《ƘADDARAR RAYUWA》K Page 60
Advertisement
**
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
ZAYNAB BAWA
#Follow me on
"
Allah yasa mucika da imani rayuwa dole saida addu'a kada mu zauna kara zube muyi addu'a sannan mu koyawa yaranmu addu'a, Aduk lokacin daya kasance zaki/ka fita gida kiyi addu'a."
(BISMILLAHI TAWAL KALTU ALALLAH WALA HAULA WALA KUWWATA ILLA BILLAH)
Kokuma kice
(ALLAHUMMA INNI A'UZU BIKA AN ADILLA, AU UDALLAH, AU AZILLAH, AU UZALLAH, AU ADHLIMA, AU UDH,LAMA, AU AJHALA, AU JUJHALA ALAYYA.") in sha Allahu Allah zai karemu."
Page 60
A Lokacin da sanyayyar muryarta da isa izuwa kunnuwansa sai ya samu kansa da lumshe idanuwa yayinda wata kasala ta saukar masa, nunfashi ya fitar ahankali, yatafi izuwa wata duniya batareda ya iya amsa sallamarta ba, jin shiru ya sanya sawwama sake yin sallama a karo na biyu, wanda hakan yasake jefashi cikin wani irin yanayin,
Bacin randa yakeji a cikin ransa yagushe ya zamana saura dan abunda baza'a rasaba domin jin muryarta kadai ya gusar masa da bacin ransa,
Baiso bacin ransa ya gushe lokaci guda ba amma shi kansa ya tabbata muryarta kadai bazata bari ya kasance cikin bacin ranta ba domin tana saukar masa da nustuwa hadeda kwanciyar hankali,
Wata iriryar kewarta ne ta rufeshi nan da nan yaji tsikar jikinsa tafara zubawa, cikin kasalalliyar muryarsa yace why? Sawwama meyasa? Kinsan bazan iya bata rai dakeba shine yasa kika yimin wannan hukuncin?
Hukuncinki ya cutar dani ya sanyani cikin wani yanayi jiya na kwana da bacin rai,
Nan da nan jikin sawwama ya dauki rawa muryarta tafara cracking kamar wacce zatayi kuka tace nashiga uku yaya sadam dan Allah kayi hakuri ka yafeni na tuba kamin rai, bazan taba cutar da kaiba kaima kasan haka idan nayi kuma sai dai cikin rashin sani kaicona da nabar abun kaunata jiya ya kwana cike da bacin raina Allah ya huci zuciyarka ka sanyaya maka ita, ka yafeni bazan sake ba bazan sake kwatanta irin haka ba,
Iska sadam ya furzar sannan yace bbu komai yawuce amma idan kika sake zan sake kwana cikin wani bacin ran, koma menene gara kifito ki fadamin hankalina zaifi kwanciya da ki boyemin, sawwama tayi shiru tana saurarensa ita duk a tunaninta kiran ta da yayi bata kusa shine yadaga masa hankali har haka zaiyi zaton ko rashin lpy kokuma haihuwane tataso,
Sawwama tace in sha Allah bazan sake ba banyi hakan da nufin quntata zuciyar da take cike da soyayyata ba,
Ajiyar zuciya sadam ya saukar yace shikenan yawuce, hira suka dan taba da sawwama sannan sadam cikin zolaya yace yaronna nawa saina roqa kenan kafin a turamin pic din yarona nagani?
Damm dammm gaban sawwama yafadi dan maganar tafito mata a bazata. Shirunda tayine ya sanya yace toh shikenan barina roqa ataimaka a turamin pic din yarona nagani naji sanyi a cikin zuciyata, idanuwana sunata azalzalata dason ganinsa inaso naganshi naga kamannin waya dauko ni ko mahaifiyarsa, idanni yadauko nayi miki wayo sai kiyi qoqari ki haifo mai kama dake idan kuma ke ya dauko ni yakamata inazo indage a haifomin mai kama dani,
Advertisement
Wadannan kalaman suka tabbatarwa sawwama cewa sadam yasan ta haihu toh wuaa fada masa? Koh mummy?! No mummy bazata sanar dashiba itada ta gargadeni da kada na sanar dashi toh waye?
