《ƘADDARAR RAYUWA》Ƙ page 68
Advertisement
**
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa
#Follow me on
"
Marubuciyar
*BIBIYATA AKEYI*
* Y'AR FARI*
* YARIMA FAYAD* paid 200
page 68
Tsawon lokaci suka ɗauka a wajan basu fito ba Sawwama ta zuba ido har tagaji, hawaye ne kawai yake zirya a kumatunta, har aka fara event idon sawwama yana kan yanda sukabi, sunfi 1hour wajan kafin suka fito, bata iya karantar yanayin da suke ciki ba, kawarda kanta gefe tayi daga nan bata sake ɗagowa ba, tana jiyo hafsa ta iso wajan zamanta ta zauna ƙawayenta sai gwaɗa masoyinta sukeyi yayinda ita kuma tanata kinibibi, baƙin cikine ya cika Sawwama ta miƙe ta ɗebi yaranta da suke kujerar kusada ita, tana shirin ɗaukan jakarta ya sanya hannu domin ɗaukan hamdan ɗan razana tayi ta juyo idanuwanta ya sauƙa akansa murmushi ya sakar mata tayi saurin kawarda kanta ta sake masa hamdan ta ɗauki jakarta batareda ta kalleshi ba ta bar wajan can gefe taje tazauna yanda ko kallo su hafsa bazata yiba bare ta jiyosu,
Binta wajan da tazauna yayi yana tambayarta abunda yafaru, cikin tsantsar nuna kulawa yake faɗin me yasameki? Naga yanayinki ya canja
Wani abunne yafaru?
girgiza kai kawai tayi
rage tsayinsa yayi sannan yace
"koh zaman wajan ne yayi miki wani iri? Sake girgiza masa kai tayi zai sake mata wata tambayar aka nemi ganin Sadam abokin ango, dafa ta yayi yace ina zuwa yanzu zan dawo saina kaiku gida idan zaman wajanne baiyi muku ba, batareda yajira amsarta ba yajuya yayi ciki, tana jiyowa Mc ya sake neman ganin ƙawar amarya hafsa a,
Hafsa tafito cikin taku ta isa izuwa wajan ta tafi da hankalin maza dayawa amma banda sadam wanda take nufarsa, shi hankalinsa yana wajan Sawwama tunanin canjin yanayinta lokaci guda yakeyi,
Bai ankara ba yaji hafsa tazo daff dashi tana sakar masa murmushi yaƙe yayi mata sannan yaja da baya domin sanin idon matansa yana kansa,
Abida alokacin dataji ankira Sadam hankalinta ya koma wajansa har zuwan isowar hafsa gareshi zaro ido tayi a fili tace yau naji shegiya cikinsa data shiga da take wani zuwa kusa dashi, huci tafarayi tanaji kamar ta isa wajan ta wanke fuskarta da mari,
Sadam bai wani tsaya a wajanba dan hankalinsa gabaki ɗaya na wajan Sawwama yakoma gareta, duk yanda yayi Sawwama tafaɗa masa abunda yake damunta taƙi yayi da ita yasake kuma taƙi sakewa,
Marairaicewa yayi yace Sawwamaty wai me yafaru ne? Bakida lafiya ne? Wani abunne yake damunki? Yanata jero mata tambaya amma taƙi kulashi,
Sadam yashiga damuwa sosai ya ajiye yaran a kujera can daban ya riƙota kamar wanda yake shirin maidata cikinsa,
Najeeb daga yanda yake yana kallo abunda yake faruwa ya taɓa amaryarsa yace "kinga abunda nake faɗawa hafsa amma taƙi yarda koh?
