《ƘADDARAR RAYUWA》K Page 61
Advertisement
**
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa
#Follow me on
"
Page 61
Da sauri tafarka daga baccin datake ganin rana tafito ya sanyata sakin salati domin ko sallar asubahi batayi ba a gaggauce tashiga toilet tafito daure da alwala tagabatar sallah sannan ta kishingida a jikin sallayar domin wani baccine a idanuwanta bata samu bacci dawuriba ba jiya da daddare tazauna tanata tunani kamar yanda tasaba tana tunanin daya zame mata jiki yazama aikin yinta a kullum, bayan baccin ya dauketa kuma saita yi wani mafarki, mafarkine mai dadin gaske wanda bata taba koda kwatanta irinsaba hakan ya sanyata makara sallar asubahi,
bata dade da kishingida ba wani baccin yasake daukarta irin mafarkin datsu taci gaba dayi gata gakuma yarima cikin hankalinsa suna zaune suna hira cikeda nishadi afuskokin kowannensu,
Suna zaune a wani waje mai yalwar furanni hadeda bishiyoyi, kana ganinsu zaka hango tsantsar farin cikin dasuke ciki a cikin mafarkin take karasawa kusa dasu, tazo daff dasu cikeda murnar ganin kanta tareda yarima a wannan yanayin, farin cikin dayake fuskartace ya gushe, annashuwan fuskarta ta canja izuwa tashin hankali sakamakon ganin fuskarta tana canjawa wani kamanni hankalintane yatashi ayayinda ta ga gabaki daya kamanninta ya canja izuwa kamannnin wata yarinya wacce bata taba ganin fuskartaba shikuma yarima ko ajikinsa kamarma baisan da canjawar fuskarba saima wani farin ciki daya karu akan fuskarsa a firgice nabila tafarka daga baccin data keyi mafarkin datayi datsu ya sanyata farin ciki amma na yanzu yabata tsoro, me mafarkin datayi yake nufi kenan? Fuskarta ta canjawa zuwa wata fuskar? Wacece wannan wacce tagani amafarkinta?
Wannan sune tambayoyin da batada amsarsu batada kuma wanda zai amsa mata, jiki a mace tatashi tashiga tayi wanka tukunna ta shirya tafara yan gyare-gyare,
Saida nabila tagama duk wani abunda zatayi na gyaran gida izuwa breakfast sannan tanufi dakin yarima dan ganin yanda yakwana, murda hannun kofan tayi tashiga da sallama duk da tasan cewa bazai amsataba, akwance ta hangoshi a katafaren gadonsa har yanzu bacci yake bai farkaba da sauri ta karasa gaban gadon tadan rankwafo tataba fuskarsa jikinsa bbu zafi ajiyar zuciya tasauke sannan a hankali tafara taba kafarsa tana fadin yarima! Yarima! motsawa yayi a hankali sannan yabude idonsa ya zubesu akanta gabantane yayi mummunan fadi sakamkon yanayin data ganshi irin yanayine mai kamada wanda taganshi ranar, kallo ne yakeyi mata kamar wanda yakeson gano wani abun tattare da ita, cikin faduwar gaba nabila tajuya dasauri niyyarta takoma dakinta tadauki waya takira umma tazo taga yanayin da yake ciki,
Caraf taci ya cafko hannunta a tsorace tajuya ta dubeshi batayi auneba taji sautin muryarsa ta daki dodom kunnuwanta,
Am sorry!
shine abunda yake kokarin ambata, dukda abunda yake fadi bai fito radauba domin harshensa kamar a harde yake amma nabila ta fahimta abunda yake shirin fada, sandarewa nabila tayi a tsaye takasa aikata komai cikin tsoro sai tsaro idanuwanta take koda sau daya bata tabaji ya ambaci wata kalma ba sai yau,
Advertisement
Saurin saketa yayi ya rike kansa,
Atake kansa yafara jujjuya masa kamar wanda ake hajijiya dashi haka yaji kawai ya sake wani irin kara a tsorace nabila tafita bbu mayafi tashi sashin mai martaba bata sameshi anan ba a firgice tayi hanyar fita sukayi kicibus da umma, umma wacce ganin nabila ahaka ya sanya itama ta rikice ta rikota tana tambaya nabila mai yasamu haaliifan? A firgice tace umma yarima yayi magana yanzu kuma ihu yakeyi umma tayi saurin sakin abunda yake hannunta tayi cikin sashinsu da gudu a haka taje ta tarasda yarima rikeda kansa yanata kuwwa,
Karasawa tayi tasaka kuka ta rikeshi gam ajikinta sai kokarin kwacewa yakeyi nabilace tayi aika akaje aka gayawa mai martaba yana faada yataso yazo yasamu abunda yake faruwa, mai martaba bai dade yana masa addu'a ba abun ya lafa ba kamar daba da sai yakusan kwana akansa ana abu daya,
Bayan yasamu baccine nabila take basu labarin abunda yafaru umma tana kuka tana fadin in sha Allahu komai yakusan zuwa karshe yarima kakusa samun lpy,
Mai martaba yace lamarin kam akwai cigaba domin ko yanzu a kankanin lokaci komai ya lafa saba'anin abaya da ake kwana ana abu daya,
Zamuci gaba da addu'a in sha Allhu komai zaizo karshe da yardar ubangiji,
Ranar umma anan takwana wajan yarima, shikuwa yarima bacci yawuni yakwana yanayi danko farkawa baiyiba."
