《ƘADDARAR RAYUWA》Ƙ page 67
Advertisement
**
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa
#Follow me on
"
Marubuciyar
*BIBIYATA AKEYI*
* Y'AR FARI*
* YARIMA FAYAD* paid 200
page 67
Ɗakin dake daff da nasu ta shiga ta shinfiɗa hameeda saita ta tabbatar baccin nata yayi nisa sannan tafito izuwa falo, Sadam na ɗauke da hamdan yana masa wasa yayin da shikuma yaketa ɓalɓala dariya kallonsu ta tsaya yi daga nesa gwanin sha'awa, a hankli ta taka ta ƙarasa wajanda suke zama tayi gefensu sannan tace "miƙomin shi yyaa Sadam dare yayi sosai gara shima yayi bacci kamar ƴar uwarsa, ɗago yaron sadam yayi ya yi masan peck a both kumatunsa sannan ya dubeta yace "yaronnan nada sabo sosai bawani daɗewa nayi tare dashi ba amma ya sake dariya kawai yake min, murmushi Sawwama tayi sannan tace"su yara haka suke ko yau suka fara ganinka idan suka sake dakai zaka ɗauka tun dacan sun sanka idan kuma sunada ƙuiwa ko kullum suna ganinka sai sunyi maka ƙuiwa, daɗin daɗawa kaifa mahaifainsu ne dole su sake dakai sosai ba kamar sauran mutane ba,
Miƙa mata shi yayi ta ƙarbeshi ta kimtsashi sannan ta bashi mama alokaci ƙalilan shima yayi bacci kamar ƴar uwarshi ta kaishi ta kwantar dashi saida tayi musu addu'a sosai sannan tafito duk wani abunda yakamata ta tattare saida ta tattareshi suka kulle ƙofa sannan suka shiga daga ciki, Suna shiga sawwama ta isa izuwa ma'ajiyar kaya ta ɗauki kayan bacci ta saka sannan ta ƙarasa gado ta ƙwanta ta lumshe idanuwanta shima rage kayan jikinsa yayi sannan yace "zo muje muyi wanka, Sawwama tace ni bacci nakeji kaje kayi kawai nayi wanka daff zamu fito daga gida,
Kamo hannunta yayi yace"no wannan na dabanne wancan daban noƙe kafaɗa sawwama tayi tace "oh oh nayi wanka bazan ƙara wani ba mura nakeyi"
"aida ruwan zafi zamuyi yafaɗi batareda yajira ta ƙara faɗin wani abunba ya ɗauketa cakk zuwa banɗaki, tsawon lokaci suka ɗauka wajan wanka sannan suka fito, wannan dare gabaki ɗaya sun rayashine a farantawa junasu yaransu basu farkaba sai asubahi, Sawwama tana jiyo kukansu tatashi ta nufi wajansu shikuma ya wuce zuwa masallaci a ɗakin yaran tayi sallah saida ta tabbatar sun koma bacci sannan takoma ɗakinsu tasamu har yadawo daga sallah, komawa bacci sukayi basu suka tashi ba sai 10:00am sai bayan ta farka tagama duk wasu abubuwan da yakamata har izuwa lokacin su hamdan bacci sukeyi, bayan tagama shirya gidan ta haɗe breakfast sannan tashiga wanka tafito sanye da towel wanda iyakacinsa cinya, batayi auneba taji sadam yashigo ɗakin yi tayi kamar bataji shigowarsa tazauna tafara shafa ma lallausan fatar jikinta mai, a hankali takebin kowane saƙo na jikinta tana murzeshi da mai, yayinda Sadam yana gefe yana ƙare mata kallo duk yanda ta sanya hannu idonsa nakai, kasa jurewa yayi ta isa zuwa wajanta hannu ya sanya ta tatsi mayin dake kan dressing mirror ya tsugunna akan ƙafafunsa murza man yayi atafin hannunsa yakai hannun zuwa jinyarta yafara shafa mata mayin amma kamar wanda yake murza fatar da gayya da wata manufa ta daban runtse idanuwanta tayi ta huɗesu akansa sannan ta dubeshi cikin wani yanayi daƙyar ta iya riƙe hannun haɗeda faɗin "yaya Sadam meye hakan ni nafa gama shafa man kaya kawai zan saka, janye hannunsa yayi batareda ya kalleta ba yacigaba da shafa man daga bisani ya janye towel ɗin yayi ƙasa runtse idanuwanta tayi bata buɗeba har yagama shafe kaff illahirin jikinta da man