Sadam bazai taɓa sonta ba mace ɗaya yakeso arayuwarsa itace waccan ya faɗi yana nuna Sawwama sannan ya ɗaura da faɗin kuma ni ina bayan Sadam akan abunda yakeso dan Sawwama ta cancanci soyayya suna rayuwar farin cikinsu kar tazo ta tarwatsa musu farin cikinsu, duk wannan maganar da yakeyi yana yinta ne cikin raɗa irinta amarya da ango,
Amaryar Najeeb tayiwa kawarta alamu da tazo ta rangwaɗa tatashi ta isa izuwa wajan dan gani take duk ƴan matan wajan baya kamarta, Amaryar najeeb ta riƙo hannun hafsa tace kalli can gefe zakiga Sadam da matarsa hafsa ki kalli yanda yake kulawa da ita yana sonta sosai ki hakura dashi dan Allah ki nemi wani karki shiga cikinsu ki tarwatsa musu farin cikinsu,
Harara Hafsa ta wulla mata tace "ni nace miki farin cikinsu zan tarwatsa? Yaushe mukayi hakan dake? Nima zaman aure zanyi kamar yanda kowa yake zaman aure, Soyayyar da mace take nunawa miji da wanda miji yake nunawa matarsa nima shi nake muradi, shin ina laifina anan? Ko tunda ke kinsamu kinyi aure kar wasu suyi?
Advertisement
Duk wannan maganar da takeyi idanuwanta yana kan Sadam da Sawwama wacce ya maƙale kamar zai maidata ciki sai siriritata yakeyi ita kuma taƙi faɗa masa damuwarta dan tana buɗe baki da niyyar magana kuka zata sanya itakuma bataso tayi kuka cikin mutane dama agidansu ne saita zuba masa shagwaɓarta da sangartakarta iya son ranta ko zaiji tausayinta ya rabuda wannan yarinya mai ido a tsaitsaye,
Ga mamakin Najeeb da amaryarsa kawai sai ganin hafsa sukayi tafarayi zuwa wajanda Sadam da Sawwama suke da sallama ta isa wajan ta sanya hannu ta ɗauki Hameeda ta juya wajan iyayen da murmushi, da mamaki Sawwama take kallonta shima Sadam ɗin hakane a wajansa ya ɗauka sun gama maganar da zasuyi da ita, mai kuma ya ƙara kawota wajansa?
Baƙin ciki yasanya Sawwama lafewa ajikinsa ta kwanta luff dan batason ganinta gabanta sai faɗuwa yakeyi,
Hameeda tafara turjewa tana miƙawa iyayenta hannu jijjigata hafsa tafarayi tana faɗin kiyi haƙuri baki sanni bane amma soon zamu saba nima zan zama mamarki, Sadam ya miƙa hannu zai karbi hameeda Hafsa tayi saurin jada baya tace no barta kawai a haka zamu saba,
Sawwama dai batace komaiba amma zuciyarta sai bugawa takeyi, Sadam ya nisa sannan yace no kawota kawai tanada kuiwa bazata yardaba kuma a'ina zaku saba? Bayan angama bikinnan idanba wani ikon Allah ba banajin zaku sake haɗuwa, wata ƴar ƙaramar dariya hafsa tayi tace "Toh ai dama ni ikon Allahn nakeso yayi aiki akanmu, tadubi Sawwama tace antyna ina wuni?
Sawwama ta ɗago batareda ta amsa ba ta dubeta wai ita take cewa anty itada ko shekara ashirin batayiba ƴar kusan ishirin da biyar take kiranta da anty, batareda ta amsa ba ya miƙa hannu ta karɓi hameeda domin lokacin tafara kuka tana karɓanta kuma tayi shiru, Jin Sawwama tayi shiru bata amsa gaisuwar Hafsa ba yasa sadam yasha jinin jikinsa tabbas Sawwama tasan wani abu dake gudana tsakninsu da hafsa shin ko dalilin canjawarta kenan?
Da sanyin jiki Sadam yace"sawwamaty i can explain ba wani,,,, miƙewa Sawwama tayi batareda tajira ya ƙarasa maganar ba atakaice tace zan shiga daga ciki na shayarda ita, ko jira batayi ba ta wuce tabarsu a wajan,
Sadam ya dubi hafsa yace kinga abunda kika jawo koh? Bantaɓa kallon Sawwamaty a irin wannan yanayin ba, a yanzu koda inada niyyar aurenki nafasa barema banida niyya Sawwama kaɗai ta isheni rayuwa, murmusawa tayi tace "inada jaa a wannan zancem domin bahaka yake ba idan ita kaɗai ta isheka rayuwa meyasa ka auri har mata biyu?
