《ƘADDARAR RAYUWA》K page 53
Advertisement
**
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa (z3iiyyb3rw3r)
#Follow me on
"
Muna saida kaya, material, laces, atampha, shadda, takalma kayan kitchen da sauransu akan farashi mai sauki siya daya ko sari,
Alarabee's hair cream is available pcs, cotton, half cotton, yana gyara gashi, cire dandruff, hana karyewar gashi, yana softening gashi, yana saka bakin gashi yana saka cika da tswon gashi🥰 masu bukatar kaya ko hair cream ku tuntubu wannan lambar 08161146563
Page 53
Sadam baije kiran dady ba sai da ya tabbatar ya zauna yagama tsara abunda zai fada idan yaje can, har rubutawa yayi a paper yanata mai-maitawa kamar karatu🤔 yanda idan yaje bazai manta koda kalma daya ba,
Saida ya tabbatar ya shirya kalamanda hankalinsu dady da mummy zai dauka sannna ya nufi gida,
Wata irin nutsuwa sadam ya tattaro yashiga gidansu da ita wacce kana ganinsa kaga salihin bawa,
Yasamu mummy tacika tayi fam kadan yarage ta fashe sai huci take jiransa kawai takeyi ga abida kusada ita tayi wani luff kamar mras lafiya,
A nutse sadam yashiga har cikin dakin mummy ya tsugunna har kasa ya gaidata yayi kamar baisan duk wani abunda yake faruwa ba,
Dakyar mummy ta amsa gaisuwarsa kansa yana kasa yace mummy dady yadawone? Yakirani datsu wai yana nemana, harara mummy ta watsa masa tace eh ai kayi abunda za'a nemeka ne ai dan kaniya, sadam yayi magana cikin wata innocent voice yace me yafaru mummy? Dan kwalo tayi masa tace haka kaji maras kunya au bakamasan abunda kayiba?
Sadam ya sunkuyarda kai mummy tace tashi muje wajan dadynku hana jiranka kema abida taso nan mutafi,
Cikin drama sadam ya zaro ido yace abida! Mai kuma yakawoki? Ban fada miki kidaina fita bada izinina ba?
Mummy tace eh ai dole kafadi haka ka jibgeta bakaso tazo tafada ba, sadam yace nikuma? Mummy tace A'a ni! Shiru sadam yayi yafice daga dakin zuwa shashin dady, durkufe abida da mummy sukazo duka sameshi gaban dady bayan sun shigo dady yafara magana da fadin sadam kabani makaki i am disappointed 😔 sadam harka sanya ahnnu ka doki mace? Eyeh sadam? Bakada hankaline? Kataba kallon ko zungiro nayiwa mummynku? Sadam macen auranka itace abin duka a wajanka, kaban mamaki banji dadiba sam da abunda ka aikata, Allah yagani sadam Allah ne shaida inabin bayanka a komai amma bazan goyi bayanka adukan yar mutane ba,
Advertisement
Mummy tace ai wallhy dabadan dadynku ya hananiba sadam yau da saina sharara maka mari abunda ban taba yimaka shiba iya tsawon zamana dakai da yau saina yimaka, saboda abunda kayi kaban mamaki kanuna banda girma akan idonka ka dubi abida ka daketa akan wata kaskantacciyar matarka?
Dady yace sadam baka kyautaba gaskiya a yanda ta nuna min kana nuna banbamci atsakaninsu kuma bata isa yin maganaba saika hauta da fada kamar zata daketa jiya kuwa saida ka dakeba,
Sadam baice komaiba saida ya tabbatar sun gama sannan yace Dady ka gafarceni amma ni bansan me kuke magana akai ba, ita abidar ce tace na duketa?
Mummy tayi salati ta sanarwa ubangiji tace kaji yaro karya kenann akaia maka?
