《ƘADDARAR RAYUWA》Ƙ page 39
Advertisement
**
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa (z3iiyyb3rw3r)
#Follow me on "
Page 39
Buɗe ƙofar ɗakin sadam da akayine ya sanyashi juyowa ya dubi wanda ya shigo, ganin najeeb ya sanya ya miƙe zaune, ƙarasawa ciki najeeb yayi ya zauna kusada sadam, Kallonsa sadam yakeyi har ya zauna baice masa komai ba, duka najeeb yakai masa yana faɗin me yake damunka sadam kasan kwana nawa ina kiranka baka amsawa? Ko ranar da result ya fita sanda na kiraka amma bakayi picking ba, nisawa sadam yayi yace bazaka gane bane najeeb wallhy ita kanta wayar ma ni wani lokacin bansan yanda takeba, gabaki ɗaya kaina yayi zafi, mai yafaru kanka yayi zafi? Najeeb ya tambaya, nisawa sadam yayi sannan ya shaida masa abunda yake faruwa, dariya najeeb yayi yace sadam mijin mata biyu, tsaki sadam yaja yace meye hakan? Na faɗa maka magana kuma kana yimun dariya, wata dariyar najeeb ya ƙara yi yace to ai naga kai ɗan gata ne mata biyu lokaci ɗaya, kaga mummy tayi suprising ɗinmu muna tunanin bazata barka ka auri ɗaya ba sai gashi har biyu zata aura maka, nisawa sadam yayi yace amma najeen nifa kaga abidar nan idan nace maka ga cikekken kamanninta nayi maka ƙarya, rabona dana ganta na manta, kuma kai ni inaga zamuzo sa'anni da ita dan ba ƙaramar yarinya bace, dafa kafaɗarsa sadam najeeb yayi yace haka zakayi hakuri sadam, kaga yanda mummy dakyar ta amince da zancennan abu kaɗan zaka yimata ta nemo abunda zata nemi ruguza maka naka auren, tausayin sawwama nakeji! Sadam ya faɗa cikim sanyin jiki, sannan ya ɗaura da faɗin bata nunanin bataji daɗi zancen aurenba bata nunamin damuwa akan cewa su biyu can aura ba, amma ko bata faɗa ba nasan deep down cikin ranta bazataji daɗi ba, tana da hakuri fiyeda tunani najeeb banaso hakurinta yasa acuceta, banaso ta shiga wani hali dalilin aurena, banaso a musgunawa sawwama saboda ina matuƙar sonta, nisawa najeeb yayi yace naji wannan sadam abu ɗaya zakayi idan bakaso a musguna mata, idan bakaso mummy ta tsaneta kayi ƙoƙari wajen kwatanta adalci atsakaninsu, kayi ƙoƙari ka fita hakkin kowacce acikinsu, kayi ƙoƙari wajan kwatanta adalci, ka danne sonda Kake yiwa sawwana idan suna tare su biyu da abida, hakanne zaisa mummy ta kalli cewa ka riƙe mata zaɓinda tayi maka hannu bibbiyu itama saita riƙe maka naka zaɓin hannu bibbiyu,
Advertisement
Allah yasa kawai sadam yace, sannan kuma ka daure ka ringa zuwa wajan abidan domin itama kuɗan saba ko kadanne bazai yiwu ace anyi sure bbu sabo ko kaɗan ba, hmm kawai sadam yace daga man suka bar wannan zancen suka shiga wani dance daban."
Bayan 5days sadam yana zaune a ɗaki mummy ta aiko a kirashi tashi yayi da sauri saboda shi yanzu sam bayason kiran mummy a akoda yaushe ta kirashi yasan akwai wani abun a ƙasa,
Zama yayi gefe yace gani mummy! Uhmm sadam dadynka ya bada kuɗi a haɗa kayan aure lefe, duka na abida dana wannan yarinya wayema sunanta? Sawwama sadam yabata amsa atakaice, eh ita toh shine na kiraka naji yanayin gidansu saboda kowa a haɗa masa dai-dai ƙarfinsa,
Amma mummy mai zai hana a haɗa duka iri ɗaya ba dai-dai dady ya bada kudin ba?
