《ƘADDARAR RAYUWA》Q page 23
Advertisement
**
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa (z3iiyyb3rw3r)
#Follow me on
Page 23
Sawwama ta maida hankali sosai wajan koyan abunda tajeyi saboda taga sadam nason tayi karatu ita kuma har in dai sadam yana son abu har indai bai sa6awa shari'a ba koda ita bataso zata daure tayi,
Shima sadam nasa hankalin yana wajan exam dinsa haka dai lokaci-lokaci yakan shigo ya dubata."
Sati uku curr su sadam sukayi suna exam sannan suka gama,
Sanda sadam yayi kwana biyu curr agida yana hutu bai zuwa ko ina,
Hayaniya mummy tahana qannensa yi acikin gida saboda karsu takura shi yagama exam yana buqatar hutu,
Mummy lailaya sadam takeyi tanaji dashi sosai,
Bayan sadam yagama hutunsa sai kuma yafara fitan dare zuwa wajan sawwama,
Anan suka fara samun matsala da mummy dan nunawa tayi batasan zancenba bazai ringa fitan dareba
Wai cewarta idan abaya yace karatu yake fit yanzu fa?
Yawan banza ita kuma bazata daukaba,
Sadam yashiga damuwa sosai lokutan dayake exam daurewa yakeyi yake tsallake kwanaki baije wajan sawwama ba gashi yanzu yagama exam lokacinda yake kallon lokacin zuwa wajan sawwama akai-akai yazo amma mummy tana neman hanawa,
Saida dady yashiga wannan lamarin kafin sadam yasamu damar fita tatass yayiwa mummy yace aishi sadam ba yaro bane bakuma mace bace da zata ringa cewa bai isa yafita ba sannan kuma yace mata aiy dade da bawa sadam damar fita zuwa 9:30 yadawo gida dan haka yasoke wannan zance baiso yaqaraji tayi zance akan fita har in dai ba 9:30 yawuce awaje ba,
Mummy dai dady yafi qarfinta kuma tanajin maganarsa sosai haka babu yanda ta iya tana kallo sadam ya shirya yafita abunsa."
Sanda ya biya bookshop ya siyo littafai wanda dama suna rubuce jikin form na islamiya akan zasu siya sannan yakama hanyar gidansu sawwama."
Sadam wajan sawwama yawuce kai tsaye daya isa yadade awaje babu wanda zai aika ya kirawota, sai alokacin yakejin haushin rashin mallaka mata waya da baiyina, yana tsaye saiga baba yazo zai shiga gida yana tura wheelbarrow dinsa,
Saurin durqusawa sadam yayi yana gaidashi baba ya amsa fuska asake yana fadin A'a sadam kaine atsaye nan?
Maman nawa bata fito bane?
Sosa kai sadam yayi yace wallhy baba ban samu wanda zai kirawomun ita bane,
Ashha ashha baba yafadi sannan yace idan irin haka tafaru daga yanzu kashiga da kanka ka kirawota gidan yanzu aiba baqonka bane,
Advertisement
Shiru sadam yyi yana tunanin ta yanda zai fara shiga gidan,
Babane yace to madallah anyi dawainiya da mamana harda qanwarta kuma Allah yayi albarka amma da baka takura kanka bama sadam da zan sanyata,
Kan sadam yana qasa yace babu komai baba,
Gyada kai baba yayi sannan yace" toh shikenan Allah yayi albarka ni barina qarasa ciki sai inyi mata magana,
Godiya sadam yayiwa baba, sai baba yatura barrow dinsa yayi ciki,
Sadam yabishi da kallon tausayawa, ayanda ya fahimta baba baida wasu shekaru matashine sai kuma rashi da wahala da sukayi masa yawa dan a kintacensa baba bazai wuce shekaru talatin da biyarba idan ya daura a da biyar to bada yawaba,
Azamaninnan wasu kamarsa ma samarine basuyi auren fari ba,
Kana kallonsa zakaga cikarsa ta fulani cikakken ba fillatani ne dogo baida qiba,
Matashi amma wahala ya sanya yadawo kamar wani wanda yafi shekarunsa,
Matasa irinsa yanzu sukeji da samar taka da jini ajika,
Gabaki daya tausayin baba ya rufeshi yanaji cikin ransa da yanada hanya daya taimaka masa yafita a halin kunci dayake ciki,
Muryarta mai sanyi da dadin sauroro mai sanya nutsuwace ta katseshi daga tunanin daya fada,
Ajiyar zuciya ya sauke alokacinda ya daura idanuwansa akanta,
Sam baiji takun tafiyartaba bai sanda isowartaba saida yaji sallamarta,
Murmushi ya sakar mata hadeda amsa sallamar,
Zaunawa tayi agefe tana gaidashi ya ama yana tambayarta ya makaranta ta amsa masa da fadin Alhamdulillah sannan ta daura da tata tambayar da fadin ya jarabawa?
