zan tafi bazan sake dawowaba?
Saboda!!!! Sawwama tafara magana sai kuma takasa qarasawa ta sunkuida kanta qasa,
Murmushi sadam yayi cikin tausayawa yace" zan dawo sawwama ai sonda nake miki ba qarya bane, akanme zan rabuda abunda nakeso dan wata qaddara ta fada miki?
Ashema soyayyata bata cikaba kenan.
Ashe ba son gaskiya nake mikiba,
sawwama ina sonkine tsakani da Allah soyayyarda nakeyi miki babu algus acikinta,
Dan wannan abun ya faru dake bazai rage dai-dai kwayar zarra cikin sonda nake mikiba,
Inaso kisani bazan ta6a rabuwa dakeba da yardar Allah zamu kasance atare,
Dagowa sawwama tayi ta dubeshi cikin rawar murya tace to idan kai ka yarda iyayenka fa?
Murmushi sadam yayi yace akanme zasu sani?
Ni zan aureki ba kowaba,
Wannan sirrin ni kadai ya shafa, babu ruwan kowa cikin wannan lamarin sawwama,
Wannan sirri nane ni dake zan rufa miki sirrinki
Kamar yanda zan rufe nawa sirrin kai koma fiyeda yanda zna rufe nawa sirrin, mahaifana da kowa bazan bari susan wannan zancenba saboda sirrinki sirrina ne, sirrinki yarufu awajena bazan bude ba har wani yaji,
Sunkuida kanta tayi qasa kwalla yanabin kan kumatunta ta tabbata sadam masoyin asaline,
Zaiyi wuya tasamu wanda yakeyi mata so irin wannan,
Sadam ne yaci gabada fadin sawwma nasan qaddara zatayi iya fadawa kan kowa bbu wanda yafi qarfinta,
Bazan iya gudun dan adam akan wata qaddara data fada masaba saboda nima banfi karfintaba akowani irin lokaci Allah zai iya jarabtata,
Nidai abunda nake buqata daga gareki kisoni sonda babu algus acikinsa,
Kisoni tskani da Allah
Kada kisoni dan wani abu kodan na nuna miki cewa inasonki cikin kowani rin hali kema kiji zaki sakamin da maidaomin da soyayya ba,
Inaso ya kasance kin soni saboda Allah yakasance kin soni saboda kasancewata ni bakowaba bakuma dan wani daliliba,
Idan so ya kafu dan wani dalili ba fataba mai zai faru ranarda akace babu wannan dalili?
Bayan gushewar dalilin da aka gina soyayya akansa shin soyayayr zataci gaba da yaduwa ko zata mutu,
Abu dayane zaka yishi wanda har abada bazakaga karshensa ba shine yin abu dan Allah,
Nidai ina sonki dan Allah sawwama, aduniya da kika gani babu wanda yake tsarawa kansa rayuwa komai kikaga yafaru daga Allah ne,
Babu wanda yake za6awa kansa rayuwa dan damuna za6in rayuwa akanmu da dayawa baki gansu a halinda suke cikiba,
Dago ido sawwama tayi tana dubansa kalamansa cike suke da hikima da sanin ya kamata,
Kalamansa sun shigi sawwama sosai, komai zaiyi yana aiki da hankalinsa wajan aikatashi hatta kalamansa suna kan mizani,
Cikin yanayin jin dadi sawwama tace nagode da muna qaunarka a gareni,
Allah yabani ikon mayar maka qaunarda kakemin,
Amin sadam ya amsa cikin jin dadi hakan ya nuna ta aminta dashi kennan."
Tad'i suka dan ta6a jefi-jefi saboda rashin sabo da juna,
Dare yadan farayi kafin sadam ya anqara miqewa yayi zumbur yana fadin natsaya hira dare yayi barina wuce, sawwama ji tayi kamar ta hanashi tafiya amma kunya ta hanata, agaugauce yayi mata sallama yatafi hankalinsa yayi gida baisan mai zai gayawa mummy ba yasan sai tayita fada, shikuma baison fadanta kokadan."
