《ƘADDARAR RAYUWA》Ƙ page 40
Advertisement
**
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa (z3iiyyb3rw3r)
#Follow me on "
Page 40
Malam sa'adu yace bazamu yanke hukunci ba ai batare munji ta bakinsa ba kai hamisu muna saurarenka yimana bayani, yaya akayi ɗan uwanka yace yanaso ku haɗa ƴaƴanku auren zumunci kuma ka turo bare? baba yayi shiru yayi ƙasa da kai mahaifinsa yace A'a kai hamisu bakai muke saurare bane kayi shiru ka kauda kai gefe?
Ɗagowa baba yayi yace baba nima kaina ba sona bane hakan zanzo ace nabawa ɗan ɗan uwana auren ɗiyata kodan ƙarfafa zumunci amma abun ba haka yakeba ita mamana kusan 2yrs kenan suke tare dashi wannan yaro baba ko makarantama shine ya sanyata islamiya Da boko kuma shine ya ɗauki ɗawainiyarta, tun lokacinda yafara nemanta nayi masa alƙawarin aurenta shine dalilin,
Toh kunji ta bakinsa malam sa'adu yace sannan yadaura da fadin amma kai hamisu ai Shi bayani yanada daɗi tun farko saika yimsa bayani tunda ɗan uwanka ne zai fahimta amma ba kayi masa shiru ba,
Baba yace yayi hakuri yaya bada nufi nayi ba amma ga ƙanwarta halima za'a iya bashi tunda tsakaninsu bbu yawa idan tagama makaranta sai ayi auren, laraba tace mai yasa sai ƙanwarta ba itaba? ai itan za'a juya abashi, malam sa'adu yace laraba bazaku maidani ƙaramin mutumiba, iyayensa sunzo a mutumce sun nemi aure awajena nabasu bazan zama mai magana biyuba tunda akwai ƙanwartan a aura masa itan kamar yanda shi hamisun ya ɓuƙata, kai kuma hamisu basai tagama makaranta ba za'a haɗa da yayarta ayi bikin gabaki ɗaya, ai aikin gama ya gama ya riƙe ƴaƴansa shima Allah yabashi rabonsa aishi baimayi tunani ba lokacin dayaje neman auran ɗiyarka wajanka ai kamar yanda uwarsu ke haifan ƴaƴa mata haka suma ƴaƴanta zasuyita haifa riƙe kayanka ka jiƙasu ka shanye, laraba ta faɗa cikin zafin rai, haka kowa yayita yaɗawa baba magana yana jinsu yayi shiru, yaya zakari yace ku rabu dashi kawai ai jinine bayason haɗawa dani nima na yafe Allah ya haɗa kowa da rabonsa haka Allah yakeyi arziki muma Allah ya bamu dai-dai rufin asiri, yana gama faɗin haka ya tashi ya tafi suma kowa da kowa ya watse aka bar daga baba sai malm sa'adu awajen, kwanatr masada hankali malam sa'adu yayi yace kaje kaci gaba da nema in sha Allahu bazamuji kunya ba zan tattara abunda zan tattaro suma ƴan uwanka abunda suka kawo sai ahaɗa maza kaje kaci gabada addu'a Allah zai dai-dai ta komai sallama baba yayi masa ya koma gida dukda halinda yake ciki bai sanarwa mama halinda suke ciki da ƴan uwansa ba, hankalin baba yatashi sosai domim kuwa duk cikin ƴan uwansa shine mai ƙaramin ƙarfi wanda abunda zai sanya acikinsa sai ya fita ya nema."
Advertisement
yaya zakari ya koma gida ransa a matuƙar bace mahaifiyar ismail take tambayarsa abunda ya faru ya shaida mata tace dama nikam tun ranarda kadawo kake faɗamin kaga sauyin fuska a tatttare dashi lokacin da kayi masa zancen nasan cewa akwai matsala akwai abunda yake nufi, amma auren yaran masu kuɗi har wani daɗine gareshi? Yaranda ba wani tarbiya garesu ba, gasu dai ga kuɗin sai muga yanda zasuje muna man muna zuba idanu, yoh wayasanma ko kuɗinnasa bana Allah da annabi bane, tunda har zasu iya Cire 200k su bada sadaki kamar wanda sukazo sayan yarinyar, haka dai sukayita ai banta auren har suka gaji sukayi shiru."