Dankwalo mummy tayi masa tace ungo naka nan ai dai-dai ruwa dai-dai gari akanme zamu hada musu kayanda yafi ƙarfinsu? Ai ayi musu iya abunda hankalinsu zai iya ɗauka kawai,
Jijjiga kai sadam yayi yace iyayenta ba masu karfi bane, wani aiki yakeyi? Mummy ta tambaya, baya aikin komai sayarda abu yakeyi akasuwa, zaro ido mummy tayi tace kai dai sadam wallhy taurin kanka ne yayi yawa mace ɗaya bata isheka ba? Iyeh? Mata biyun ba wani amfani garesu ba, sadam yace nima abunda na gani kennan mummy gara abarni na auri wacce nakeso yafi, sake baki mummy tayi tace ahh kajimim banzan yaro toh tashi ka bani wuri baza'a bari ka auri wacce kakeso ɗinba,
Miƙewa sadam yayi ya fice cikin five days mummy tagama haɗa kayan lefe nasu su duka, amma na abida yafi na sawwama, zannuwa 40 ne ana abida na sawwama 20 komai na abida ya ninka na sawwama dukda kuwa mummy bataga gidansu sawwamma ba,
Bata bar dady yaga kayan ba saboda tasan zaiyi faɗa sannan kuma yace dole sai an ƙara na sawaama, haka a cikin week ɗin aka kai kayan abida yayinda biki sai matsowa yakeyi baifi saura 10days ba idan kaga mummy alokacin gaba ki ɗaya ta dawo busy,
Advertisement
Sadam kuwa yanda kasan ba bikinsa akeyi ba, domin shi ko sau ɗaya baije yaga amaryar ba,
Sai da mummy ta sameshi tayi masa faɗa sosai sannan yafar zuwa ya ganta,
Ita kuwa sawwama ta maida hankalinta gabaki ɗaya akan karatunta taƙi saka zancen aurenda sadam zaiyi a ranta bare ya dameta koda sau ɗaya bata taɓa yimasa zancen ba kuma,
Daga taji zancen yana shirin damunta saita ɗauki Ƙur'ani taita karatu sai taji sanyi sannan ta ajiye,
Malam sa'adu ya tara yaransa gabaki ɗaya ya sanar musu da zancen auren sawwama ga sadakinta da aka kawo kowa sai ya kawo nasa karon a haɗa ayi abunda ya dace kowa sai mamki yakeyi sadaki 200k dan gidan waye haka kowa ya faɗi abunda zai iyayi banda yaya zakari wanda mamaki yagama kasheshi wato kuɗi hamisu yagani ya sanya yaƙi bawa isma'il auren hafsa kenan? Ya kasa ɓoyewa yabar abun cikin ransa gaban mahaifinsu da kowa yace ashe hamisu kuɗi yafi maka zumunci kenan? Sun kuida kai baba yayi ya kasa cewa komai, mahaifinsu malam sa'adu yace zakari mekake nufi kenan? Yaya zakari yace kwanaki nazo nasamu hamisu da wani zance ni aganina abun farin cikine da murna na shaida masa cewa ismail yaga ƴar wajansa yanaso tunda na faɗa sai naga fuskarsa ta canja maimakon yayi murna sai naga gabaki ɗaya ya canja fuska nida na ɗauka zaifi kowa murna, nabarshi akan zaiyi shawara da iyalinsa akan zai nemeni har yanzu zancen da nake maka baicemim zai bada ko bazai bada ba nidai kawai an kirawoni nazo da nazo na tarasda wannan zance, kaji ashe shi kuɗi yafi masa zumuncine, aikuwa kuɗi ba shine kwanciyar hankali ba inji yaya amadu, yaya sabiru yace amma hamisu ka bamu mamaki banyi zaton cewa zakaƙi ɗam uwanka akan kuɗiba, laraba mahaifiyarsu datake gefe tace yoh wannan matar tasa zata barshi ne ya farantawa ƴan uwansa rai? Itada take haifo masa ƴaƴa mata kaga sun zama mata jari, miƙewa tayi tana faɗin toh ni dai wannan aure bada yawunaba, malam sa'adu daya gama sauraron abunda suke faɗi yace laraba dawo man ki zauna, bbu musu tadawo ta zauna, malam sa'adu ya dubi baba yace hamisu kaji mai ƴan uwanka sukace inaso inji ta bakinka menene dalilinka na aikata hakan?
Laraba tace toh koma menene dalilinsa gida bai koshi ba za'a kaiwa wajene iyih fisabilillhi malam." aina aka taɓa yin haka? Ace gana gida yanaso a ɗauki yarinya abawa bare, ba'a taɓa yiba baza'a fara akanmu ba."
* FITATTU BIYAR NA KUD'INE.*
*FEEDOHM - SILAR WAYE?*
*ZAINAB BAWA- YARIMA FAYAD.*
*ZEE YABOUR - DR MUHRIX.*
*HAJJA CE - ANNURIN ZUCIYA.*
*NANA DISO - GIMBIYA SUHAYMA.*
LITTAFI BIYAR AKAN___500,
IDAN HUDU KIKE SO___450,
IDAN KUMA UKU NE___400,
IDAN BIYU KIKE SO___350,
IDAN KUMA D'AYA KIKE SO 200.!