sannan ya miƙe ya dauketa cakk tsillo tafarayi tana faɗin yaya sadam meye haka? Yanzu fa nayi wanka, Sadam bai kulata ba har saida ya idda nufinsa, bayan nan sannan sukayi wanka wani man tasake shafawa ta sanya turare mai sanyin kamshi, kwalliya ba mai yawa ba zallan powder man baki da maskara tasaka ya sake fito da eyelashes dinta dake masu tsayine sai maskara ya sanyasu sukayi kauri, atampha tasaka rigada skirt wanda yafito da illahirin surar jikinta ba ƙaramin kyau kayan yayi mata ba ta ɗaura dan kwalinta ya zauna ɗass yayi kyau gwanin sha'awa,
Advertisement
Duk yanda ta wulga idanuwan Sadam nakan ta, ji yakeyi kamar ya haɗiyeta dan so da ƙauna,
Sai wajan 11:30am kafin sukayi breakfast, lokacin yaran har sun tashi ta wankesu ta shiryasu, tana shirin haɗa musu madara Sadam yace baisan zancenba mama zata bawa yaranshi, haka dole saida ya sanyata ta shayar dasu na tsawon lokaci kafinnan ya barta tabasu madara, kirjinta har zogi suke mata saboda ba halin ta zauna zaice ta shayar dasu koda kuwa ba kuka suke ba, tana gamawa dasu shima kans sai ha ɓullo da wani lamarin na daban wunin ranar Sadam ya sanya ta sake wanka yafi a irga kaman wani sabon aure haka yakejin kansa,
Wuni yayi curr babu yanda ya fita sai Sallah. Shi yama manta da Abida ko sau ɗaya bata faɗo masa arai ba, ya tarkata komai ya watsa gefe Sawwama da yaransa kawai suke gabansa,
Kwana biyun da sukayi tare ba ƙaramin farin ciki suka bawa junansu ba, a wannan lokacin soyayya da ƙauna kawai sukayita shayar da junansu toh ba anan gizo take saƙar ba, saida dare yayi sadam shaff ya manta da zancen wani raba kwana har saida Sawwama taga baida niyyar tafiya tayi masa tuni,
Ɗan karamin tsaki yaja cikin ransa yace "Wai har anyi kwana biyun? A'iya tunanina na ɗauka kwana ɗaya kaman jiyafa kika dawo, girgza kai Sawwana tayi tace "A'a ƙwana biyu kenan da dawowata yau yakamata ka koma, da sanyin jiki Sadam yace " lallai lokaci yana tafiya banyi auneba har lokaci yayi,
Yafaɗi haɗeda cigaba da zamansa an ɗauki lokaci taga baida niyyar tafiya ya sanya taƙara yimasa tuni miƙewa yayi rainsa ba daɗi, Sawwama wacce itama takejin ranta duk babu daɗi ta miƙe ta riƙo hannunsa kallonta yayi ganin yanyinta ya canja ya sanya ya sakar mata murmushi ko zata saki ranta, murmusawa itama tayi ya janyota jikinsa ya rumgume ɗago fuskarta yayi ya haɗe bakinsu wane ɗaya ya daɗe yana kissing nata sannan ya saketa har bakin ƙofa ta rakashi sannan ta kulle haɗeda yimasa fatan alkahiri ta juyo izuwa ciki,
Kashe duk wasu na'urori tayi tashiga ɗaki itada yaranta addu'a tayi musu ta ƙwantar dasu ta kwanta itama,
Kewar sadam ta isheta hakan yasa ta jawo yaranta ta rumgume ahaka bacci ya ɗauketa."
Sadam yana shiga gida ya tararda Abida ta cika tayi famm jiransa takeyi, yana shiga yayi arba da ita ya ɓata rai dama tun ranar bai ƙara sakewa da itaba, kai tsaye ɗakinsa ya nufa tabi bayansa tana faɗin "sai yau kaga daman dawowa? Ai ko zaka ka ajiye acikin gidannan zaka dawo kaduba yanda ka barta bare mutum, kuma matarka wacce nakeda hakki akansa wallhy Allah bazai barka ba mugu azzalimi, Sadam da ɓacin rai ya dubeta yace duk mai yayi zafi haka? da har kike bina da mugayen sunaye akwai wani abunda kike buƙatane agidannan wanda nafita ban tanadar miki ba?
Kona barki da yunwa?
Duk wani abu da zaki buƙata na ajiye miki shi, har menene haka tsagwaran rashin kunya zakizo ki nunamin?
