《ƘADDARAR RAYUWA》Q page 22
Advertisement
**
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa (z3iiyyb3rw3r)
#Follow me on
Page 22
Sadam yayiwa sawwama alqawarin akan zaiyi karatu iyakar iyawarsa har sai yaga yayi qoqari kodan ya sanyata cikin farin ciki,
Sun fara exam Alhamdulillah komai yana zuwa masa dasauki barinma yanda mutanenda yake tareda su suka dage sosai da addu'a akan jarabawarsa, addu'a baga mummy baga sawwama ba kowa yana nasa qoqarin,
Mummy kuwa har tashin dare takeyi itakuwa sawwama bawai tasaba da tashin dare bane dan bata ta6a yiba,
Hakan yasa cikin sallolinta na ranar take zabga masa addu'a,
Sa'i-sa'i yanzu sadam yake zuwa wajan sawwama kamar yanda ta buqata yazauna yayi karatu,
Shi kansa bahaka yasoba kawai dai yabi yanda tasoone itama anata wajan bawai hakan tasoba kawai tasan cewa idan ta yaci gabada zuwa kullum zai takurane."
———-
Yau satinsu sadam daya da fara exam amma zuciyarsa takasa sama masa ntsuwa gameda karatun sawwama kamar yanda yace saiya gama exam, amma yanzu yana ganin ra'ayinsa yafara canjawa baiga amfanin jira har sai yagama ba,
Saboda bazai juri ganinta cikin halin rashin sani ba, dama ace karatun bokone amma karatun islama aida matsala ayau idan tamutu wajan Allah batada wani uzuri hakan yasa ya yanke shawarar tun tu6arta da maganar fara zuwa makaranta idan yaso daga baya bayan yagama exam sai ayi maganar makarantar boko,
Akwai interval na kwana biyu tsakanin exam dinsu hakan yasa ya yanke shawarar zuwa wajanta yau da dare idan Allah ya kaimu,
Kamar yanda yasaba zuwa bayan ya fita sallan isha'i kai tsaye kawai ya wuce,
Wajanta bayan ya isa ya aika aka kirawota, sawwama dama ta sanya rai da zuwansa shiyasa bata wani jimaba tafito domin tagama shiryawa tsaff,
Tafito cikin tafiyarta na nutsuwa kamar wacce batason taka qasar, yanayin yanda take tafiya a nutse yasanya idan tana tafiya ko qaran takun tafiyanta ba'aji, sadam idonsa yana kan qofar alokacinda idonsa ya sauka akanta ya sauqarda ijiyar zuciya yana mai qara godiya a Allah cikin ransa nutsuwar sawwama kadai ta cancanji asota,
tabbas ganin sawwama kadai kan sanya masa kwanciyar hankali yakanji sanyi yana ratsa duk wani gabban jikinsa aduk lokacinda yayi arba da ita,
Lumshe idanuwa yayi ahankali yabudesu akanta wani irin soyayayrtane take fisgarsa,
Itama sawwama anata wajan hakanne,
Farin ciki ta tsinci kanta aciki alokacinda tadaura idanunta akan fuskarsa mai cikeda dakamala,
Ga wani irin kamshinsa wanda akoda yaushe kafin ka qarasa wajanda yake kamshinsa yake qaraso maka, takan rasa wasu irin turare haka yake amfani dasu wanda kamshinsu ke saukarda nutsuwa da farin ciki,
Qarasawa tayi da murmushi akan fuskarta ta nemi waje tazauna wadan wani kututturen iceh take qofar gidansu,
Advertisement
Cikin muryarta mai sanyi da dadin sauraro ta gaidashi cikin kadabi,
Amsawa yayi yana binta da kallo sakamakon hasken farin wata ya haske gabaki daya ilahirin wajan,
Numfashi yasauke ahankali sannan ya kauda idansa daga kallonta sai alokacin sawwama tasamu sukuni aduk lokacinda ya tsareta da ido alokacin take rasa duk wani kuzarinta, cikin nutsuwa tabude bakinta tace" ya jarabawar?
Murmushi yayi aduk lokacinda sautin muryarta da duki dodon kunnunwansa yakanji dadi, har yanzu baiji murya mai dad'in nataba,
Koda baka santaba muryarta kadai ya isa yasa kajuya ka kalleta,
Idan tayi magana sau daya tabbas zakaso taqara bude baki tayi wata maganar domin dadin sautin muryarta,
Kuma da yadda take magana cikin nutsuwa,
Sadam ya lula cikin tunanin sawwama bai samu damar bata amsar tambayartaba,
Turo dan bakinta tayi tana fadin yaya sadam shine ina magana zakayi shiru ka rabu dani?