TURA KUDINKI TA WANNAN ACCOUNT D'IN.
3126584401 FIDDAUSI MUSA FIRST BANK TARE DA SHAIDAR BIYA A 08036953516
KO KUMA.
ACCOUNT NUMBER:- 0003075326 ZAINAB M BAWA
Jaiz bank SHAIDAR BIYA TA 08161146563.
*KO KATIN MTN TA WANNAN LAMBAR 07065283730 TARE DA SHAIDAR BIYA.*
*SANNAN MUYI ADDING D'INKI A FITATTU GROUP🌹...*
Ina kuke masoyana masoyan rubutuna🥰 hajiyata kin karanta bibiyata akeyi? Nasan bazaki kasa karanta Y'ar fari fa? Dakuma wanda nake rubutawa yanzu Qaddarar rayuwa? To yaya kikaji salon🥰😍 ya qayatar koh? hajiyata wadannan aiba komai bane somon ta6ine cikin shirinda nayi na nishadatar daku hajiyoyina manyan mata Ku biyoni cikin littafina na YARIMA FAYAD🥰 wannan littafin salonsa daban yake akwaia zazza6ar qauna🥰😍 ciki dana tanada muku, 200kacal zaki sameshi, ga dadi ga sauqi🥰 Don neman qarin bayani,
tuntubeni ta wannan no 08161146563,
Kokuma ki biya kudinki ta wannan accnt 0003075326 zainab m bawa JAIZ BANK.
Ku antayo daga ciki😊😌
Hajiyata kada ki bari abaki labari."
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
Advertisement
- In Serial22 Chapters
WELCOME TO THE APOCALYPSE
Invading aliens change our world, trapping all humans inside a game run by an insane AI system known as Beginners Guide. Humans are forced to fight monsters to survive. I'm in the process of finishing the book. Posting a chapter every other week. Hope you enjoy. Feel free to let me know what you think.
8 172 - In Serial19 Chapters
Ritz Aven : Can I live normally?[Hiatus]
A girl that was never given the chance to live a normal life. A girl that was used by the humans, only to see her as a monster after the war. Enraged, she started hating the humans and became the earth's antagonist. In the end, she was killed by her own childhood friend.After her death, she met the earth's god. She was given a chance to start over at a new world. A world without the human race that she hated, and a world that was completely different from earth.WARNING: This is supposed to be a shoujo fiction, you know, female mc, romance and stuff. So don't expect action.HIATUS ANNOUNCEMENT: I need more love reference or other things like that before I can continue writing. Time to read more shoujo mangas.
8 90 - In Serial15 Chapters
常鳴屋 [Chinese]
常鳴屋是我的精神世界里的家,在這里我會儲存我的各種不同類型的短篇作品,不定時更新。我只是一個坐在常鳴橋下講故事的人。
8 133 - In Serial13 Chapters
They Can't Separate Us (Pjo kronercy/pernos mutant fanfic)
Percy is a mutant and trouble seems to chase him everywhere at home, at school, even at public bathrooms. Read about his troubles, on not being accepted into society, while having an important, abusive boyfriend. (No Greek Mythology Au)Previously a one-shot( I am doing other chapters, on request)Minor cussing!! DISCLAIMER!!! I do not own the Percy Jackson or the Heroes of Olympus series they all belong to Uncle Rick.
8 143 - In Serial25 Chapters
Church Boy |Yoonmin|
;Being gay is a sin.;Wait intill I have you on your knees sucking me off, church boy.
8 137 - In Serial68 Chapters
Wings of the Republic
(A SEQUEL OF FOR OUR UNITY)Indonesian Civil War is over.The country was quickly rebuilt and it seems it will be peace in our time.But it was a prelude of a larger war..Economic collapse and devastation after Middle East World War united Middle East and North African countries, along with Pakistan, Bangladesh, Maldives, Somalia, followed by Turkey, into a theocratic caliphate and declared jihad. Non-Arab states with large Muslim population like Indonesia, Malaysia, Nigeria, India, former Soviet Central Asian states, along with restored Imperial State of Iran, and Israel, mortal enemy of Arabs, were threatened as they refused to pledge allegiance with the United Caliphate Confederation, the UCC.Soon, great powers joined the fray and the stage was set for a World War III, in the world which strategic nuclear warfare has been rendered obsolete by advances in electronic and cyber warfare, space-based global missile defense, and directed energy weaponry.This is the story of heroic pilots of Indonesia as they fly the flag over South Asia and Middle East. Warnings:This story contains Gore, Violence, Extreme religious contents, Vulgar languages, and reference to racism, war crimes, and unfavorable portrayal of a certain group.
8 375

