《ƘADDARAR RAYUWA》K page 32
Advertisement
**
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa (z3iiyyb3rw3r)
#Follow me on "
Page 32
Da fara'a baba ya ƙarasa wajan yana faɗin A'a yaya zakari kaine agidan namu? Aida kayimun aike sai nazo basai kazo ba, da fara'a yaya zakari yace A'a zuwanne ai ya kama shi yasa kaganni niɗinne yakamata inzo ba kaiba, baba yace toh Allah yasa dai lafiya yaya? yaya zakari yace Ahh lafiyace ta kawoni wallhy haɗeda ɗumbin alkairi, baba yace toh alhamdulillahi madallah abu yayi kyau,
Gaisawa sukayi baba ya tambayi ya iyali yaya zakari yace sunanan lafiya to madallah haka akeso ai baba ya amsa,
miƙewa baba yayi yace barina shiga ciki na dauko tabarma yana faɗin haka ya sanya kansa ya shiga ciki a ƙanƙanin lokaci yadawo hannunsa riƙeda tabarma shimfiɗawa yayi yace yaya bismillah suka zauna,
Yaya zakari yace toh alkhairi ke tafe dani hamisu yarone ɗan wajena ismail ya hango abunda mu bamu hangoba kasan ana faɗin abunda babba ya hango yaro ko ya hau rimi bazai hango ba amma wannan karon zancem ba haka yake ba wannna karon yaron shine ya hangi abunda mu manyan bamu ganiba,
Cikin rashin fahimtar yanda maganar yaya zakari tadosa baba yace kamar me kenan ba yaya?
Shigowar halima zauren hannunta d'aukeda ruwa a cup na silver yasa sukayi shiru amsa sallamarta sukayi ta isa ta ajiye ruwan had'eda gaida yaya zakari amsawa yayi cikin fara'a,
Sai bayan tatafi sannan yaya zakari yace toh ismaila dai yazomun da wani zance, to shine na zauna dakyau nayi tunani sai naga zancensa yana kan hanya, yaro yayi kyan kai,
Shiru baba yayi yana saurarensa yaya zakari yaci gabada faɗin
Wato shi ismail yaga ƴar wajanka babbar me sunan mama kenan koh?
Baba yace sawwama kenan?
Yaya zakari yace eh ita ce inaga babbar dai yacemin ranar dayazo ya ganta ya yaba da hankalinta sosai sannan ya shaidamin cewa yana sonta zai aureta, gaban baba yafad'i dammm jin zancen ɗan uwannnasa yaya zakari yaci gaba da faɗin to shine nace barina sameka dan wannan abun farin ciki ne sosai zumunci mai ƙarfine zai ƙara ƙulluwa atsakani, dama nace masa toh baza'ayi abu kai tsayeba zan sameka kai mahaifin yarinya in faɗa maka sannan kuma kaje kayi shawara da mahaifiyar yarinya dakuma ita kanta yarinya kaji ta bakinsu idan babu idan wani tsayayye sai ayi magana tunda wuri ayi abu cikin kwanciyar hankali, tunda nasan koda ka samesu toh ai abu bazai gagara ba dan suma zasuyi murna amma adai samesu ɗin,
Advertisement
Baba kansa yana ƙasa daƙyar ya iya ɗagowa ya ɓoye damuwarsa yace toh shikenan yaya In sha Allahu can samesu muyi magana yanda mukayi zan sanar dakai Allah ya za6a mana abunda yafi alkhairi, yaya zakari ya amsa da amim miƙewa yayi yana faɗin toni barina wuce yanda kukayi sai ka sanar dani ɗin,
Baba yace har tafiya yaya baku gaisa da mutanen gidanba gashi kuma ko ruwa baka shaba, yaya zakari yace Alhamdulillahi nagode ina gama cin abinci na taho ka gaidamin da iyalin, baba yace toh zataji, miƙewa yayi ya rakashi har waje da ɗan nisa kafinnan yadawo,
Jiki a sanyaye baba ya shiga gida zama yayi gabaki ɗaya kamar wanda ruwa ya cinyeshi, mama ta kalli baba cikin kulawa tace baban sawwama wani abunne yafaru?
Girgiza kai baba yayi yace ummi bai faruba amna yana gab da faruwa saboda zancenda yaya zakari yazomin dashi yau yayi matuƙar girgizani narasa awani ma'auni can ajiye zancen,
Mama ta matso kusa dashi tace mai yazo maka dashi kuma?