Ita ɗayar baka sonta ne ka aureta? Kamar yanda ka aureta baka sonta haka nima zaka aureni amma sai dai ni ba irinta bane, bazan taɓa yarda nayi wannan zaman dakai batareda kafara sona ba,
Sonda kake ikirarin kana yiwa matarka shi, shi nakeso na kwace idan kuma hakan bazai yiwuba toh ko gida biyu ka raba mana shi tunda wancar sakara ce,
Da mamaki Sadam yake dubanta yace"sakara? Sakara ba kikace? matata kika kira da sakara a gabana?
Toh bari kiji ko inason matata ko banasonta babu wanda zaici mata mutumci na ƙyaleshi ko waye kuwa, kuma duka mata ina sonsu,
Soyayyar danake musune ya sanya na auresu, kekuma rashin sonda nake miki ya sanya bazan iya aurenki ba, ko sake miki da kikaga nayi dalilin sunan kine ba sunaba ko takalmi sawwama tayi amfani da irinsa bazan iya wulakanta shiba bare sunanta, amma jin ƙudirinki akanta yasa naji kin zama wata abun ta daban, baki cancanci sunanda aka sanya miki ba sam, ki canja sunaki domin masu suna Hafsa sunada tsarkakekkiyar zuciya, sannan ki zama mai kamun kai kunya da kawaici ita mace ba'asanta da wannan halin naki ba,
Advertisement
Idanuwanta sun canja ranta ya ɓaci sosai dan atunaninta yanda sadam yake sake mata zata iya faɗin maganarda takeso akan matarsa ya share, kokuma tana tunanin har isarta takai ta zata iya wulakanta masa mata ne oho?
Zaman jiran Sawwama yakeyi a wajan domin akwai jakarta gakuma hamdan, ran Sadam ya ɓaci sosai dan laifin kansa yake gani dahar ya sake mata haka tasamu bakin magana akan matansa, wai me wasu ƴan matan suke ɗaukar kansu ne? Shikenan daga namiji ya sake miki natarsa ta gaza ne? Idan ya nuna yana sonki shikenna saiki ɗauka bayason matarsa ne ya sanya yazo gareki, wato ita mace wani ɗaukaka da daraja Allah yayi mat, darajarta bazai taɓa misaltuwa da matarda baka kai ga auranta ba, Koda kuwa bayason matarsa,
Neman waje tayi ta zauna a gefensa tama rasa abunda zata faɗi don jikinta yayi sanyi duk wani rawar kamta ya sauƙa, haƙuri tafara bashi tana faɗa masa irin soyayyar da take masa bazata iya rabuwa dashi ba bawai faɗi hakan dan tozarci ga matarsa bane sonsa ne kawai yake tunzurata" Sadam bai ƙara tanka mata ba,
Har aka tashi daga event ɗin Sawwama bata dawoba ita kuma hafsa bata tashi a kujerar da take ba mutane suka fara watsewa sai a sannan Abida tafara neman yanda Sadam yake,
Juyawa tayi ta waige-waige can ta hangoshi zaune buduwar ɗazu na zaune a gefensa sai magiya take masa, ƙugu abida ta riƙe tana faɗin eh lallai wata yau tanaso nayi mata rashin kirki acikin wajannan da azama ta nufi wajansu tana zuwa ta tokari kujerarda Hafsa take aikuwa tayi tagal-tagal zata faɗi sadam ya damƙe kujerar ta tsaya cak da masifa tadubi Abida tace ke mahaukaciyar inace ko bakya kallo ne?
Abida tace au ban ganki bane sorry nazo wajan mijina ne so banyi tunanin akwai wata zaune kusada shiba,
Hafsa ta nanata mijinki! Kece ɗayar matar Sadam kenan?