Halima?! Kai anya kuwa ai halima batada contact dinsa nacan, amma ai idan batada contact dinsa ai zata iya dauka a wayarta ta sanar dashi , ajiyar zuciya tasauke cikin sanyin jiki tace yaya sadam kayi hakuri dan Allah ka yafeni banyi haka dan bata maka rai ko in musguna maka ba,
Kasan dole zanbi umarnin mummy nayi mata biyayya, kuma itama nasan bawai ta hana asanar dakai haihuwar bane danta musguna maka ko shiga tsakaninka da yaranka ba tana tunanin kana cikin halin karatu kuma ace kadawo,
Shiru sadam yayi yana sauraren sawwama bayan tagama yasaki wani dan siririn murmushi, tabbas jiya kwana yayi yana tunanin meyasa sawwama zatayi masa haka! Mayesa zataqi sanar dashi ta haihu? yayi zamansa yayi tunanin lokacin daya fadawa sawwama cewa idan ta haihu zaizo amma bai iya tuna lokacin ba, koda ya karkare tunanin bai samuba sai yace toh ta'iya yiwuwa alokacin suna shan soyayya ne shine yayi mata wannan alqawarin batareda ya saniba,
Yasan sawwama sarai batada fade-fade zance kukayi da ita ba lallai tasake maimaitawa ba, amma yaya zaiyi tunda bakin mahaifansa yaji wannan,
Sai yanzu dayaji kalamanta ya tabbatar aikin mummy ne tunda yasan zata iyayin fiyeda hakama, wani murmushin yasake saki hadeda girgiza kai yace Allah dai yaja kwanan mummy take taken ta kadai na kwanakinnan idan yayi la'akari yakamata yagane cewa da wata akasa, yanda jiya tayi kasa da murya tana bashi hakuri kadai ya isa ya sakashi cikin shakku, mummy bazata taba yabon sawwama babu wata akasa ba ayanda yasan mahaifiyarsa bazata taba daukan wata shawara daga wajan sawwama ba duk kyawun shawarar kuwa,
Tun lokacin yakamata ya tsaya yayi tunanin cewa sawwama tsoron mummy takeji bazata taba sakewa da mummy harta yanke wannan hukuncin ba,
Duk wannan baiyi tunaninsa ba amma saboda me? Saboda irin gaskatawa dake tsakanin d'a da uwa, saboda irin yarda dake tsakanin d'a da mahaifiya, a iya tsawon rayuwa yaro yakan yarda da mahaifiyarsa fiyeda kowa a duniya yakan gaskata zancen mahaifiyarsa batareda tunanin zata iya karyatashi ko cutar dashi ba, wannan yarda da amana dake tsakanin d'a da uwa mummy takeso tafara breaking nata tsakaninta da danta, ajiyar zuciya ya sauke a cikin ransa yana tunanin toh sai yaushe? Sai yaushe mummy zataso sawwama su zauna lpy? Sai yaushe mummy zata sauko daga zafin da tadauka da sawwama, muryarsa sawwama ce ya katseshi da fadin yaya sadam kayi shiru, kace wani abu dan Allah, iska ya furzar daga bakinsa ya lumshe idanuwansa hadeda mikewa a kan bed yace" ina sauraron sanyayya kuma daddadan muryarki shine kika katseni dalilin daya antayani tunani kenan,
Advertisement
Idan ina sauraron muryarki sawwamaty banaso ta katse idan ina kallonki banason dainawa idanuwana suna cike dason ganinki, ranarda suka ganki bansan yaya zasu kasance ba zasu kwashi tsawon lokacin suna kallonki yayinda hancina zai shaki daddadan kamshinki, kunnena suna sauraron muryarki akusa dani, gani nake kamar ranar kara tsayi takeyi na matsu na kaqu naganki kusa dani,
Turo baki sawwama tayi tanajin kalamansa na saukar matada nustuwa da wani dadi cikin ranta,
Cikin shagwaba tace yaya sadam bakafa amsamin tambayata ba, yar karamar dariya yayi yace duk wannan amsar dana baki bata gamsheki kenan, to kibari duk ranar da nadawo zan baki abunda zai gamsar dake ya karashe maganar cikin zolaya,
Rufe ido tayi da dayan hannunta yayinda dayan yake kare da waya tace laaahh yaya sadam nifa ba haka nake nufi ba,
Kwaikwayan maganarta sadam yayi yace toh me kike nufi?