Abida ta murguɗa baki tace toh ai ba abinci bane kawai matsalata ba tunda ba agidan yunwa ka ɗeboni ba,
Kuma bakakai nayi maka rashin kunya ba aiba girmata kayi ba ta ƙarasa maganar tana riƙe ƙugu da turo baki, dariya Sadam ya saka wanda saida yasa ta tsaya tana kallonsa, arayuwarsa ya daɗe baiga shashasha irin abida ba ko bai girmeta ba a haife amma darajar aure Allah yabashi girman"
Ya lurada cewa itaɗin sokuwa ce ta karshe,
Advertisement
Ɓata rai tayi tace kayimin laifi kuma kanamun dariya mahaukaciya ka ɗaukeni?
Dariya tana cinsa ya girgiza kai yace A'a, tace toh tunda ba hakaba kabani haƙuri zan haƙura, Sadam yace toh kiyi haƙuri, murmushi tayi ta zauna gefe kusadashi tace na haƙura amma da sharaɗi ɗaya,
Menene sharaɗin ina jinki, A'a saika yarda da sharaɗin kafin na faɗa, yace A'a tayaya zan yarda da sharaɗi batareda nasan wani iri bane faɗi ina jinki,
Sharaɗin shine nima zakamin ciki kamar yanda kamata ta haihu nima na haihu,
kallonta Sadam yakeyi rashin wayon Abida har yayi yawa sakarcine da ita gashi itakuma ba ƙaramar yarinya ba, nisawa yayi yace" toh naji amma sai kin bani haƙuri nima dan abunda kikayimin a ranar friday banji daɗinsa ba rains ya ɓaci daga dawowarmu kika ɓatamin rai wanda acan ba haka kikemun ba, canjawa Abida tayi takoma wata salaha tace "ai shiyasa nace maka muzauna acan karmu dawo zamanmu acan yafi daɗi kaima baka ɓatamun rai, iska sadam ya furzar yace ki fahimci wani abu inada iyali anan inada mahaifa ina buƙatarsu kusa dani ke baki buƙatar mahaifanki kusa dake?
Yatsina fuska tayi tace har indai zanzo ko sau ɗayana ashekara nagansu ai shikenan bbu komai,
Sadam yace "ni awajena akwai komai,
Nidai yanzu mubar wannan maganar kawai nima kamin ciki, toh yace haɗeda aikata abunda takeso kawai dan gudun fitinarta."
Washe gari kuwa itama ta tayarda rikici wai bazai fita wajan Sawwama ba itama dole tarama abunda tayi mata,
daƙyar ya zare yaje yaga Sawwama da yaransa dan bazai iya haƙuri ba idan yana nesa yayi juriyar rashin ganinsu yanzu yana kusa bazai iya ba."
Bikin najeeb yanata ƙaratowa hidima kawai sukeyi basa samun zama su dukansu Sawwama da abida bawani samun ganinsa sukeyi ba sai lokaci-lokaci,
Sawwama ta fahinceshi yayinda abida ta ɗaura hakan akan yana zuwa wajan sawwama ne shiyasa baya samun lokacinta,
Tunda aka fara bikin najeeb wata ƙawar amarya ta maƙalewa Sadam sai guje mata yakeyi amma kamar chewing gum tadawo masa wata bini zai-zai,
Tunda najeeb ya fahinci haka yayiwa amaryarsa magana cewa tayi mata magana dan Sadam matanshi biyu kuma yasan abokinsa mata biyu ma banda ya zama masa done da bazaiyi ba,
Shikuma Sadam dalilin dayasa wasu lokutan yake sauraronta saboda kasancewar sunanta hafsa, shikuma a duniya baya fata wata rana tazo da zai iya wulakanta mai sunan, sonda yake yiwa Sawwama bana wasa bane shiyasa duk wani abunda ya danganceta yana girmamashi, amma ya kuɗirta aransa biki kawai za'ayi agama, ana gamawa ko hanya bayason ya sake haɗawa da ita dan Abida Sawwama mai shiru-shiru da haƙurima take caja masa kai akanta bare ya ƙaro wata,
Amaryar najeeb da kanta tasamu kawarta tayi mata bayani, da mamakinta cewa tayi ko mata huɗu ke gareshi har indai zai saki ɗaya ya aureta toh zata aureshi bare mata biyu, ita taji tagani tana sonsa ahaka,
Najeeb yayi mamakin jin kalamanta dakansa ya sameta yace "hafsa ki fahimci wani abu koda kin aureshi bazaki taɓa samun soyayyarsa ba saboda mace ɗaya yakeso, ita kanta ta gidan takasa samun soyayyarsa saboda hankalinsa naga Sawwama, Dariya hafsa tayi tace ikon Allah tsawon lokacin aurensu takasa samo zuciyar mijinta ya sota lallai wannna sakaraAr mace ce bata iya takunta ba, kabarni kawai na aureshi a baya sona kowa ta iya allonta saita wanke, ganin tayi nisa ya sanya najeeb kawai ya rabu da Ita."