Shiru baba yayi yakasa cewa komai yayi ƙasa da kansa, mama wacce iya tunaninta ya tsaya a abunda ta fahimta tace baban sawwama hhar indai akainane kada ka sanya ranka a damuwa nasan zancen bai wuce ace ka ƙara aure domin samun ɗa namiji da zai gajeka ya kula da kai ba, idanta nine kada kaji damuwa domin ba hanaka zanyi ba,
Girgiza kai baba yayi yace da wannan ne zaifi yimun sauki ummi domin inada damar da dance eh ko A'a wannan kaina kaɗai ya ashafa ba ƴaƴana ba zan iya ɗaukan ko wani irin lamari duk zafinsa akaina amma ba akan ƴaƴana ba,
Mama wacce kanta ya gama kullewa tace ban gane mai kake mufiba baban sawwama, baba yace wai ɗan wajansa isma'il yakeson auren sawwama, dafa ƙirji mama tayi tace auren sawwama kuma?
Baba yace haka dai yace kingani na farko bazan iya bashi auren sawwama ba saboda dalilai biyu, na biyu rashin bashi auren sawwama zai ta6a zamuncin mu,
Advertisement
Abu na farko da zaisa bazan bashi auren sawwama ba shine dalilin wannan abu daya faru da ita idan ɗansa ya aureta dole zai san da faruwar hakan zai dauki mamana da wata manufa ya ringa yimata mummunan kallo, ba fata akeyiba ba lallai ya iyaci gaba da zama da itaba, kuma bazai yiwu mugaya musu yanzuba saboda faruwar abu samada shekara uku ace bamu sanar da dangiba saida akazo neman aurenta zasu iya yiwa mamana wani mummunan fassara nikuma bazanso hakaba yayinda bazanso abunda zai taɓa zuciyar mamana ko yaya yake sannan daga karshe zasu iya cewa sun fasa auren yayinda sukaji wannan labarin kuma ba lallai dan suna ƴan uwanmu ace sun rufa mana siriinmu ba,-
Abu na biyu da zaisa bazan bashi aurentaba shine inason abunda mamana takeso mamana tanason wannan yaro sadam, dan kyautatawa ɗan ƴan uwana dasu kansu ƴan uwana bzan iya tauyewa ƴata hakkinta ba yazamana na barta ko oho sukuma na biya musu buqata ba na shiga rayuwarta na fifita farin cikinsu akan nata, bazan iyaba bazan iya yanda wasu iyaye sukeyi su fifita farin cikin ɗan ɗan uwansu akan na ƴaƴansu ba, shine yaganta yace yanaso kinga idanna bashi aurenta shi na cika masa buri na faranta masa na bashi abunda yakeso yayinda na baƙantawa ƴata na rabata da abunda takeso, kinga hakan babban shiga hakkine, wannan yaro sadam yayi ɗawainiya da sawwama yayi ƙoƙari ya naima mata ilimi na arabi dana boko sutura idanna samu inayi mata dai-dai gwargwado amma kafin nayi mata ɗaya yayi mata uku, yanason sawwama sosai kina kallon idan naki bashi aure nabawa ɗan ɗan uwana me sunanmu zai dawo?
Maciya amana mama tabashi amsa itama jikinta yayi sanyi baba yace bayan cin amana harda butulci, dan haka zuwa gobe idan yazo dakaina zan sameshi muyi magana dashi ya sanarwa iyayensa suzo ayi magana tunda aka fara haka gara ayi yawuce mana kawai duk wani tsai gumi da gutsuri tsome ya ƙare, ƴan uwana kuma nasan yanda zanyi dasu,
Sannan dan Allah wannan zance daga ni sai ke banason mamana tasan da wannan dance saboda nasan halinta dason faranta mana zata iya sacrificing na farin cikinta akanmu,
mama tace in sha Allahu babu wanda zaiji wannan zance, baba yace toh Allah yasa,
Baba ranar bacci ɓarawone kawai ya ɗaukeshi ya tsaya yanata tunanun yanda zai ɓullowa all'amarin."
Ina kuke masoyana masoyan rubutuna🥰 hajiyata kin karanta bibiyata akeyi? Nasan bazaki kasa karanta Y'ar fari fa? Dakuma wanda nake rubutawa yanzu Qaddarar rayuwa? To yaya kikaji salon🥰😍 ya qayatar koh? hajiyata wadannan aiba komai bane somon ta6ine cikin shirinda nayi na nishadatar daku hajiyoyina manyan mata Ku biyoni cikin littafina na YARIMA FAYAD🥰 wannan littafin salonsa daban yake akwaia zazza6ar qauna🥰😍 ciki dana tanada muku, 200kacal zaki sameshi, ga dadi ga sauqi🥰 Don neman qarin bayani,
tuntubeni ta wannan no 08161146563,
Kokuma ki biya kudinki ta wannan accnt 0003075326 zainab m bawa JAIZ BANK.
