《ƘADDARAR RAYUWA》QPage 28
Advertisement
**
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa (z3iiyyb3rw3r)
#Follow me on "
Page 28
Satinsu sadam biyu suna ibada suka dawo gida yayinda hankalinsa gabaki d'aya yayi wajan sawwama kayanda ya siya mata gabaki d'aya a bag din hannunsa ya ajiyesu bai yarda ya hada abubuwanda ya siya mata dana mummy ba saboda baisan yanda zata dauki lmarin ba,
Bayan sun isa gida hutun kwana daya kawai ya yi yatafi wajan sawwwama ba qaramin murna sawwama tayi da ganinsa ba shima haka ji yayi kamar wanda ya dauki tsawon lokaci batareda ya gantaba aaranar yakai wajan 10:00pm kafinanna yabar wajan sawwma koda tashiga gida sanda baba yayi mata fada sosai, shikam bayan ya koma gida kusan kowa ya shiga daki so babu wanda yasan da rashin dawowarsa,
Bayan sun dawo da 5days ya kawowa sawwama tsaraba sosai ya yi mata siyayya barinma abayas masu kyau sosai harda baba yakawowa jallabiya."
Sadam yaji dadin yanda ya samu sawwama ta maida hankali sosai akan karatunta yayi mamaki domin bayan tafiyarsa da kanta take ta qarawa kanta karatu,
Rayuwarsu tafiya takeyi a kullum qara sabo sukeyi soyayyarsu qara nisa takeyi duk wannan abunda akeyi har yau mummy bata fahimci halinda sadam yake ciki ba."
—————
Nabila tana kula da yarima sosai yanda ya dace sai dai ko kadan yaqi sakin jiki da ita duk yanda zatazo su zauna waje daya dashi tana zaunawa awjan zai tashi tana kula da maganinsa yanda ya kamata duk wani abunda mai martaba yakawo ayi masa bbu 6ata lokaci takeyinsa,
Da safe bayan ta kaiwa yarima abinci babu yanda batayi dashiba yaci ko kallon wajanda take yaqiyi,
Tsayawa tayi tana kallonsa yanda ya kauda kansa gefe, ta6e baki tayi dama tasan bawai zaici bane kawai dai takawo masa ne,
Wucewa tayi izuwa dakinta ta kwanta wani bacci ya dauketa gabaki daya agajiye take jinta, maganar gaskiya ita dai nabila bata saba aikin wahalaba saboda mahaifinta yanada kudi sosai ita dai kawai tanada zuciya mai kyau dakuma hali mai kyaune shiyasa da daura niyyar kulada yarima kuma tanada tausayi sosai,
Sai bayan tayi bacci tatashi sannan tafita izuwwa palour kamar yanda ta barshi haka ta sameshi bai tashi daga wajanda yake zauneba tausayinsa ya kamata, qare masa kallo tayi idan za'a fada maka bazaka ta6a yarda cewa yarima baida lafiya ba kamar yanda mutane suke fadi ciwon hauka, ita bataga wani haukanda yakeyiba, shidai kawai bai magana kuma koda magana kayi bazai ta6a nuna maka ya fahimci mai kace ba ga dukkan alamu kuma baya fahimtar ne sai dai yabi mutum da ido kawai, sai kuma ihu dayakeyi da daddare sa'i-sa'i zaunawa tayi kusa dashi ta dauki abincin takai bakinsa duk yanda tayi ya bude bakin amma firr yaqi,
Advertisement
Tana cikin lallashinsa yaci abincin taji sallamar umma sosai umma taji dadin ganin yanda nabila ta sanya kai tanata lallashinsa miqewa nabila tayi cikin girmamawa tana yiwa umma sannu da zuwa,
Zaunawa umma tayi tana murmushi tana kallonta tana fadin sannu nabila an kwana qlau?
Sunkuyarda kai qasa nabila tayi sannan tazauna aqasan carfet tana gaida umma, amsawa umma tayi cikin fara'a tana fadin sannu da aiki nabila Allah yabiyaki, qasa nabila tayi da kanta sannan tace amin a hankali,
Daukar abincin umman tayi tana fadin yana rigima koh?