Sadam ya girgiza kai cikin iya kwarrwa a drama yace ni banceba mummy saboda banida masaniya akan abunda tazo tafada muku, amma data fadi abunda tazo tafada danima anjirani anji abunda yafaru kafin ayankr hukunci,
Dady ya jijjiga kai yace hakane dama idan anji ta daya bangare ajira aji na daya bangaren saboda maslaha akeso baza'a taba fahimta ba idanba an tsaya anji tabakin kowaba amma dukda haka sadam bazan goyi bayanka a duka ba, wannan ba dabi'ar mijin kwarai bace koda kaine mai gaskiya zan hukuntaka a hakan dakayi, dan ba dalili bane dukan mace, sadam ya girgiza kai yace sam dady ni ban dakeba ba, sai dai idan sharri taso hadawa shine zatace na duketa, dady ai idan akazo akace maka zan iya dukan mata zaka karyata danni koda gigin wasa ban taba tunanin saka hannu jikin matata da duketaba, kuma itama abida ban duketaba, dady yace toh wannan abu da daure kai yake kuma tacemin baka dawowa sai karfe dayan dare idan kadawo asubahi kake ficewa menene amfanin hakan,
Inna lillahi sadam tafadi sannan yadubi abida da mamaki yace abida kifadi tsakaninki da Allah nine bana dawowa gida sai shadaya? Abida zatayi magana yayi saurin katseta yace dady duk rintsi bana wuce 10:00pm awaje kuma dalilin dayasa nake kaiwa haka saboda sawwama da batada lpy ne,
Advertisement
Kuma maganar fita asubahi kuma dady idan ta kwanta bacci yanda kasan kasa bata tashi har lokacin fita aikina sai dai na shirya kaina mostly awaje nakecin abinci ta dalilin haka har ulcer nakamu dashi nafada mata taki gyarawa shine kawai nake wucewa gidan sawwama naci abinci daganan na wuce dady kaga laipina a wannan lamarin?
Girgiza kai dady yayi yace A'a abida kuwa tasake baki kawai tanajin sharrinda sadam yakeyi mata,
Sadam yacigaba da fadin dady ko jiyan datake cewa na duketa ban duketaba nadawo tana fadamin bakaken maganganu duk wata maganar datazo bakinta ta tsaremin hanya ta hanani wucewa shine kawai na tureta na wuce hakanma bai isheta ba har kofar dakina tabi tana bubbugawa tana fadin maganganun da sukazo ranta ban kulataba saida nafito sallar asubahi nasameta kwance a kofar dakina tana jira nafito tayi bala'i nikuma dana fice yasa ban dawoba gudun rikici amma dady kaga hakan danayi mata bai isheta ba har saida tabiyo nan ta hadani da sharri,
Jijjiga kai kawai dady yakeyi mummy kuwa sai salati tana bin abida da harara mummy tace aikuwa idan hakane abida baki samu saraba wallhy gara ki canja hali tun wuri kuka abida tasaka ganin batada kalaman da zata wanke kanta ta rufza da ita, mummy tace kinsan kece maras gaskiya amma kika saka inata bala'i inata bala'i da wani wajene nan da kinsakani jin kunya,
Dady ya girgiza kai yace abida baki kyautaba idan kika yiwa mijinki kazafi ribar mai zakici?
Karki sake yin haka koda wasa ko banan ba, yanzu da wajan abbanki kika kai wannan zancen kinsan zai dauki zancen da zafi saboda bbu mahaifin da zaiji an duka masa ya yakyale, haka bbu kyau karki sake, abida tanason yin magana amma kuka ya hanata tanata fadin Allah dady,,, Allah dady,,, mummy tace rufamin baki ki tashi mutafi, tatashi taja hannunta suka fice, sadam zuciyarsa tayi sanyi amma abida tadan bashi tausayi,
Sai bayan yagama shirya drmarsa sannan hankalinsa yadawo kan sawwama a gaugauce yayiwa dady sallama yafita dady yace toh adaici gaba da hakuri kasan lamarin mata sai hakuri koda shekarunku daya da mace to sai kayi hakurin zama da ita saboda hankali bazaizo dayaba,
Sadam yace bbu komai dady,
Sadam yayiwa mummy sallama yatafi duk da dantane amma saida tadanji kunyarsa na zakewar datayi,
Mummy adaki fada take yiwa abida tana fadin ahakan abida kikeso mijinki yasoki ya kaunace ki? Ashe dama ke shashahsha ce? Bakisan yanda zaki tarairayi miki ba ki kula dashi? Sokuwa kai, tun wuri ki farka daga mafarkin da kikeyi kina jina? Koh wallhy abida kisan mai yake miki ciwo ki nemi hanya tun dare baiyi mikiba, daga masifa kuma sai mummy tadawo yimata nasiha, har abida taji zuciyarta tayi sanyi amma dai ranta cike yake fall da tunanin zancenda sadam ya shirya dama gaskiyar hausawa da sukace idan baka iya kama barawoba shi barawo zai kamaka,
Har dare abida takai agidan mummy sannan tatafi kafin tatafi sanda mumy tace mata kada tasake ji idan takoma karta sake dago da maganar."