Sawwama tace cefa nace kayi hakuri! Aina rigada nave nayi hakuri koh? Jiya mummy tarigada tayimin bayanin komai kawai dai naji babu dadi ne amma dana zauna nayi tunani sai naga koda hakan da kikayi yasa banji dadiba biyayya da kika yiwa mahaifiyata yasani jin dadi nasan ko idona ko babu ke mai biyayyace gareni da mahaifa na,
Ajiyar zuciya sawwama tasauke tace hakane yaya sadam mummy mahaifiyace a gareni kuma ina kaunarta fisabilillahi itace wacce ta haifomin kai danake alfahari dakai da babu ita ba lallai na sameka ba, kuma nasan tayi hakanne da dalilinta mai karfi mu yarane abunda iyayenmu suka hanga mu bazamu hanga ba biyayya agaresu shine mana mafita, zamuyi biyayya zuwaga abunda sukeso har indai bai sabawa shari'a bai kuma saba'a fadin Allah da manzonsa ba, iyayenmu kuma sunada ilimi na addini bazasu taba sanyamu ku kaucewa hanyar Allah ba mu faranta musu muma sai Allah yajikanmu yabamu masu faranta mana,
Kai sadam ya jijjiga na gamsuwa da maganar sawwama hakane Allah yayi miki albarka, nagode nagode kwarai da gaske da tayani samun aljannata,
Sawwama tace kadainamin godiya yaya sadam aljannata tana karkashin zanyi iya kokarina dan naga ka dagamin na shiga wannan kofa to kaima dole na tayaka muyi biyayya dan mugudu tare mu tsira tare,
Sadam ya datse zancen da fadin toh yanzu dai ki aturamin pic din yarona danna fara gane cewa dagasken rowarsu akeso ayimin,
Sawwama tace ayi hakuri ranka shi dade yanzunann zan tura maka,
Batareda takashe wayarba tayi masa sending pics dinsu kusan guda 20,
Sadam ya dauki samada 10minute tana jira taji yayi magana amma shiru shikuwa can kallon yaran kawai yakeyi duk tunaninsa yaro daya sawwama ta haifa baiyi zaton yan biyu bane, sai yakeji kamar wasa sawwama take masa, farin ciki ya lullubeshi yakai wayar bakinsa ya sumbaci pic din, sai yaji kamar yayi tsuntsu yadawo ya rumgume yaransa ajikinsa,
Jin shirun yayi yawa yasanya sawwama tace yaya sadam kodai kishine ya kamaka saboda kaga duka dani suke kama,
Batareda ya amsa maganarta ba yace Allah yayi miki albarka, amin sawwama ta amsa,
Sadam yace sawwamaty kin bani farin ciki maras misaltuwa nagode miki,
Allah yabiyaki, kinsha Wahala sosai koh?
Sawwama tace eh dayake kasan dafarko ag,,,,,, shiru tayi ta katse zancen danta tuno warning dinta yayi mata akan kada tayarda da zauna agida tana farajin nakuda, saurin canja zancen tayi da fadin dayake nayi goduwar nakuda shiyasa nasha wahala saida abin ya gagara sai akayi CS, CS! yafadi cikin al'ajabi, sawwama cs akayi miki amma shine har kika iya boyemin idan wani abun ya sameki fa?
Har indai irin haka tafaru koda kin fadamin bayan an hanaki fada zan fahimcekk idan kina ganin kuma bazkai iya saba musu ba saiki sanya ko halima ta fadamin kinga bake kika fadi da kanki ba,
Toh kawai sawwama tace danta matsu zancen ya tsaya haka,
Ta sauya zancen da fadin amma yaya kagani dani sukayi kama koh?
Sadam yace Eh naji wadannan sunyi kama dake nagaba kuma triplet zaki haifa kuma dani zasuyi kama, ina dawowa tsarabar da zan fara baki kenan,
Dariya sawwama tayi tace banda dai kana dawowa yaya sadam ka manta CS akayimin?