Yaqi cin abinci ai haka yakeyi, murmushi nabila tayi ta sunkuida kanta qasa tace umma bayason cin abinci wata rana haka yake kwana baici komai ba,
Murmushi umma tayi tace kada ki damu zanna zuwa ina bashi dama sau daya yake cin abinci arana baya wuce haka sai ruwa,
Eban abincin tayi takai bakinsa a hankali ya bude bakin umma ta sanya masa,
Murmushi umma tayi ta sanya hannu ta share masa gefen bakinsa tana son yaronta sosai hka tana tausayin fiyeda kima,
Sanda tagama bashi sannan ta ajiye tabashi ruwa, nabila ta tsura musu ido cikin tausayi da kuma qaunarsu yanda taga umma na tafiyar dashi kamar wanda batason koda kudane ya ta6ashi ta lura umma nason yarima sosai so maras misaltuwa, son da take masa baya iya 6oyuwa,
Umma tadan dade sannan tayi musu sallama tatafi tanajin nabila ta qara kwanta mata arai,
Washe gari da safe nabila ta shirya taje gaida mai martaba bayan sun gaisa mai martaba yadubeta cikin kulawa yace ina bakida wata damuwa? girgiza kai nabila tayi tace babu komai,
Toh Allah ya miki albarka idan dai kinji da wani abu kada kiji komai ki sanar dani bazanso ki cutu ba,
Jijjiga kai tayi tace in sha Allah,
Daga nan tafita sashin umma,
Bayan sun gaisa umma tace nabila aida baki fito bama zan shigo zuwa jimawa kadan, kada kina fita kina barinshi shi kadai kinji? toh nabila ta amsa cikin ladabi umma tace yawwa Allah yamiki albarka maza tashi kije kutafi da ruma saita tayaki zama zuwa dare, idan kuma kinaso ta dawo sashinku da zama saina sanarda mai martaba saboda Zaman kadaici kada yayi miki yawa,
Murmushi nabila tayi tace aikuwa umma zanso haka saita dawo mu zauna,
Umma tace toh babu komai in sha Allah zan yiwa mai martaba magana,
Ruma datake jinsu cikin murna tace umma dama wallhy ya yarima kullum sai nayi mafarkinsa nima zan fiso nakoma can din."
Haka kuwa akayi da umma taje gaida mai martaba ta shaida masa buqatarta mai martaba baiqiba washe gari ruma takoma shashin da zama,
Advertisement
Da dare yayi taga nabila tashiga daki ta kwanta mai makon d'akin da yarima yake, ruma kamar zatayi shiru sai kuma takasa hakuri tace' anty nabila ba'a d'akin ya yarima zaki kwana ba?
Ba'a cika barinsa shi dayaba saboda cikin dare yana tashi,
Murmushin nabila tayi tace dafarko can nake kwana sai naga kamar ina takurashi saboda bai sakewa har in dai ina wajen shiyasa nadawo nan,
Jijji ga kai ruma tayi ta koma ta kwanta."
Da safe ruma ta shirya tafice zuwa school ba ita tadawo ba sai la'asar.
Haka dai rayuwa taci gaba da tafiya musu amma ko kadan yarima yaqi sabo da nabila fir ko abincin hannunta yaqi ci daga ummansa sai ummansa kadai yake kar6an abinci ko ruma ma sai lokaci-lokaci yake shan ruwan hannunta."
—————-
Bayan dawowar sadam da 1week an shiga satinda za'a koma school mummy ta siya mai mota kamar yanda ta fad'a dama cewa nata gift din sai shn dawo, baqaramin murma sadam yayiba,
Wash gari yakaiwa sawwama tagani, itama tayi murna tayi ta yiwa mummy addu'a sosai yaji dad'in addu'ar ta ga mahaifiyarsa,
Nisawa sadam yayi yana kallon sawwama nutsuwarta ke qara masa soyayyarta cikin zuciya, cikin kulawa sadam yace sawwmaty inaso zaki koma school saboda zamanki haka bawani amfani gareshi ba,
Sunkuida kai sawwma tayi tace ni bazanqi komawa school ba amma kafara tuntubar baba tukunna kaji mai zaice,
Nisawa yayi yace in sha Allah zan masa magana,
Sawwwama inaso kiyi karatu sosai mummyna tana son karatu sosai dalilin karatu ya sanya ta siyamin wannan motar sawwama ki daure kiyi karatu idan bakiyi karatu ba mummyna zata iya rabamu yayi maganar cikin karyewar zuciya,
Dasauri sawwama ta d'ago ta dubeshi cikin tashin hankali tace tarabamu kuma yaya sadam akan karatun? Lumshe ido yayi hadeda jijjiga kansa yace eh mummy nason karatu sosai fiyeda tunaninki,
Shiru sawwama tayi gabanta ya tsananta faduwa saboda bata kawo rabuwa tsakaninta da sadam saboda yanda ta sanyashi aranta,
Ganin yanda jikinta yayi sanyi yasa sadam ganin wautarsa na gaya mata wannan maganar lallashinta ya fara yi da fadin, ki kwatarda hankalinki sawwmaty in sha Allah bbu mai rabani dake idan bakiyi karatu ba nace kuma ni zan zauna dake ko ayaya ina sonki,
Bazan ta6a bari arabamu ba in sha Allah zamu kasance atare,
Qaqalan murmushi sawwama tayi amma hankalinta duk yabi yatashi."