————————————————
Nabila-Yarima
Ina kuke masoyana masoyan rubutuna🥰 hajiyata kin karanta bibiyata akeyi? Nasan bazaki kasa karanta Y'ar fari fa? Dakuma wanda nake rubutawa yanzu Qaddarar rayuwa? To yaya kikaji salon🥰😍 ya qayatar koh? hajiyata wadannan aiba komai bane somon ta6ine cikin shirinda nayi na nishadatar daku hajiyoyina manyan mata Ku biyoni cikin littafina na YARIMA FAYAD🥰 wannan littafin salonsa daban yake akwaia zazza6ar qauna🥰😍 ciki dana tanada muku, 200kacal zaki sameshi, ga dadi ga sauqi🥰 Don neman qarin bayani,
tuntubeni ta wannan no 08161146563,
Kokuma ki biya kudinki ta wannan accnt 0003075326 zainab m bawa JAIZ BANK.
Ku antayo daga ciki😊😌
Hajiyata kada ki bari abaki labari."
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
💞
Advertisement
- In Serial351 Chapters
The Guardians' Throne - The First Magic Swordsman
After a long time in the darkness, a lost soul is transported to another world, and there the soul is given another chance and is reborn as a boy…In a world of swords and magic, Zaos is given another chance after hearing an unknown voice asking him to protect someone. While he couldn’t remember many things about his old life, he still decided to live his new as much as possible. Even though it looked like he was destined to do something, Zaos chose to follow his own path as much as possible.He tried that… but it looked like the machinations of destiny won’t give him much option. Weird things were happening in the kingdom he was born, and before he could imagine… Zaos was throw in the middle of a war in which some were trying to revive the god of the world, and others were trying to prevent it. Zaos will fight in this war while he also looks for the person he is supposed to protect.
8 4652 - In Serial1780 Chapters
Heaven’s Devourer
The Yanhuang Ancient Domain, vast without end, gave birth to many Celestials and Demons of antiquity tore Heaven and Earth apart and surpassed the control of the 3 Realms and 5 Elements over the endless years it has existed. Numerous Gods, more than ten thousand races, and humans born with a God class body have also come out from the Domain, traveling through the nether, warping Yin and Yang, omnipotent.
8 1413 - In Serial89 Chapters
Justice in the One Piece World
After a tragic death, the sisters Kara and Diana got a deal from God. "You can mess up the One Piece Storyline for my entertainment!" "Can we have some cheats? We don't want to die right away" "Sure, here you go" "Holy crap, seriously?" Follow the 2 OP sisters as they join the Marines and mess up the Storyline. Warning: This story is mostly light hearted with 2 OP MCs on the loose in the One Piece World. if you do not like this sort of novel, I recommend you do not read it. Note: This story was heavily influenced by Kestix's "Lia and Lara will Seek the One Piece" Please go support his work as well. Of course, I do not own One Piece. I only own the OC (Original Characters) that I put into the story. Enjoy! I recommend reading this story at 20px. You can choose the font size above :) Also, I do not own the Cover Art. It is from One Piece Wiki Fandom
8 301 - In Serial54 Chapters
The Wandering Scholar
Zhou Mingzie, A young Chinese American is suddenly brought into a mythical land, similar to China in many ways, but is most definitely not. This new world appears to contain cultivation elements like the Wuxia and Xanxia stories he read throughout highschool, but he can also gain Levels and Skills, I mean Paths and Techniques. Sure he is Chinese, but he grew up in America, so he doesn't want to ascend to the heavens and fight spirit beasts, does he? But Mom wants him to embrace his heritage more...jk...unless? [participant in the Royal Road Writathon challenge] Inspired heavily by The Wandering Inn and Beware of the Chicken, as well as cultivation novels in general, this story hopes to take a Westernish approach to the standard Cultivation approach, being more subtle and changing how it approaches the standard tropes of the genre, without abandoning them entirely.
8 190 - In Serial15 Chapters
Into You/ / HyunLix
Hi guys!!! This is my first WattPad story I hope you gonna like it...☺️💕This is Hyunlix smut🔞!! Wanna read it but you don't like smuts? Don't Worry I will remind you when it's gonna come and you will decide😉! Have fun. ☺️
8 101 - In Serial9 Chapters
•complicated• (Enhypen Mgl)
Ахлах сургуулийн сурагчдын бодолд юу оршдог бол?
8 129