Kwayar idonsa ya sauke akanta yana binta da wani irin kallo ita kanta yau tarasa wani irin kallo haka sadam keyi mata mai kashe mata duk wani kuzarinta,
Me kikece? Ya tambaya cikin sanyin murya,
Har lokacin bai daga idanuwansa daga kantaba,
Kanta yana qasa tace ina tambayrka yaya jarabawa?
Alhamdulillah ya amsa atakaice,
Gyaran murya sadam yayi alamun yana sonyin magana hakanne yasan yata d'agowa cikin rashin sa'a abunda take gudun yafaru wato idanuwansu ya sarqe waje daya,
Wani irin faduwa gabanta yafarayi hakan yasa tayi
Saurin sauke idonta qasa dan bazata juri kallon kwayar idanuwansa ba,
Wani irin abu sawwama ke gani cikin kwayar idonsa
Mai daukar hankali tabbas ta tabbada akwai wani sinadari cikin kwayar idonsa kokuma zallan kyawunsu ke kwasarta batada wannan amsar,
Ajiyr zuciya sadam ya sauke cikin nutsuwa yafara magana,
Sawwama zamanki haka bayamin dadi, banason ganinki haka baki zuwa makaranta baki zuwa boko baki zuwa islamiya nayanke shawarar zaki koma islmiya awannan satin,
Dagowa tayi ta dubeshi tace da wani lokaci kenan,
Koma da wani lokacine sawwama ke zaki za6i wacce kikeso idanma ta darene kikeso saiki koma amma zamanki haka sam baiyiba,
Shiru sawwama tayi tana tunani ta tabbata babanta bazai barta tayi islamiya da dare ba garama ace da yamma to amma idan yamma ne sana'arta fa?
Kinyi shiru sawwama ko bakison makarantar ne?
Girgiza kai sawwama tayi tace A'a inaso ma amma dai baba bazai barni zuwa makarantar dare ba,
Shiru sadam yayi yasan dalilin da zaisa baba ya hanata zuwa makaranta da daddare bazai wuce yanada nasaba da abunda ya faruba.
Kuma har in dai hakane yanada gaskiya,
Zuwa yamma fa? Sadam ya jefo mata tambaya,
Kuma ya tsareta da ido,
Zuwa yamma ai ina sana'a,
Wannan ba uzuri bane sawwama sana'a ai bazata hana neman ilimi ba,
Advertisement
Abunda nakeso dake shine ki ajiye sana'ar yamma lokacin makarantar bazai wuce 2hours ba 4-6 idan kika dawo sai kiyi,
Kai ta gyada masa alamun gamsuwa da maganarsa dan batajin zata iyayen musu dashi wani irin kima take ganinsa da ita,
Murmushi yayi hadeda fadin nagode, kanta ta sunkuya qasa batareda tace komaiba,
Miqewa yayi zai tafi yace tayi masa magana da baba sawwama bataso tafiyarsa awannan lokacinba amma babu yanda ta iya haka ta miqe ta sanarwa baba yana magana dashi,
Koda yazo maganar makarantarta yayiwa baba, baba bai wani jaa zancenba ya amince sadam yayi masa godiya kamar wanda shine za'a sanya a makarantar,
Bayan baba yakoma sawwama tafito sukayi sallama yawuce,
Koda baba yashiga ciki ya shaidawa mama yanzu sukayi dashi mama ma taji dadi,
Baba yace yaron yayi tunani mai kyau in sha Allah wannan satin zan fara neman islamiyar wacce muke dan kusa da ita,
Sawwama ne tace mama maganar sana'atafa ko halima zata ringa kamawa kafin nadawo?
Eh hakanma yayi cewar mama,
Halima dai batayi magana bane amma itama har cikin ranta tanason tashiga islamiya amma tunaninta ita kanta sawwamar kudin biya mata sai andage balle aka hada da ita, tunanun hakanda tayi ya sanyata tayi shiru bata fadi akan itama tanasoba."