Bayan ya tafi haka yabarta da tunanun wannan abun cikin ranta,
Haka takwana da tunanin washe gari da safe kafin baba yafita sawwama taje ta sameshi noqe-noqe tafarayi takasa fada masa, kallonta yayi gar zai fita sai kuma yaja ya tsaya yana fadin mamana akwai wata magana ne? Bakinki yanason cewa wani abun, sosa kai sawwama tayi takasa fadawa baba, sake baron yayi ya isa kusada ita yana fadin mamana lafiya kuwa? Wani abunne yafaru?
Girgiza kai sawwama tayi yace to menene mamana,
Kanta yana qasa tace baba dama inason komawa makaranta ne idanda hali idan kuma babu saina hakura babu komai,
Murmushi baba yayi jin kalamanta akowani irin zance takanyi amfani da kalaman nutsuwa da hankali,
Kijira idanna dawo mamana zamuyi magana in sha Allah komawarki makaranta bazata gagarba,
Godiya sawwama tayi masa sannan ta yi masa adawo lafiya."
Da sadam yazo ta shaida masa cewa baba ya amince yace zai nema mata makaranta wacce zatana zuwa,
Murmushin jin dadi sadam yayi yace shikenan baki jira na tambayeshi ba shine kika tambayeshi da kanki?
Tura baki sawwama tayi tace bakaine kace za'a rabamu ba shine na fada masa dakaina,
Murmushi sadam yayi yace ai nace miki bazan ta6a bari arabamu ba ko?
Qara tura baki sawwama tayi tace naji tsoro sosai,
Murmushi sadam yayi yana kallonta yace sawwamaty yaushe kika kamu sosai ne haka?
Rufe ido sawwama tayi tace nima bansaniba,
Murmushi sadam yayi kunyar sawwama tana burgeshi komai awajanta kunya ne,
Nisawa yayi yana qara jin sonta a furzarda iska yace akwai school a islamiyanku tayi miki?
Zaro ido sawwama tayi tace yaya sadam ta islamiyarmu fa makarantar kud'i ce,
Uhum nasani ai tayi miki?
Gyada kai sawwama tayi shikenan, kawai yace bai qara cewa komai ba."
Cikin qaramin lokaci yasamawa sawwama admission a ss1 amma a 3rd term ake ahaka aka bata admissin tafara zuwa,
Yayinda shikuma sadam suka koma school ya shiga shekararsa ta karshe,
Ahaka rayuwa take ta tafiya mawa sawwama da sadam cikin so da kaunar juna, ahaka su sawwama suka shiga SS2 shikuma sadam yana first semester d'insa na final year."
—————
Ina kuke masoyana masoyan rubutuna🥰 hajiyata kin karanta bibiyata akeyi? Toh Y'ar fari fa? Dakuma wanda nake rubutawa yanzu Qaddarar rayuwa? To yaya kikaji salon🥰😍 ya qayatar koh? hajiyata wadannan aiba komai bane somon ta6ine cikin shirinda nayi na nishadatar daku hajiyoyina manyan mata Ku biyoni cikin littafina na YARIMA FAYAD🥰 wannan littafin salonsa daban yake akwaia zazza6ar qauna🥰😍 ciki dana tanada muku, 200kacal zaki sameshi, ga dadi ga sauqi🥰 Don neman qarin bayani,
tuntubeni ta wannan no 08161146563,
Kokuma ki biya kudinki ta wannan accnt 0003075326 zainab m bawa JAIZ BANK.
Ku antayo daga ciki😊😌
Hajiyata kada ki bari abaki labari."