Tunda aka fara bikin sadam baije da matars ako guda ɗaya ba sai ranar wuni dafarko yaso yaje da kowacce ranarta daban sai hakan baiyiwuba,
Gidan Abida ne yafi kusada gidan bikin kawai sai yabi yafara ɗaukan sawwama sannan yawuce gidan Abida, yana isa ya kirata ya sanar da it aakan tafito, tafito taci wanka da kwalliya sai wani taku take tana zuwa taja ta tsaya cakk ita duk tunaninta da ita zai tafi sai taga Sawwama, ƙololon baƙin ciki ya tokareta kamar ta sa hannu akayi tayi ihu takeji,
Sadam yace "shigo mutafi mana ke kaɗai muke jira, kasa haɗiya baƙin cikinta tayi tana faɗin waye zai zauna abaya? Ni? Takoma baya saina shiga mutafi, batareda Sawwama tajira sadam yayi magana ba ta ɗebi ƴaƴanta ta buɗe ƙofa takoma baya, tissue ta sanya ta goge yanda Sawwama ta zauna sannan ta shiga, Sawwama ta gaisheta ko kallo Sawwama bata isheta ba bare yaran ganinsu kaɗai baƙin ciki take ƙara mata,
Sadam ya Shanye fushinsa ta hanyar furzarda huci yajuya yadubi sawwama ya sakar mata murmushi itama ta maida masa, yaja motar suka tafi,
Gidan Najeeb suka nufa dan anan za'ayi events na buɗar kai, suna isa Sadam ya fito ya buɗe ƙofar Sawwama ya karɓi hamdan sannan itama tafito ɗauke da hameeda, sunyi matukar kyau sosai Sawwama sai wani yalyali takeyi ba wata kwalliya tayiba amma tayi matuƙar kyau,
Saida yakaisu har cikin wajan yabata hamdan kafin ya juya dake anyi decoration wajan yayi kyau sai suka zauna amma kowa gefenta daban,
Kusada wasu ƴan mata Sawwama tazauna tana iya juyo hirarsu kaɗan-ƙadan wata daga cikinsu taji tana faɗin hafsa ga man ɗinki can ya iso fa kinga yanda yayi kyau? Yanda kasan shine ma angon da kansa, miƙewa hafsa tayi tana faɗin "ai Sadam ya haɗu bari naje na sameshi kona ɗanji sanyi araina zamana anan jiransa kawai nakeyi, ambatar sadam da tayi ya sanya gaban Sawwama faɗuwa rass, tanaso ta juya taga ko Sadam mijinta ake nufi amma fargabar abunda zata gano ya hanata,
Kasa jurewa tayi saida ta kalli wajanta wannna hafsa ta nufa, tabbas Sadam ɗinta ta nufa, Sadam mijinta dishi-dishi take gani Sadam ta hango yana saukewa hafsa sinƙi-sinƙin murmushi tun kafin ta ƙaraso, da rangwaɗa ta isa zuwa Sadam,
Tana isa tace "kayi wuyar gani man, tun datsu nake jiranka akwai wata muhimmiyar magana da nakeso muyi dakai,
Sadam yace gani nazo yanzu zamu iyayi ko sai angama events?
Hafsa no no muyi yanzu kafin amarya da ango su ƙaraso, amma nan yayi cikin mutane ko zamu ɗan keɓe? Why not yafaɗi haɗeda binta suka bar wajan, duk wannan abun akan idon Sawwama, nan danan tafara jin jiri shin me hakan yake nufi? Sadam aure zai ƙara? Dama yanada budurwa? Shine yake nuna mata cewa ta isheshi rayuwa,
Sunkuyarda kanta tayi kawai dan tanajin babu daɗi, hawaye yana bin fuskarta,
Abida duk batasan wainar da ake toyawa ba ta kifa kanta a waya sai danne-danne takeyi."