Alhamdulillah jarabawa angama sai jiran sakamako,
Allah yasa muga alkhairi sawwama tafadi kanta yana qasa,
Samada minti biyar suka dauka babu wanda yace komai sawwama ita kanta yana qasa,
Shikuma sadam ya kafeta da ido yana kallonta tayi masa kyau sosai,
Cikin hijabanda yasiyo mata ta sanya guda daya hijabin ya sutura jikinta gabaki daya ya rufe mata ko'ina,
Fuskarta kawai ta tafin hannuntane awaje,
Sawwama jikinta yabada ita yake kallo hakan yasa takasa daga idonsa saboda tasan tana dagawa idonta sai sauka akan nasa,
Ita kuma nauyinsa takeji sosai.
Tsarguwa tafara yi jikinta yafara rawa ganin haka yasanya ya sake murmushi mai sauti kadan ya kauda kansa gefe yana fadin waini haryanzu tsorona kikeji ne?
Shiru sawwama tayi batace komaiba itadai iya saninta ba tsoronsa takejiba nauyinsa takeji sosai,
Ganin tayi shiru taqi amsawa ya sanyashi kauda zancen da fadin yaya karatun akwai dadi kuwa?
Nodding head dinta tayi tace uhmm akwai dadi,
Advertisement
Dubanta yayi yace lallai toh ina sauraro mai dame kika koya cikin 2weeks?
Shiru tayi kamar mai tunani nan kuma tafara jero masa abubuwanda ta koya,
Mamaki sosai sadam yasha dan baiyi zaton cikin 2weeks zata dauki wad'annan abubuwanba, wajan qur'anine ma yaji tadanyi baya da alamu ba sosai ake koya musu qur'an a ismaliyar ba, sunfi qarfi ta wajan littafai,
Lallai ta maida hankalinta sosai kan karatunta domin ko ayanzu taqaru dayawa,
Jijjiga kai yayi yace ga books dinda ake koya muku saiki qara maida hankaki,
Kar6a sawwama tayi hadeda yimasa godiya,
Sadam bai jima sosai ba yayi mata sallama saboda kada ya wuce lokacinda dady ya sanya masa,
Yayi mata sallama yawuce gida, saida taga tafiyarsa sannan tajuya tashiga gida,
Sanda ta zauna sannan ta miqawa halima littafan tana fadin debi naki ki zubamin nawa adaki,
Murna halima tafara tana fadin kinga dama anata magana akan musaya,
Mama datake zaune tace madallah dama naji kun fadawa babanku bai samu kudi bane daya siya muku gashi sadam ya siyo to Allah yayi albarka,
Amin su duka suka amsa."
————-
Washe gari sadam da zaije wajan sawwama sanda yabiyo ya siyo qur'ani guda biyu masu kyau sosai yakaiwa sawwama,
Qur'an din sunyi mata kyau sosai tayi godiya, aranar yafara daura mata karatu saboda yaga karatun Qur'anainta yaja baya,
Haka tabawa halima daya ta riqe daya,
Haka sadam kullum yazo saiya qarawa sawwama karatu kuma tana daukan sosai,
Tarteel yake qara mata da qur'an idan yayi saita karanta yana koya mata da tajweed,
A kullum yazo saiya sanyata tafara yimasa karatu saboda dadin muryarta kafin daga baya ya daura mata,
Sawwama bata dauki karatunta da wasa ba da qarfinta da dage tanason koyon karatu, Allah saiya dubi zuciyarta yasa take ganewa sosai fiyeda tunanin mutum,
Kuma shima sadam tadage sosai,
Najeeb babu yanda baiyi da sadam ba akan yakaishi yaga sawwama ba amma fir yaqi,
Haka koda sunzo siyan awara ranarda babu makaranta sadam baya karasawa balle har najeeb ya fahimci wani abun."