Wazirinr gaban hajiya babba a zaune ya gurfana kamar mai shirin yimata sujjada,
Kana ganin hajiya babba kasan a kufule take ranta yana bace sosai,
Hajiya tadubi waziri cikin takaicin dake cinta arai tace waziri kanason 6atamin aikina, kanason cusamun bakin ciki, yaushe har kayi saken da har akakai wannan matakin?
Ashe idan bana saka idanuwa akan lamuran nan shikenan zaku barsu su tabar bare?
Ashe ni ban kai ku tsayamin akan abuba kenna kuyimin abubuwanda suka kamata ba?
Jiya nayi kwanan bakin ciki!
Naji bakin ciki da sako ya isoni wai haalifa yafara magana! Saida ta jaa numfashi mai cikeda huci da zafi tace nadade arayuwata banji bakin irin najiya ba,
Inaso kayimin bayani yaya aka samu akasi haka tafaru?
Waziri yayi kasa da kansa yana fadin Allah ya hyci zuciyarki ranki shi dade Allah yaja zamaninki yaja kwananki da girman kujerraki, bbu ke bhu faduwa har abada, bbu ke bbu kara shiga bakin ciki irinna wanna karon har abada, hajiya tace ba wannan nakeson jiba yaya akayi haka tafaru?
Lokacin sabunta aiki yayi ka sabunta ko baka sabunta ba?
Waziri yafara kame-kame yana fadin ayimin afuwa ranki shi dade tabbas lokacin sabunta aiki yayi amma bansan mai ya sha'afar daniba,
Hajiya babba tace ka sha'afa?
Me hakan yake nufi kenan? Aikin da ake yinsa shekara da shekaru dimun da'iman shine yanzu ya sha'afar dakai?
Advertisement
Waziri ya kwantarda kansa yana fadin Allah yahuci zuciyarki Ayimin rai, hakan bazata sake faruwaba gobe-gobe zan sauka a wajan aikinann,
Hajiya cikin fushi tace yau basai gobeba idan aka sake samun matsala irin haka zanyi maka horonmak bala'in tsanani ,
Waziri yayi kasa dakai yace makamancin haka bazata sake faruwaba ranki shi dade,
Hajiya babba tace da dai yafi, kuma ka taimaki kanka,
Hajiya tace dalilin dayasa banaso na hada maka aiki biyu lokaci daya kenan saboda ka maida hankali akansa kada asamu matsala, daya aikin da mukayi magana dakai ranar asamu wanda zaija ragamarsa amma ba kaiba dan banason sake samu akasi duk karancin ko yaya yake banaso,
Waziri yace yanda kikace hakan za'ayi,
Ran hajiya babba yabaci sosai da sosai batayi zaton wannan sakacin daga wajan waziri ba saboda yafi kowa maida hankali akan aiki,
Waziri yatashi yatafi aranar yayi shirin barin kasar dan sabunta aiki."
Hajiya suwaiba itama anataa wajan hankalinta ba karamin rashi yayiba da labarinnan ya isota, aranar ta nemi yaya hadiza tace mata duk yanda za'ayi ayi kuma duk yanda zata fita tafita taje ta nemi musu wanda zai share musu hawayensu dan wancan yayi sake har yabar yarima yafara magana, aikuwa hakan akayi aranar yaya hadiza tayita yawon nema musu wajanda zasuje a aranar tasamu amma sai dai ba'a gari bane kuma wajan da nisa, tana fadawa hajiya suwaiba washe gari suka kama hanya."