Sadam yadawo zuwa wajan sawwama kamar yanda ya saba kullum-kullum a kullum yana sanya rai yaji sawwama tayi masa magana amma shiru,
Ranarda ya gaji da shirunta domin bai san ma'anar shirunba ya tsareta yana tambayarta, bakiji maina faɗa bane? Sawwama tace uhmm banjiba kuma taji kawai batason zancenne, ƙarya bata dance dakeba sawwamaty nasan kinji amma barina sake maimaitawa yanda zakiji dakyau, nace ko sau ɗaya baki ta6a yimun magana akan aurennan ba? Baki nuna ɓacin ranki ba, bbu kishi bbu komai shin baki kishi nane?'
Yaƙe sawwama tayi tce yaya sadam nuna kishina ko rashin nunawa bashi zai hana yin auren ba to mai zaisa na tayarda hankalina na tayarda naka?
Haka Allah ya nufa Allah yasa hakan shine yafi alkhairi, sadam ya amsa da main yana mamakin hali irinna sawwama shekerunta ƙalilan amma halayyarta na masu shekaru da yawa."
har biki ya ƙarato sau biyu sadam ya ta6a zuwa wajan abida ahakanma saboda mummy ne tayi insisting shiyasa, abida kuwa sunyi event sosai guda ɗaya sadam ya hallara ahakanma mummy ce ta sanya shi agaba kafinnan, Ranar friday aka ɗaura auren sadam da abida, aranar aka kai amarya."
Mummy ta kashe kuɗi sosai a bikinnan kamar wacce tun farko takesson auren, abida kuwa mahaifanta sun zuba mata kaya sosai kamar bada kudi aka siya ba, tunda akayi auren sadam ke ƙoƙarin kyautatawa mata gwargwadon iyawarsa kokaɗan baya nuna mata auren rashin soyayya sukayi, kamar yanda yake ƙoƙarin bawa sawwama itama lokacin ta,
Advertisement
A wannan lokaci abida da mummy suka fara ƙoƙarin sunja ra'ayin sadam yanda gabaki ɗaya zai hakura da auren sawwama."
--------------
Jikin yarima kwana biyu yana ɗan tashi da dare ko kaɗan basu samun bacci danma wani lokacin mai martaba wajansa take kwana,
Nabila sai idan rana tayi kafinnan take samun bacci, wahalarda takesha kwana biyunman ba abune mai misaltuwa ba,
Haka yauma suka kwana basuyi bacci ba, da rana ma haka tayta juyi akan gadon ta kasa bacci tunanine fall cikin ranta samada shekara guda suna abu ɗaya sai ciwon yayi kamar zai warke sai ya dawo sai yayi kamar zai warke sai yadawo, kwana biyunnan har wata rama tayi, zuciyarta ce take tambayarta shin haka rayuwarta zata ƙare cikin bauta batareda wani ci gaba ba? Haka zata zauna tayita bautar mutuminda bai masan tanayi ba?
Wanda a fili ƙiri-ƙiri yake nuna tsanarta, yanzu tafara gajiyawa sosai da irin hali take ciki koda yaushe rayuwarta ahaka take, tund ata auri yarima ko anguwa bata taɓa zuwa ba shekara guda, Sau biyu ta taɓa kallon mahaifiyarta, mahaifinta kuwa a shekarannan bata sanyashi a ido ba, nabila batasan lokacinda kukan tausayin kanta ya kwace mata ba, sanda tayi kuka har kanta yafara yimata ciwo sannan ta tsagaida ta ɗauki waya da danna."
* FITATTU BIYAR NA KUD'INE.*
*FEEDOHM - SILAR WAYE?*
*ZAINAB BAWA- YARIMA FAYAD.*
*ZEE YABOUR - DR MUHRIX.*
*HAJJA CE - ANNURIN ZUCIYA.*
*NANA DISO - GIMBIYA SUHAYMA.*
LITTAFI BIYAR AKAN___500,
IDAN HUDU KIKE SO___450,
IDAN KUMA UKU NE___400,
IDAN BIYU KIKE SO___350,
IDAN KUMA D'AYA KIKE SO 200.!