Hafsa ta juya tace man wannan ce matarka ɗayar? Kiff abida ta buge bakinta tace ubanki ne ba man ba mijin nawa ne ya dawo man ɗinnaki?
Miƙewa hafsa tayi da bala'i tace ke har asuwa da zaki bigen baki? Toh matar son ma tashi tayi tabarni dashi bare keh ta nuna Abida tasake faɗin hhat izuwa yanzu kin kasa sanyashi ya soki"
batayi auneba tayi sauƙar maruka akan fuskarta both side,
Abida tana huci tana surfa bala'i gata dai mace iya mace ga ado dukiya da ilimi uwa uba tanada kyau amma sam abida batada aji, huci take yi tana faɗin agidan uwarki ne yace miki baya sona? Kin sanni wacece? Kinsan waye babana? Sai nayi maganinki,
Yawanci mutane sun watse a wajan sai tsirarru suna ganin abunda yake faruwa suka yiyo wajan harda amarya da ango,
Hafsa riƙeda kumatu mamaki ya cikata abida tana huci tana faɗin kaɗanma kika gani har indai akan mijina ne, Sadam yayi shiru acikinsu yaras a zaiyi backing Abida da ake son kwacewa miji ko Hafsa da tasha maruka, matar Najeeb taja ƙawarta tana faɗin meyake faruwa, hafsa bana faɗa miki ba saida nace karki fara,
Hafsa cikin zafin rai tace ni toh mai nayi? Menene laifina danna so shi, shin ba'a aure ita za'a aureta?
Najeeb yajuya ga Sadam yace baka ganin me yake faruwa ne bakaza kulasu ba?
Sadam yace "inama gani toh mai zance musu?
Kasan dai bazan goyi bayan wata akan matata ba, tunda naja mata kunne tun farko banso abun yakaiga haka ba, Yajuya ya dubi hafsa yace "kiyi hakuri da abunda Abida tayi miki, yana faɗin haka ya tashi da hamdan a hannunsa yabar wajan, kowannnsu baki sake suka bishi da kallo,
Sawwama tana kallon duk abunda yake faruwa, tun daga tashinta izuwa abunda yafaru da Abida, bayan tashinta abunda ya bata mamaki shine yanda taga Sadam yaja ya zauna kuma bayan ya fahimci ranta abace tabar wajan a tunaninta zai biyo bayanta, Sai taga akasin hakan domin shi yana zaune da Hafsa tana masa magana, har abida tazo ta samesu"
Yanata duban Sawwama bai ganta ba baisan kuma yanda tayiba, itakuma tana ganin miƙewarsa ta shiga gefen flowers tazauna idan ba lura akayi sosai ba baza'a taɓa sanin da wata a wajanba."
Najeeb haƙuri kawai yake bawa abida dan da gaske son sake dukan hafsa takeyi, daƙyar suka iya shawo kanta ta haƙura ta bari akaja hafsa daga wajan,
Ganin yaduba ko'ina bai ganta ba ya sanya ya kira wayarta kamar bazata ɗaukaba saida yakusa katsewa takai hannu zata ɗauka sai kuma tafasa tabarshi ya katse a silent tasaka wayar saida yakira sau 4 tana gani miƙewa tayi tafito daga wajanda take yana hangota ya isa wajanta yana faɗin ina kika shiga? Nayita kiran wayarki bakiyi picking ba! Batareda tabari sun haɗa ido ba tace ina can wajan tana faɗin haka ta raɓashi tawuce, bag ɗinta tabi taɗauka sannan tayi jikin mota, gabaki ɗaya jikin Sadam yayi sanyi baitɓa kallon Sawwama a wannan yanayin ba ko lokacin daya sanarda ita Abida zai fara sure bata nuna damuwarta ba, bayanta ya juya yabi har zuwa jikin mota ya sanya key ya buɗe tashiga ta zauna a baya ya miƙa mata hamdan,
Komawa yayi ya nemo Abida sannan ya dawo suka tafi a hanya ko tari mai ƙarfi Sawwama taƙiyi yayinda Abida taketa huci tana surfa bala'i,
Sadam ya tsaida motar can gefen titi yace "ya'isa haka abida tun datsu kike abu ɗaya, bakiga ƴar uwarki ba ko uffan batace ba kuma ita ma taga abunda kika gani,
Harara abida tajuya ya watsawa Sawwama wacce ko kallonsu bata yiba iyakacin kunnuwanta kejin abunda suke faɗi,
Juyawa tayi ga Sadam tace ni b aƴar uwata bace, kuma ai dama ba zaka haɗani da itaba, idan tayi rigima dasuma itace zata kwana ciki saboda ita ba ƴar kowa bace nikuma fa?