Cikin kwanaki kadan jikin yarima yasake rikicewa jikinsa yayi tsanani dayafi na baya sosai,
Murnar su Umma takoma ciki yayinda labarin rikicewar jikinsa ta isa izuwa ga hajiya babba sai alokacin hankalinta ya kwanta,
Itama hajiya suwaiba anata wajan zatonta nata aikinne yaci har ya dawo da yarima haka,
Waziri ne gurfane gaban hajiya babba kamar wanda yake shirin yimata sujjada, cikin kaskantar da kai dakuma girmamawa yace Allah yaja zamaninki Ranki shi dade, hannu kawai hajiya ta dagawa waziri nufinta ba haka takeson jiba,
Waziri ya fahimci yanda hajiya babba ta dosa cikin son ya birgeta yafara fadin Hajiya anje an sabunta aiki wannan karon aikine akayishi na hakikanin gaske matsalar da muka samu wancan karon baza'a sake samun makamanciyar hakanba,
Hajiya babba ta gyada kai cikin gamsuwa da zancen waziri domin kuwa labari ya iso gareta irin yanda jikin yarima ya koma,
Waziri ne ya katse mata tunaninta da fadin wani hanzari ba gudu ba hajiya wannan yarinya matar sa izuwa yanzu yakamata ace mun san yanda mukayi da ita, tunda har tatafi tadawo hakan yana nufin itama zai iya samun wani taimakon daga gareta toh amma idan muka kawarda dagabaki daya daga gareshi, zamu samu daya daga cikin iyalanmu tashiga a matsayin mata gareshi aikinmu zaifi tafiya yanda mukeso komai zai tafi a yanayin tsaronmu zai kasance babu wata fargaba a tattare damu duk wani abunda muke bukata zamu sameshi cikin sauki, nunfashi hajiya babba taja sannan tace"
Nabar komai a hannunka duk wani abunda yakamata ayi toh ayishi, cikin girmamawa waziri yafice daga wajan hajiya babba."
Umma zaune bakin gadon da yarima haliifaa yake kwance idanuwanta cike da hawaye tana kallonsa cikin ranta sake-sake takeyi tunanin bbu irin wanda baizo cikin ranta ba,
Daga hannuwanta biyu tayi sama tace Allah Allah abunda ta iya fadi kennan kuka yayi kokarin kwace mata saurin toshe bakinta tayi da hannunta a hankali taci gabada rera kukanta gwanin tausayi wannan al'amari na yarima izuwa yanzu yaci ace idanda sabo ta saba toh amma ta yaya?
Ta yaya uwa zata saba da ganin d'anda ta haifa acikinta cikin wahala? Wannan abune wanda bazai taba yiwuwa ba koda idanuwanta sun saba da ganinsa cikin wannan halin zuciyarta bazata iya sabo da ganinsa ahaka ba,
Akoda yaushe idan ta kalli yarima haliifaa cikin wannan hali rayuwarsa ta baya ke sake fad'o mata yarima haliifaa ya kasance saurayi mai cikeda gwarjini , birgewa, shiga rai uwa uba addini da sanin ya kamata, iya kacin wadannan halayensa tayi sabo dasu amma ba wannan halin da take kallonsa aciki ba yanzu,
Jin motsinda tayi ya sanyata saurin hadiye kukanta ta sanya hannuwanta ta share hawayen dake kan fuskarta, da sallama nabila tashigo dakin, umma ta amsa sannan tasaki wani murmushi mai cikeda zallan damuwa, nabila ma ta maida mata murmushin da qaraso tace umma kije ki huta saina zauna a wajansa, rankwafar da kai umma tayi cikin sigar tausayi tace kayya nabila babu wani hutun da zan iya cikin wannan hali ke kije ki kwanta koda baki samu bacci ba kidan huta jiya haka muka kwana ido biyu cikinmu babu wanda ya runtsa,
Sunkuyarda kai nabila tayi kwallar tausayin kansu ya cika mata idanuwa, dukansu sun dawo abun tausayi itada umman da yariiman gabaki daya wani lokacin ma harda shi kanshi mai martaba gashi girma ya kamashi ga wannan al'amari mai tsoratarwa da rikitarwa dake faruwa da magajinsa hawayenda suka cika idanuwata suka sauko akan kumatunta, hawaye sun kuyarda kanta kasa tayi saboda bataso umma taga halinda take ciki amma saida umma ta fahimci yanayinda tashiga
A fili umma tace kiyi hakuri nabila kiyi hakuri bazan gaji da tausarki da baki hakuri ba, hakika wannan itace *
*
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
💞
Advertisement
- In Serial15 Chapters
The Queensguard: An Isekai Love Story
Hundreds of years ago, the Empire of Asgardia ruled all of the Frostlands with an iron fist. The dark elves subjugated the high elves and the dwarves, enslaving them and abusing them to bring further prosperity to the Empire of Asgardia and the dark elf race. One day a high elf warrior led a rebellion to liberate her people from their dark elven oppressors. She was aided by a small group of elite warriors with unyielding loyalty. That warrior would be crowned as the First Queen of the newly established Kingdom of Alfheim, and her loyal band of warriors would come to be known as the Queensguard. Today, the Kingdom of Alfheim is now the most powerful nation in the world, and the tradition of the Queensguard has continued on. Warriors from all over the land aspire to join the ranks, but only a select few will have the honor to be chosen. Tetsuya Miyazaki is an eighteen year old high school boy from another world. A social outcast searching for a purpose to fight for. Chelsea the Fierce is a half-orc orphan, cast aside by the world and saved only by the kindness of a stranger. This is the story of the monster and the hero. An unlikely pair of underdogs and their extraordinary journey into the world of the Queensguard.