Washe gari sadam yafita nemawa sawwama islamiya baisha wahalaba yasamu kusa dasu dan tsallaken titine kawai tsakaninsu dasu sawwaman,
Islamiyar tanada kyau sosai amma sai dai school fees yakai wajan 3k registration dinta kuwa yakai 7k ahaka sadam yayi duk wani abunda ya kamata bai koma gidaba sanda ya dinka mata uniform dakuma hijabai saboda tunda yakeda ita da hijab biyu kawai yake kallonta iya rayuwarsa, kuma ahakanma duka sun kode abunda bai saniba dayanma na bokon tane dayake tadaina zuwa shine take amfani da hijab dinta,
Sadam bai yarda yashiga gida da kayanba saboda baida amsar tambayarda mummy zatayi masa,
Sai bayan ya fita sallar isha'i yabiya yakar6i kayan wajanda yabada ajiya,"
Koda ya isa yasamu sawwama tagama tashiga ciki dan haka ya aika aka kirawota,
Bayan sun gaisa ya bata kayan dan bawani dadewa zaiyiba saboda yanada exam gobe da sassafe, kuma gabaki daya yau bai samu yayi karatu ba,
Yayi mata kwatancen school din sannan ya shaida mata akan gobe sufara zuwa sauran abunda yarage bashida yawa da zarar sunje za'a kaisu ajine kawai,
Ganin yana sauri ya sanya bata tambayeshi itadawa ba godiya tayi masa sosai yayi mata sallama yatafi,
Koda tashiga mama taganta da kaya sai tahau fada, akanme yasa zata kar6i kayansa, babane ya dakatar da ita yace baki kar6i kayan kin bude kin ganiba kika hau masifa, saannan ina laifi dan sawwama ta kar6i kayansa aiba ita ta rokeshiba,
Matso nan ya umarce sawwama matsowa tayi ta miqa masa kayan baba yakar6a yabude, kayan islamiya ne kala biyu aciki sai hijabai guda 5 dogaya har qasa,
Sai takardun rejister,
Miqa mata takardan baba yayi sawwama ta amsa ta karanta sai yanzu tagane mai yake nufi dayace gobe sufara zuwa,
Itada halima yayi musu register, uniform dinma na mutum biyune,
Miqawa halima tayi tana fadin hardake yayi mana register tsalle halima ta daka tana murna,
Baba ne yace toh madallah abu yayi kyau Allah yayi masa albarka su duka suka amsa da amin,
Mama ma tace abu yayi kyau gaskiya Allah ya saka masa da gidan aljanna,
Cikin jin dadin addu'ar mama sawwama ta amsa,
Kayan makarantar suka gwada dukansu kayan sunyi musu yawa amma bawai sosaiba hijabin kuwa har qasa yake shara, haka itama na halima dake bambamcin tsayinsu itada sawwama kadanne,
Sauran hijab dinma duka har qasa suka kaima sawwma zasu yadika masu kyau,
Aranar sadam yasha addu'a awajan yan gidannan barinma sawwama wacce dama akwaita dason hijabai rashine kawai yasa tayi hakuri."
Washe gari tun 3:30 suka shirya zuwa islamiya saida sukayi sallah sannan suka kama hanya bayan sun isa akayi musu duk wani abunda yadace sannan aka kaisu aji, ajinsu daya da halima har seat dinma dai nasu dayane,
Sai 6 aka tashi daga islamiyan suka kamo hanyar gida,
Tun daga nesa sawwama take ganin kamar sadam tsaye jikin mashin dinsa tana zuwa kusa kuwa taga shi dinne,
Murmushi ta sakar masa shima ya maida mata qarasawa wajansa tayi tana fadin yaya sadam ina wuni?
Lafiya qlau ya karatun Alhamdulillah ta amsa, baqaramin kyau tayi masa cikin uniform dinba dama kawai yabi hanyar makarantarne dan yaganta cikin uniform,
Yaya jarabawar ta tambaya,
Numfashi ya sauke sannan yace jarabawa Alhamdulillah sai kewarki dake addabata,
Hannu biyu sawwama tasanya ta rufe fuskarta tana dariya, murmushi yayi mai sauti yace kiwuce gida kinga ni dama na biyone kawai naganki kuma na ganki gida zan wuce,
Batayi maganaba halima ta qaraso tana gaidashi ya amsa cikin sakin fuska yana fadin yan makaranta ya karatun Alhamdulillah halima ta amsa sannan tayi masa godiya sosai,
Sawwama tace yawwa babama yace nayi maka godiya,
Kai kawai sadam ya daga mata sannan yace tawuce gida,
Tafiya tayi tana juyowa tana kallonsa yana sakar mata murmushi daga nan yatada mashin dinsa yayi gida suma suka wuce gida."