TURA KUDINKI TA WANNAN ACCOUNT D'IN.
3126584401 FIDDAUSI MUSA FIRST BANK TARE DA SHAIDAR BIYA A 08036953516
KO KUMA.
ACCOUNT NUMBER:- 0003075326 ZAINAB M BAWA
Jaiz bank SHAIDAR BIYA TA 08161146563.
*KO KATIN MTN TA WANNAN LAMBAR 07065283730 TARE DA SHAIDAR BIYA.*
*SANNAN MUYI ADDING D'INKI A FITATTU GROUP🌹...*
Ina kuke masoyana masoyan rubutuna🥰 hajiyata kin karanta bibiyata akeyi? Nasan bazaki kasa karanta Y'ar fari fa? Dakuma wanda nake rubutawa yanzu Qaddarar rayuwa? To yaya kikaji salon🥰😍 ya qayatar koh? hajiyata wadannan aiba komai bane somon ta6ine cikin shirinda nayi na nishadatar daku hajiyoyina manyan mata Ku biyoni cikin littafina na YARIMA FAYAD🥰 wannan littafin salonsa daban yake akwaia zazza6ar qauna🥰😍 ciki dana tanada muku, 200kacal zaki sameshi, ga dadi ga sauqi🥰 Don neman qarin bayani,
tuntubeni ta wannan no 08161146563,
Kokuma ki biya kudinki ta wannan accnt 0003075326 zainab m bawa JAIZ BANK.
Ku antayo daga ciki😊😌
Hajiyata kada ki bari abaki labari."
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
Advertisement
- In Serial1697 Chapters
I’m Really a Superstar
Zhang Ye, who only wanted to become a celebrity, had tunneled to a brand new Earth that was different. At the radio station, during the host hiring interview. A loud voice narrated, “Up above the sea’s grey flatland, wind is gathering the clouds. In between the sea and clouds proudly soars the Petrel, reminiscent of black lightning. Glancing a wave with his wingtip, like an arrow dashing cloudward, he cries out and the clouds hear his joy in the bird’s cry of courage. In this cry–thirst for the tempest!” As such, the interviewers of this world that had never heard of Gorky’s “The Song of the Stormy Petrel” were so shocked that they stared with their mouths agape! The story begins from here.Thank you for reading novel I’m Really a Superstar @ReadWebNovels.net
8 2961 - In Serial45 Chapters
Against the heavens.
A boy gazes upon the seemingly endless ocean stretching out in front of him, gazes at the endless world ripe for exploration and adventure. But when he closes his eyes, the only thing he can see is a pair of disembodied eyes, blurry and indistinct voices whispering to him from the darkness. Is he haunted or just delusional, exactly what lies behind the things Li Yang sees when he closes his eyes? And exactly what is the Seed of Creation?
8 166 - In Serial30 Chapters
Other World Perfection
Astolfo is a simple child with a fractured soul in a world of magic and mysteries. Plagued with memories that are not his own and a premonition of great dangers, Astolfo navigates through life in pursuit of perfection, one day at a time Updates: Mondays and Fridays
8 230 - In Serial20 Chapters
Christmas Special - F1 One Shots - Completed
JUST CHRISTMAS ONE SHOTS - 2020
8 118 - In Serial7 Chapters
Insane Romance
This is a Toga x Uraraka x Tsu #18 in tsuraraka
8 261 - In Serial14 Chapters
Date A Live: Prelude
As humanity peaks amidst a technological boom, old hatreds and conflicts are still present, ready to sow seeds of calamity. A group of four friends is caught in the crossfire and suffers the consequences. Meanwhile, an extraordinary being finds herself on new land. Exploring the unfamilliar world around her, she has to come to terms with all the ugly and wonderful things she encounters.Will the world reject or accept her for who she is? A non-canon fanfiction story telling the tale of what happened before the main story of Date A Live (DAL).I do not own the Date A Live trademark or light novels by Kōshi Tachibana.
8 178