8 211 - In Serial50 Chapters
Spirit King
After his sister and around ninety-nine thousand random people around the world disappeared in one day three years ago, Niko’s life had always been revolved around finding her. He was facing dead end after dead end, until one day he was summoned to another world along with ninety-nine thousand other people. Putting two and two together, he came to the conclusion that his sister was also summoned to this world three years ago. This world is filled with danger, and evolving is key to surviving. The evolved lived while those unable to adapt perished. With the hope of finding his sister as motivation, he aimed to become strong in this world of magic, monsters, demons, and gods.
8 222 - In Serial9 Chapters
The Story of JP Starwind, Part 1: A Hole in Heaven's Eye
500 years after the Great Exodus, tucked away in an obscure galaxy where mankind can mend itself in peace, JP Sol Starwind and Danther Minth run from an outstanding gambling debt. But debt is a wolfhound and its owner, Khal Dowin, is a hunter. And, after seven years of running, they have finally been found... or have they?
8 201 - In Serial36 Chapters
Demon Hunters
Far in the future, the last two viable cities in the western hemisphere – Technoburbia and New Baravia – struggle for control over a vast and largely desolate land. Officially they are at war. In practice, the war has been a stalemate for a generation, the disputed frontier between the two city-states never moving. In the city of New Baravia itself, a vast circular concrete wall keeps its inhabitants in, and its refugees out. For its citizens, life is monotonous and unequal, with enormous wealth in the hands of nobles, criminal gangs, and entertainment bosses. It is the last of these that control the hit entertainment show, “Demon Hunters”. A chance, perhaps, for the ordinary man or woman to rise up, and change their fate... This LitRPG novella is based around a futuristic battle-royale situation, partly set in VR, and partly in a post-apocalyptic city. The story features combat and action, some strong language, and lots of great characters that will stick with you! [participant in the Royal Road Writathon challenge]
8 110 - In Serial63 Chapters
Omega A Legacy Reborn
Follow the adventures of Richard and his friends as they enter the popular online virtual game of Omega as they battle against other players to become the best team in the world. As an addition to that, they must discover the history of the Legendary Pieces, legendary artifacts with unique powers. Some sentient, most of them even corrupted by previous owners. Throughout this journey to become the best team in the world, they will have to fight Black Hat and some Grey Hat Hackers, other owners, and even other entities that will try and destroy the game they love or even worse...The World. So, Hop in and watch as History unfolds in this Online adventure. Are You all Ready? Because Here...We...Go! Entering Omega NOW!!
8 213 - In Serial33 Chapters
math class | gwinam x reader
It's my first day at Hyosan High School. The school is nice, and the people seem friendly, as far as I can tell. However, one boy in my math class caught my eye. But why is everyone telling me that he's a bad guy? I mean is he, should I be careful of him? rankings from like ages ago # 1 in #realevents out of 404 stories# 10 in #diary out of 57.5K stories # 4 in #yourpov out of 402 stories # 11 in #femreader out of 4.7K stories # 38 in #onjo out of 438 stories # 4 in #aouad out of 518 stories # 1 in #gwinam out of 324 stories # 12 in #allofusaredead out of 1.2K stories
8 61