Gaskiya yawan vote da viewers na wattpad sunyi kadan shiyasa yanzu zan ringa bari sai bayan kwana bibbiyu ina yin update gaskiya viewers da vote sunyi kadan."
✔️ote
Comment
Share
Follow
To be continued
Zaynab Alabura
Advertisement
- In Serial133 Chapters
Rise of Demon King
By the stroke of fate, Ren finds himself in a world of demons, Kalkan kingdom. Damned by his circumstances and his human-like appearance, Ren struggles to survive in a world in which strong rule the weak. The Selection of the next king of the Kalkan kingdom is about to begin, bringing along many conflicts that make life much harder to endure, but unwilling to give up, Ren is determined to survive and prosper. Buy Volume 1: https://www.royalroad.com/amazon/B07JNJKSCH Buy Volume 2: https://www.royalroad.com/amazon/B07JMYJW3B Donate Via PayPal- paypal.me/kuanyshbekovsayan I will post at least a chapter per month My name is Sayan Kuanyshbekov, and I am the author of this book.
8 370 - In Serial11 Chapters
DARK EDEN: The Death God's Origin
Year 3077. Humanity had perfected the Virtual Reality Simulator, a system that allows individuals to experience alternative universes of video games in real-time. Unknown to humankind, catastrophe strikes and the Simulator central gets hijacked by an unknown man, with plans to establish a world modelled after a video game: Dark Eden Online (DEO). "To you, those who have lost all hope. To you, those that seek to live a better life. To you, those that humanity itself had abandoned…now is the chance to change, to start over. What is it that you desire most? Is it money, fame, love, friendship, or is it something like…revenge? Or perhaps something even greater? In this new world, you can become even God. Now, the 7th hour of the 7th day in 7th month of 3077 has arrived. Ladies and gentlemen, I welcome you to the world of Dark Eden."----------------------------------------------------------------------------------------------------------------------------------------------Status: OngoingBrought to you by Team Lux:Story- Hikaru SeishinEditor- Yoshii OkanaCorrespondent- Sachiko
8 94 - In Serial14 Chapters
The American Heist
If you could make one wish, what would it be? In this story our main protagonist Jack, receives an anonymous tip that a Black poker chip that grants the power to make a wish is being stored in the most secured place in the world, Fort Knox's Gold Bullion. After realizing what he can do, Jack decides he'll pull off the impossible. But Jack knows he can't do it alone.
8 406 - In Serial10 Chapters
MaNan FS - Love + Arrogance✅
What happens when a girl is pampered beyond limits...???What happens when she turns out a bit arrogant...??Well, a bit would be fine but what if she takes advantage of that pampering of the only brother she has.Meet Nandini Murthy, arrogant sister of Abhimanyu Murthy who never says no to his daughter like sister.Peep in to know how this pampering and his so called bro love turned middle class, simple, down to earth person to a monster.Can Abhi save his sister from the monster whom she herself wished to have him in her life...???A LITTLE BIT DARK...SO NO BASHING PLZ...
8 93 - In Serial14 Chapters
Whispers (Draco Malfoy x reader)
After bumping into him in the train, Y/n L/n heard Draco Malfoy whispering about her to Blaise Zabini.Doesn't go by a certain year, you can imagine it as any year you want. WARNINGS :-extremely cliche and predictable -keep in mind that I wrote this when my writing skills were not as developed
8 133 - In Serial37 Chapters
The Contract ✔
"I know you only care, not because you love me, but because you love what is in me." She said and turned away, afraid of what he was going to say, how he was going to reject her.He hushed her and pulled her to him so they was no space in between, and placed his lips on hers. He pulled away and looked at her, a whirlwind of emotions in his eyes, and then spoke again. "At first, I only cared about the baby, not you. But now I want you. Because I've fallen in love with all of you. It's no longer my baby; it's now our baby."Then she pulled him back to her, to finish what he started. ...Tobi Ademi, the third richest man in Nigeria has everything an average guy wants: wealth, fame and of course, an endless supply of women.A total control freak, he prefers to be in charge of everything; even the way he gets an heir to his empire. He decides to hire beautiful but uncontrollable, Abena Omotosho, or rather, he rents her womb. He gradually moves from his daily routine of life, to something much more worthwhile. Something called, 'living in the moment'.And then he realizes, that he can't control everything, especially not love, because once love chooses you, there are only three words for you: out of control....It's a contract: simply business and no strings attached, but no business deal is that easy, and especially not this one....Highest Rank Achieved : #220 in Romance...> Blessed and Black Special Awards Winner 2017
8 167