✔️ote
Comment
Share
Follow
To be continued
Zaynab Alabura
Advertisement
- In Serial18 Chapters
Esper Online: The 15 Thrones
Esper Online one of the worlds top VRMMORPG's is about to release its' first expansion, The 15 Thrones. Millions of players world wide eagerly await the expansion to the high fantasy completely emersive game! With new playable races, a release of in game gods, and a brand new Master AI to watch over the world it is expected to become one of the biggest virtual events of all time! But, something is wrong... Pre Expansion characters are missing. There appears to be only one server world wide, and most confusing of all... Players who log out don't log back in... ***Participant in the 2021 Writathon challenge!***
8 192 - In Serial21 Chapters
Persona Non Grata
After the events of Dr. Jose Rizal's second novel "El Filibusterismo", the story follows the tale of the former students Basilio and Isagani in the aftermath of the failed assassination plot against the most powerful governing political figures in the Delos Santos residence. Now a licensed doctor and a tenured businessman, Basilio and Isagani returns to the Philippines after their 10-year venture in Spain and in the United States to spearhead a large-scale project for the Spanish crown. For the first time in the history of the country, the Spanish government has allowed Indios to pioneer major public works, and the Filipinos, seeing this as major milestone of their race, welcomed it cheering and with open arms. It was also during that same year when the new Captain-General was appointed to the Philippines following the scandal involving the outgoing Captain-General, who sent an entire battalion of Indio conscripts to be deliberately slaughtered by a gang of tulisanes led by a man going by the name 'Matanglawin' (Falcon-eye). Leonardo Montes, the incoming Captain-General, was both feared and loved by his subjects. A close friend of the king and reputed for upholding honor, discipline and goodwill among his subjects, he won the confidence of the Cortes and of the Filipino people when political unrest arose during the tenure of his predecessor when he represented the Philippines in the high courts and won the case. However, Montes, now at the early days of his tenure, is faced with a huge and pressing problem: the widespread opium trade in the Philippines. Chinese immigration to the Philippines has increased at an exponential rate since his predecessor came to power and so is the circulation of the substance within the country. And to make matters worse, strange cases of killings and abductions began to terrorize the country, with the motives of the culprit unknown...
8 221 - In Serial38 Chapters
through the screen - kim namjoon
pinkboii: hi! (:minni94: who is this?? pinkboii: ur new obsessionminni94: im blocking you, white boy.[ started october 18th, 2015 ][ ended april 2nd, 2016 ]
8 148 - In Serial25 Chapters
IM JUST THE BILLIONAIREs WIFE
If it wasn't hurt it wasn't love, loving means hurting but a true love can bring all of the pieces. Love means a lot it can change us but it can also break us.Do people can stay together without love what if you will force to be with someone who you doesn't well know. The worst part is you learn to realize that your not only force into a loveless marriage but you also need to deal with the emotionless man not to mention that his eyes, his face all about him declares and show power and coldness. How long can you able to stand and remain firm when the man you need to face every day looks so intimidating, a jaw dropping man who don't give any justice in every word you can possibly describe him. This is the story of a woman who lives her life to the fullest she's enjoying her life even though everything seems too difficult for her to survive and be alive. She always believe that she needs to be strong to be able to survive. But then unexpected things happen that test her so much. How long can she remain strong and face everything. What if she is going to marry a womanizer billionaire that trap her into a loveless marriage. How can she remain strong when the billionaire broke her and got her a night that change her life. What if the woman he once loved in the past returns, and her past hunts her a nightmare she hope did not happen along time ago. How can she remain strong along the way, is she going to run away or she will stay and tamed the man who dragged her into a new sophisticated life.This story will show us the ups and down of life in a darkest shade of life there is always a hidden light that embrace the soul. And how love can be able to change the person itself how far love conquer all.
8 153 - In Serial26 Chapters
To Escape a Possessive Mate
Nora hates it when werewolves and vampires make themselves known to the world. All she dreams about is escaping to a human community, when she gets chosen to be the mate of werewolf Vincent. Upon learning of her desires to run away, Vincent does everything to keep Nora by his side.
8 194 - In Serial46 Chapters
kill my mind - m. atsumu
𝐚𝐧𝐝 𝐢 𝐝𝐨𝐧'𝐭 𝐤𝐧𝐨𝐰 𝐰𝐡𝐚𝐭 𝐢'𝐝 𝐝𝐨 𝐰𝐢𝐭𝐡𝐨𝐮𝐭 𝐲𝐨𝐮 𝐧𝐨𝐰 ↳ in which something fake turns real
8 125