Ku antayo daga ciki😊😌
Hajiyata kada ki bari abaki labari."
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
Advertisement
- In Serial47 Chapters
May Aien Have Mercy
He was a slave for life, born without a name. One of many, and yet few, that allowed the majority to live comfortably at the cost of their well being. Despite these circumstances, his kindness and righteousness knew no bounds. Not once had he resented the Gods or blamed destiny for his circumstances. Not once had he lost sight of what he believed in, no matter the cost he had to pay to do so. This was the man known by his peers as Mentor. Yet, even the ideals of such a man had one day begun to crumble under a cruel reality. An escape attempt ended in failure, resulting in a vicious punishment that led to the man's demise. He was finally able to welcome the sweet embrace of death, but fate was not done with him yet. Reincarnated into a different world, he was filled with hope for the future. Assuming it was his just reward and a chance for a new life, he set forth into the world, trying to reach towards a simple happiness, that could make him forget his past suffering. Alas, he didn't know how whimsical fate could be. As betrayal followed him with every step, he realized, time and time again, the shackles of his own destiny. Until at last, as he was faced with the injustices of his two lives, his ideals and hopes were broken beyond repair. Unwilling to restrain the accumulated hatred within him any longer, he'd finally unleashed it upon the world, where none would be spared from his hate-fueled vengeance against the world. Thus, if you dare follow Aien on his road of destruction, leave behind your morals, and witness the birth of a Demon.
8 874 - In Serial12 Chapters
Front Tide
He was stranded. Lost, surrounded, and no way out. -- The cover is done by iillya. You can find him in Reddit.
8 76 - In Serial6 Chapters
The Beauty Of The End
William was abandoned by his family and left with a mother who detests him. He is forced into a life of crime, stealing just to feed his mother and himself. But that changes when he's given an opportunity to turn over a new leaf in a world of magic, war and tragedy. ----------------------------------------------------------------------------------------------------------------------------------------------- The Beauty Of The End takes place in a fantasy medieval world where magic exists in multiple forms. William is a boy abandoned by his family and left with a mother who detests him, and at a young age is forced into crime just to feed the both of them. But one day he is visited by a knight order who tell him he has potential for magic. Listening to their words, he leaves to start a new life and train to become a mage like them. The Beauty Of The End updates every day and I'm hoping to push out 100+ chapters consisting off, at the minimum, five arcs. Sometimes there might be double uploads to make up for a break I might've taken. I have most of the story planned out in my head and am just writing down where I think the story should go. I have planned up to arc 2 and maybe some ideas for 3, but that's about it. Thoughts and criticism are appreciated, there's obviously going to be grammar and maybe spelling mistakes that'll I'll try to spot and fix. I might occasionally post chapters that explain certain parts of the world, e.g. lore, countries, organizations, species, magic etc.
8 212 - In Serial21 Chapters
A perfect love story {Completed}
Vanessa is 15 year old girl who's life story is pretty simple. She has a twin sister Lori that's a life guard. She has a major crush on Adam baker. One problem Adam likes Lori her sister. But when adam clones himself accidentally he might but the world in danger
8 64 - In Serial12 Chapters
Blaze and the monster machines: Secret powers
How Blaze has those magical powers? He dosen't know ether. When he hears about the magical place then he sets his views there. He dosen't know that someone wants those powers for himself and orders someone to trap Blaze. But who is she?
8 74 - In Serial61 Chapters
King of the Mountain (Witchfire 2)
Expelled from her old school for a crime she didn't commit, Ivy must gain the trust of the High Pack at Ridgeview Academy to stop her new home from going up in flames. *****Growing up werewolf is brutal. The schools are remote, the internet connection is shitty, and to top it all off, students have to battle each other for a social rank that determines their quality of life after graduation. Enmities can last a lifetime. Death lurks in the woods... Expelled from her old school for a crime she didn't commit, Ivy Thatcher must leave everything behind to start a new life at Ridgeview Academy, a supernatural boarding school in the Great Dividing Range of Australia. But being the new kid isn't the fresh start she'd hoped for. The 2015 graduates have more secrets than years to them; a serial killer is picking off students one by one; strange doorways start opening in her mind, preluding the manifestation of unprecedented powers; and even more frightening than all of that: Ivy finds herself falling for one of her classmates... Will anyone manage to survive Year 12? *****This story is now available on YONDER, your next-generation readingapp from the Wattpad/WEBTOON family. Find it in your app store now! *****[Wattpad Editor's Choice, April 2021][Can be read as a stand-alone novel]Cover designed by Stefanie Saw
8 204