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
💞
Advertisement
- In Serial69 Chapters
The Orphan Fox
Arin, an 8 years old boy, grew up as an orphan in Switzerland. Thanks to the Orphanage he lives in he could count as a lucky child. Sadly his legs were weak which could already be called completely crippled. Understanding his situation he still tries to do his best and uses his hands to craft all kinds of different objects. One day, just as he was about to join the other kids in a game in the garden, an event occurs that send him and the other on a Trip, none of them would easily forget.
8 85 - In Serial6 Chapters
Contact First
2039 - Earth A narrow beam energy signal appeared aimed squarely at earth from the TRAPPIST system. The communication consisted of a layered set of repeating data over several thousand wavelengths. Over the next few months scientists discovered that the lower wavelengths carried an encoded numerical language which could then be used to interpret the more complicated messages carried on the higher wavelengths. After half a year of painstaking work the signal was fully decoded. It described a small satellite launched along a precise trajectory towards the fourth planet of our solar system. Included was a package of advanced research that humanity would need to have ready in order to receive the satellite and decelerate it safely. The alien data provided the kick that humanity needed to turn from petty squabbling and unite to explore the final frontier. Major government and corporate leaders worked together to create the framework for the United Federation of Sol. UFS spaceports went from scaffolding to daily launches in every major city around the globe. Ships floated like dandelion seeds, spreading on solar wind to grow into colonies. 2397 - Mars orbit, Egeria Station The command center was a hive of activity as checks were conducted and systems initialized. Scientists flitted by like mayflies as communicators beeped and holoscreens spat out green tinted readouts. Nervous energy was thick in the air as everyone anticipated the culmination of over three hundred years of work. Massive fusion reactors under the planet's surface thrummed with barely restrained power as energy fed into a gleaming metallic maze criss crossing the planet. Metal fingers reached up, overshadowing the mighty olympus mons and trying to grab the stars. All over the solar system, people quickly turned to look as gigantic energy lances shot from the dusty fourth planet. Two years later. The same people that clapped loudly at the successful activation of project Hermes now wait with baited breath. A silver capsule trailing bright photonic sails is captured by a net of grav beams and guided with care bordering on reverence into the station. Holoscreens across the headquarters project an image of the sleek craft settling in the bay. Data connections are established and the holoscreens blink to white. Slowly an image forms on the screen. Across the headquarters people stare in wonder as a wholly alien face stares back. "Contact established. Welcome to the universe."
8 155 - In Serial31 Chapters
Beware of Zombies
Hey, I'm Chase Cross, the main Protag, in this zombie flick. You may be wondering what this is about and that is a good question. See I was just an ex-gangsta trying to go clean. Running a Computer Cafe with Virtual Reality Sets for the low low. I thought I was doing an amazing job, I was making above what I was expecting. The place kept itself busy, there wasn't much gun voilences as I thought it would be on a main street. To top it off, I was going to ask this beautiful nerdy girl out on a date.. And then this thing happen. The world decided it wants to nom nom on people's faces. My world was ruin from day one of the mass festival, like did I really care that someone was eating someone else? No, I did not. Like its fine if you went to a apples bs or something and order cripsy steak but they give you a rare.. It's the same damn thing for zombies. Zombie Lives Matter too.. Which is why I am a proud supporter of staying away from populations capable of turning into one and nomming on me.. Well, given that I have some kind of mutant power and that local government want to draft those of my kind to fight against the zombie mutant kind. Well, how quaint can life get?
8 74 - In Serial30 Chapters
Perfect Wish
If you are granted your perfect wish which was a RPG like system with the power to live in fiction worlds. How would you live? Would you become a hero and slay dragons and demons or would you become the villain and take the worlds for yourself. Or maybe, you just go for a life a bit more peaceful than that. Disclaimer: I don't own existing worlds or characters.
8 238 - In Serial16 Chapters
The Monster App Version 2
"Humans! Your world will end on the first day of the new year. If you wish to survive the apocalypse, receive my egg, fertilize, hatch, and evolve the creature within. Unimaginable horrors await those who fail at this simple task. Know that what is coming is for my amusement. Everyone will soon fear the name, The Majestic Pink Fluffals the Third!" This is the alternate version of the Monster App. Selvaria is the Co-author & Editor of the story.
8 54 - In Serial85 Chapters
c r a c k (BNHA chat fic) |Under New Ownership|
(cover : https://pin.it/2DMg4i2 ) c r a c c h e a d sLots and lots of cursingI wonder if the people who work at Wattpad know what kind of BULLSHIT is on their siteLol thanks for 1k reads ig
8 249