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
Advertisement
- In Serial12 Chapters
Henchman
Ignored. Written-off. Underestimated. Until a serendipitous accident shows Gus the secret of how supers get their powers. Will it be enough to help this inexperienced henchman survive? Marooned on a desert island with a malevolent force trying to thwart him at every turn, Gus must conquer each challenge he faces Can he prove to himself, along with everyone else, that he's more than anyone thought he could be? If he succeeds, history will be rewritten. If he fails... [participant in the Royal Road Writathon challenge]
8 112 - In Serial7 Chapters
The First Horseman
(Discontinued.) CJ is a 13 year old girl without many aspirations in life. She enjoys the simple things, like procrastinating on homework, reading crappy romance novels, or watching reality TV. But after one day, after innocently making honest money by selling test answers, she gets chased and trapped in the sewer. Then she gets nearly eaten by a tentacle monster and is thrown into an almost literal shit fest of monsters. She'll make it through, but she will be changed. In many ways. Updates whenever I finish a chapter.
8 184 - In Serial12 Chapters
Fall of the Seven Kings
Hunter’s hatred for the world begins when an order is given for him to be imprisoned by the church of his hometown. It’s been seven years.. Seven years of bottled up anger will not be stopped by rusty chains and horse whips. He will watch the society which others call a blessing burn to the ground. He will rip the six kings that rule the nation off their thrones.He will show them the wrath of the fallen king.. Aziya has always loved the world she lived in; the mystery, the adventure. All of it seemed more of a dream than reality, that is until she met the woman who showed her the horrors of the world. With her personal mantra “Help everyone even if they don't deserve it; Kindness will always be repaid.”, she urges herself to better the world and sets off on a journey in order to make the world a better place. The fate of our two protagonists collide as they get closer and closer towards their personal goals. Will death and pain rule the forgotten land of Alagadda or will hope and peace prevail and shield the oblivious citizens to which they call this land their home.
8 188 - In Serial40 Chapters
A series of Transmigrated Misadventures.
This is an original story about a sadistic and scheming human and his defective sometimes malfunctioning cube about how they travel to different worlds with different settings where they make people's lives miserable. Zhang Fei was anything but a normal person. He was a sadistic human who made the lives of his book characters quite miserable so when he died he was bounded to a system by The voice and entered the realm network. He got a second chance at life and could now practically make the character's lives a living hell but he soon found out that there is a downside to being a sadist as well. that's all folks , so the novel is a bit different from the normal system novels you read, the Main charachter isn't a good guy like in most novels, well he isnt a bad guy either, he is just a sadist. But the point is i tried to make the story as different as i could while still keeping the system/trnasmigration formula with it, so i don't know how you will interpret the story but i hope you still read it and enjoy it. i am not chinese so i might have butchered up the chinese names in the novel. and first time writing so if its a little bad please forgive me. And almost forgot any constructive criticism is appreciated. as it helps me know what i am doing right and what i am doing wrong and i have also posted the same story on wattapad.com. enjoy. Arc 1- [The Cube, The Sadist and The Villainess.] (COMPLETED) Arc 2-[The Lonely Island] (ONGOING) Writing in Quotation marks-"For dialogues of characters" Italic writing- For inner monologues and thoughts Bold writing in brackets- [For the dialogue of system]
8 150 - In Serial12 Chapters
My Sweet Omega (Shintodo)
(NO QUIRK AU)Hitoshi Shinsou an Alpha, befriends an Omega named Shoto Todoroki. He begins to get suspicious when all the time when Todoroki gets scared when Bakugou is around. He later finds out he's in a toxic and abusive relationship with the most powerful Alpha, Katsuki Bakugou. Will Hitoshi he able to claim his sweet Omega?⚠️Warning! Contains⚠️SmutCursing Abuse
8 181 - In Serial48 Chapters
Looed and Lost You
(I'm in the process of rewriting this book! The new version is called "Bubblegum and Blood Roses"! But please feel free to still read this one! The plots are different!)Even at a small age, Cansas Walker knew she was different. She was the little girl at school with a knife collection. Being the youngest in a family of hunters can be hard, especially when both your big sisters only fight with each other. But when Cansas starts making things happen an Archangel of the Lord saves them from the demons that mean to kill them. This Archangel stays with Cansas until she turns nine years old. He leaves breaking the little girl's heart, but her life went on. Everything seemed to be back to normal until the demon Quinn kills her mother and father. Both her big sisters go off on their own leaving Cansas in the care of their family friends, the Winchesters. They took care of her until she was old enough to go off on her own. Now at the age of twenty-one, Cansas finds herself on a hunt with the Winchester boys that brings her close to a certain Trickster. Cansas life seems to be spiraling downward as she learns the truth about herself, But with the looming threat of the apocalypse, she must be stronger than ever to take on the great pain that comes with loving and losing an Angel of the Lord. -I don't own anything except my OCs. -Seasons 2-5 with some other characters from later seasons-Character may be a mary sue but she is my mary sue
8 119