Shima sadam dariyar yayi yace toh naji bayan nadawo da shekara daya,
Uhm kawai sawwama tace, sukaci gaba da hirarsu cikin annashuwa."
Ina kuke masoyana masoyan rubutuna🥰 hajiyata kin karanta bibiyata akeyi? Nasan bazaki kasa karanta Y'ar fari fa? Dakuma wanda nake rubutawa yanzu Qaddarar rayuwa? To yaya kikaji salon🥰😍 ya qayatar koh? hajiyata wadannan aiba komai bane somon ta6ine cikin shirinda nayi na nishadatar daku hajiyoyina manyan mata Ku biyoni cikin littafina na YARIMA FAYAD🥰 wannan littafin salonsa daban yake akwaia zazza6ar qauna🥰😍 ciki dana tanada muku, 200kacal zaki sameshi, ga dadi ga sauqi🥰 Don neman qarin bayani,
tuntubeni ta wannan no 08161146563,
Kokuma ki biya kudinki ta wannan accnt 0003075326 zainab m bawa JAIZ BANK.
Ku antayo daga ciki😊😌
Hajiyata kada ki bari abaki labari."
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
💞
Advertisement
- In Serial7 Chapters
Santa’s Gift for Dr. Peter Daszak
Santa and his pet pangolin prepare the perfect Christmas gift for Dr. Peter Daszak!
8 75 - In Serial14 Chapters
Dystopia Against Fantasy
What would happen if a Dystopian Earth came across a fantasy world? Follow an elite team of advanced soldiers as they are sent into an unknown world of magic and fantasy, encountering mythical creatures and divine beings, all the while sowing the seeds for a war across dimensions. Amateur Author, please do not expect much Cover mine
8 166 - In Serial6 Chapters
The Creator's World
In a world where Creators make universes to play in, I am a Creator. My name is Michael Tanner and this is the exploration of my greatest creation. It is a world of swords and sorcery, though I choose to be a sorcerer and perhaps a little more. Join me as I explore this new universe, while in our universe, a mysterious extrasolar object enters this solar system on a collision course with our Earth's sun.
8 159 - In Serial35 Chapters
I Came, I Ran
As they were summoned, the old king in front of them said to the "Young heroes, I have summoned you here to fulfill a great prophecy, you have to defeat a coming evil, foretold by the by our High Priest, Ursum." The heroes, as observed by the king, looked around the room, and said out loud "Where are we?" "You are in the great kingdom of Vo-". Unfortunatley the king stopped before he could end the sentence. There was a dagger sticking out of his skull... -------------- This is my first story, constructive critism is appreciated and wanted. So please, help me, I am drowning in a thing called incompetence.
8 175 - In Serial11 Chapters
10 Myths about Introverts
Introverts! Unite separately at your own homes.
8 334 - In Serial36 Chapters
Why The Hell Not
Sweat started to form all around my body as the pain consumed me. It was 9pm and this had to be the worst wave of heat I've ever experienced! My body ached as the flames traveled from my core, spreading to the rest of my body. I hate heat, every type of heat, but mainly this one. Heat, in my pack, is a bitch! The second you turn 16 your heat starts. Then for the rest of your life you get a heat cycle once a month, as if having a period isn't bad enough. The heat happens right after your period, leaving you 2 weeks of peace as a woman if you find your mate your 16 years of life! If you did not find your mate at 16, when you turn 17 it will be every 2 weeks! Your period is still once a month, thankfully, but the heat cycle directly after your period is the strongest! Leaving you ONE week of peace...unless of course you don't find your mate by the time you turn 17. If you are unlucky enough to not have found your mate by the time you are 18, then yes it will be EVERY week! Leaving you NO peace!!Basically the longer you go without finding your mate, the more heat you will go through. If you're 20+ then it could be EVERY hour! Once you find your mate it goes back down to once a month, thankfully. Lucky, or lucky for me, I'm 17...meaning I've gotta deal with this every 2 weeks. This one in particular is the worst one yet! I grabbed the water on the side of my bed and tried to fix my dry throat.......
8 92