———
Sadam da sawwama soyayyarda take tsakaninsu tayi qarfi sosai shaquwace mai qarfin gaske atsakaninsu,
Soyayya sukeyi mai cikeda tsafta bbu algus acikinta,
Ana haka result dinsu sadam yafito mummy najin labarin result yafito hankalinta duk yabi yatshi shikanma sadam bai wani damuba amma haka mummy tabi ta daga hankalinta,
Aranar sanda ta sanya yaje yaduba result dinsa,
Sadam yayi mugun qoqari a result dinsa dan bai ta6a irin wannan qoqarin ba kaff department dinsu babu wanda yakaishi cin result,
Sakamkonsa yayi kyau sosai, sadam yasamu kansa cikin farin ciki baiyi qasa a guiwaba ya nufi gida,
Mummy dataga result ina ka saka ina ka aje da sadam yanda kasan zata maidashi ciki albarka kuwa aranar yashata dady yana office amma haka sanda mummy takirashi tadawo gida,
Shima dady nasa wajan ba qaramin murna yayiba,
Sai wannan lokaci hankalin mummy ya kwanta saboda taga sadam dinta yayi qoqari sosai,
Tasan cewa sadam yana karatu sosai,
Abunda mummy bata saniba sadam baya wani karatun daga hankali shidai kawai Allah yasa yanada kwakwalwar fahimtar karatunne,
Mummy har wajan aikj tajeda result din sadam tanunawa frnds dinta,
Adangi kuwa sai kira takeyi tana sanarwa mutane result din yan uwa da abokan arziki,
Babban yayanta takira ta shaida masa result din,
Bayan tagaya masa yayi murna sosai sannan yace tazo gida tanuna masa,
Da yamma mummy ta shirya taje gidansa,
Commisioner ne yayan mummy,
koda mummy ta isa bayan sun gaisa da matansa ta shiga palour wajansa,
Yaga result din sadam yayi murna sosai sannan yace dama inson yin magana dake gameda zancen sadam yanzu saura how many years yagama karatunsa?
Cikin fara'a mummy tace' yanzu kennan zasu shiga final year masha Allah yafadi sannna yace naga cewa shine danki babba shiyasa nayanke shawarar hadashi da abida diyata saboda qarin zumunci,
Dariyarda take fuskar mummy cakk ta dauke, wani iri taji harga Allah bazata iya barin sadam yayi aure kwana kusa ba,
Dan har frnds dinta sunayi mata magana akan ko zai nemi ya'yansu amma ta qirmishe idonta tace batasan zanceba,
Ina sauraronki me kikace akan hakan?
Yaqenda bai kai zuciba mummy tayi sannan tace yayaa kasan sadam qaramin yarone kuma karatun yanzu yafarshi waida inaso yadanyi nisa akaratune,
Dududi yanzu baifi 24yrs ba da dai za'a bari yadan qara karatu da shekaru ai abun zaifi,
Tunda naga abidanma yanzu itama karatu takeyi,
Dududu itama nawa take bazata wuce 22yrs ba, ai duk abun na gidane abida ai 'ya tace amma sudai yi karatun tukunna su mallaki hankakin kansu,
Jijjiga kai yayanta yayi sannan yace to shikenan zadai muga yanda za'ayi,
Toh kawai mummy tace jiki asanyaye tayi masa sallama tatafi ita dai komai zai faru bazata yarda tabar sadam yayi aure yanzuba."
———-
✔️ote
Share
Comment
Follow
To be continued
Zaynab Alabura
Advertisement
- End555 Chapters
Omniscient Reader
Only I know the end of this world. One day our MC finds himself stuck in the world of his favorite webnovel. What does he do to survive? It is a world struck by catastrophe and danger all around. His edge? He knows the plot of the story to end. Because he was the sole reader that stuck with it. Read his story to see how he survives!
8 400 - In Serial42 Chapters
I Am Not Chaotic Evil
Participant in the Royal Road Writathon challenge. Carnage, arson, and wanton destruction permeate the mind of Jeremy Fjord. However, Jeremy is a rebel — and voices in his head will not dictate how he lives his life. Follow the adventures and misadventures of a simple necromancer wizard as he struggles against clerics, paladins, and the forces of good to attain his capitalist dreams. Reaper image taken from https://commons.wikimedia.org/wiki/File:The_death.svg under Creative Commons Attribution 2.0 Generic license.
8 245 - In Serial102 Chapters
Empire of Souls
Gods? Magic? Fantasy? Nonsense. Ishmael never cared for any of those things. All that mattered was his work. The Tower of Babel. This would prove it to everyone... that gods do not exist. Until one day, it all came crashing down. His world destroyed, his life ended. Thrust into a world of magic, where gods exist. He will get his revenge. Rise, the 'Soul Eater', devourer of souls. Now will only be uploaded on Webnovel, Empire of Souls Cover art by Oracle of INKed Check here for a more clear picture: Soul Eater or Soul Eater
8 195 - In Serial6 Chapters
Making of Paradise
Fyi, for all that start reading this. I am currently rewriting this entire story and going to start the release of it when I have about 15 chapters ready. Expect it in like 2 weeks. As planet "Earth" has come of age, starting integration of the system. As planet "Earth" has come of age, starting mutation for non-human life forms. On January 1st, every living person saw these two messages pop up as blue screens in front of their eyes. Soon after, animals started mutating and becoming savage and attacking nearby humans. These mutated animals included but were not limited to; house-pets. rats & insects. Quickly, most of the technology stopped working and cities became wastelands. We follow a man named Ambros in this new, changed world as he releases his true personality.
8 192 - In Serial17 Chapters
The Demon King
Summoned to another world to bring the world some well deserved justice. Disclaimer: I do not own anything.
8 109 - In Serial15 Chapters
Study Tips
These study tips helped me. I hope it will help you guys too.
8 89