Zanyi abunda naga dama kuma nakwana lafiya, kuma hakan datayi ma alamu ne na bata sonka ai macenda keson mijinta itake kishinsa,
Sawwama wacce maganganun Abida suka fara isarta ta runtse idanuwanta duk yanda takai ga sanyin zuciya yau zuciyarta ƙuna take mata da wanne ɗaya zataji? Da waccar yarinyar koda baƙaƙen maganganu irinna Abida?
Sadaam cikin fushi yace "ya'isa haka Abida idan kinyiwa Hafsa na kyaleki ita ba kowa bace awajena bazan dauki cin fuskarki akan Sawwama ba, taɓe baki tayi tface"gaskiya na faɗa ko kaso ko kar kaso kasani cewa itaɗin bata sonka macenda keson mijinta ita ke kishinsa"
buɗe idanuwa Sawwama tayi tafara magana "shin tozarta mijinki acikin mutane shine kishi? Abunda kikayi ba kishi bane, Ni nasan me nakeyi bazan fita waje ina hauka ba,
Daga Sadam har Abida suke baki mamaki fall aransu, dukda bada faɗa tayi maganar ba amma Sadam bai taɓa jinta ta maida martanin magana ba, duk kuwa abunda za'ayi mata bazata taɓa tankawai ba,
zagi Abida zatayi Sadam yace idan kika kuskura kikayi zagi zan sauƙeki anan, Nagaji bazan iyada wannan masifar taki ba,
Maida kanta gefe Sawwma tayi tace"inada uzurinda zanyi agida ko zamu iya tafiya yanzu?
Ajiyar zuciya Sadam ya sauƙe yajuya yafara tuƙi
Abida yafara sauƙewa sannan yawuce yakai Sawwama ko waiwayowa batayiba taɗauki hameeda da jakarta tashiga cikin gida,
Hamdan ya ɗauka ya shigar dashi ya sameta tana shirin zama miƙa mata Hamdan yayi bata ƙarbeshi ba tashige ɗaki, da kallo yabita yana mamakin abunda idonsa yau yake gane masa gameda Sawwama,
Shin dama Sawwama zata iya fushi dashi?
ɗakin yabita ya samu tana ƙokarin shiga banɗaki bai hanata ba ya zauna yana jiran fitowarta,
Wayarsa ce tafara ringing yana dubawa yaga Najeeb dannawa yayi ya kara akan kunnensa,
Daga cikin wayan najeeb take faɗin ina kashiga? Naduba ban gankaba ko katafi ne?
Sadam yace "eh nakaishu gida ne, Najeeb yace kabasu haƙuri dan Allah abunda yafaru banji daɗinsa ba, Sadam yace bbu komai kabawa matarka haƙuri, Najeeb yace kafuto kazo dan Allah bazanji daɗi ace baka wajan za'a rakani ba, Sadam yace nikam nashiga gida yanzu kayi haƙuri Najeeb bazan samu fitowa ba,
Magiya najeeb yayita yiwa Sadam har saida ya yarda zaije, yaran ya ɗebo ya zubawa Sawwam akan bed ya wuce raka ango."
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
💞
Advertisement
- In Serial58 Chapters
Primordial Majesty (原始神)
Among the countless stars, at the highest level of nirvana, there was mystical place known as the Jade Heaven Land. As the grand Imperial Commander of Heaven, Shen Qin was worshiped for his cultivation talent and tremendous achievements in the paths of Dao; being one of the guardians who maintained order in the immortal plane. However, on a certain fateful night, in order to chase down and eradicate an ancient god who had heavily sinned, Shen Qin had to pay an immense price and was thus, godly wounded. With his life hovering between immortality and eternity, the will of life inside his tranquil heart, which had been tamed through millenniums, began to once again burn fiercely… Schedule for now: N/A My blog at https://ninedream.wordpress.com/ Support my novel on Patreon! https://www.patreon.com/ninedream Status: Ongoing, Active
8 193 - In Serial10 Chapters
The Demon King's Seventeenth Wife is Scary
Tao Jinghua [Crystal Flower], the deadliest and scariest Assassin to ever walk the earth, unknowingly, give up her life to save a city that is being purged. What she never know was how she died.... or so she thought. She herself didn't die, however, in her last minutes of helping a Taoist believer to safety, she accidentally swallowed a pearl and black out. When she wakes up, she found herself in the body of another existence with the same name and gender but different in look girl who is the 29 daughter of a Pottery family. Okay, fine. I don't need to live in a rich family to be happy. Okay, fine. I don't need people to say that I am not pretty. Huh? Wait, what? Is my fiancee dead? What? Could I cultivate to be immortal shall I wished it? What? You want me to marry the Fifth Princess?! Are you sure it's a princess and not a prince? What? The Demon King want me as his wife? Wait a second, first of all, who the hell are you, people?!!! Genres: Xianxia/Xuanhuan, Romance, Action, Drama, Martial Arts, Supernatural/Fantasy, Comedy PS: The cover photo does NOT belong to the author. If the owner wishes for the author of this fiction to take the photo/picture off, please PM the author.
8 112 - In Serial37 Chapters
Third Death
What happens when the Queen of the Dead, is dead? Necromancy might be magic but it can't fix everything. It can't pull the country out of debt, or heal relations between the splintered powers in Apera. Enter Vision. She's an unassuming thief, except that she happens to bear an uncanny resemblance to her missing mother, the Queen of the Dead herself. Being a woman on the streets was hard enough before people started to recognise her. Now, anything might happen.
8 140 - In Serial22 Chapters
Terror Infinity- Absolute
“Want to know the meaning of life? Want to live… a real life?†The world changes when you click YES. In God's dimension, you have to keep getting stronger, keep evolving to survive one horror movie after another. Do you kill everyone in your way to reach the end as a lone king? Or fight along with your comrades and survive through the support of friends? Everything was just for staying alive. Until you find the secret of God's dimension. Who is the real enemy?I am a huge fan of terror infinity, and I thought I'd write one myself, to contribute to you as terror infinity fans, and to me as a fan of the series. It takes elements incorperated from each of the Terror Infinity fan fics as well as some original factors by me.
8 183 - In Serial17 Chapters
risky ; the goonies
"that's way too risky," "oh, stop being a baby,"[mikey walsh x oc]
8 104 - In Serial33 Chapters
Marigold; Adventures of Scarlet Lady and Chat
You all know the story. The one about miraculous superheroes, a man who wants his family back, a girl who just wants her crush to notice her, and a boy who so desperately seeks love.Miraculous; Tales of Ladybug and Chat Noir. We've all seen the TV show...but what if it DIDN'T happen like that?What if a mistake was made?Marinette was supposed to have the ladybug miraculous. But before she could ever know the secrets it held, the miraculous box was stolen from her. But even as someone new held Tikki and the Ladybug Miraculous, Marinette stands up for what's right.In a strand of the Universe where everything has gone upside down. Where Adrien's in love with Marinette, while Marinette blushes at the thought of a masked Chat, and Chloe holds the power of good luck, anything can happen...but are you willing to find out what?
8 174

