《ƘADDARAR RAYUWA》Ƙ page 79
Advertisement
*ƘADDARAR RAYUWA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa
#Follow me on
"
Marubuciyar
*BIBIYATA AKEYI*
* Y'AR FARI*
* YARIMA FAYAD* paid 200
Page 79
Suna cikin meeting alhaji ya kirashi awaya bai samu ya ɗaukaba sai bayan yafito ya kirashi Alhaji yace masa yazo yana nemansa,
A ƙanƙanun lokaci ya isa wajan mahaifunsa bayan sun gaisa yake sanar dashi cewa yanaso suje saudi shida matarsa amarya sannan kuma suwuce wasu ƙasashe guda biyu itama ta buɗe idonta kuma duk tafiyarku ni zan ɗauki nauyinsu gabaki ɗaya,
Naga aurenku wata huɗu amma haryanzy bakada niyyar yin hakan, kuma mahaifinta basuda ƙarfi izuwa yanzu yaci ace kafara taimaka musu wannan nabar makane kai dakanka kayi kasamu ladan sirikanka da kanka,
Kansa yana ƙasa yace "in sha Allahu alhaji zanyi,
Alhaji yace "saiku fara shirin tafiya nanda wani lokaci,
Godiya yayi masa sannna yawuce wajan Hajiya ya faɗa mata abunda Alhaji yayi,
Hajiya tace "eh munga kai bakada niyyar kyautatawa shiyasa, wancan matarda ka aureta wace ƙasace bakujeba amma yanzu wannan aure wata huɗu kazauna kayi shiru, ko tsoronta kakeji shiyasa ita wannan kakasa kyautata mata?
Ƙasa yayi da kansa bai iya cewa komai ba, Har Hajiya tayi faɗanta tayi shiru, Sannan daga ƙarshe tace yakawo mata sawwama ta kwana biyu bata gantaba, ya sama da cewa zai kawota amma sai gobe,
Hajiya tace toh Allah yakaimu,
Taraddadin yanda zai gayawa Dr wannan maganar yakeyi dan baisan yanda zata ɗauki abunba,
Saida yabari ya daidaici lokacin da suke cikin farin ciki sanna ya dubeta cikin wani yanayin da bazata iya karantar mood ɗinsa ba yace "Alhaji ya nemi ganina 2days back so naje yake sanardani cewa yabiya mana saudi nida Hafsa and kuma bayan nan zamuyi tafiya zuwa wata ƙasar daban kuma komai shine yaɗauki nauyin hakan bansan yaya zaki ɗauki lamarinba shiyasa ban sanar dake ba amma yaya kike ganin zamuyi, tunda yafara magana tasake baki tana kallonsa, bazaku jeba tafaɗa ataiace sannan ta ɗaura da faɗin ai bawai an aurota bane dan taji wani daɗi tasake dakaiba meye nawani har zuwa wata ƙasa kabari idan ka saketa saika biya mata saudi tubda tarigada tadawo uwar ɗanka,
Shafo kanta yayi yace "Alhaji su duk basusan da hakanba sun ɗauki wannan aurene kamar kowani aure kuma bazan iya mayarda ƙyautarsa garenu ba saboda bansan wane dalili zance masaba kinsan Alhaji kinsan yanayin tsaurins bazan iya bijirewa maganarsa ba,
Advertisement
Kuma dana zauna nayi tunani sai naga mai zai hana mutafi da ita ɗin kema mutafi tare amma kibiyomu daga baya, bansan ko acan idan babu idonki zan iya kusantarta ba,
Fauce hannunta tayi tace nace maka A'a bazkaa tafi da itaba idan bazaka kusanceta ananba kabari kuma kasan a irin wannan lokaci da nakeda patient dayawa bazaiyiwu natafi nabarsu ba kawia ka janye zancen tafiya da ita,
Amma dai kinsan bazan iyaja da maganar Alhaji bakoh? A fusace tace ni ka saketa kawai, ka saketa tunda dama ni nace ka aureta yanzu nafasa,
Miƙewa yayi yace wai yaronki kika maidani? Duk wani abunda kikace kinaso shi nakeyi saboda na faranta miki amma ke kullum sai kiringa yin abunki da isa kinsan banason haka kuma akanki bazan ɓatawa mahaifana ba, yana gama faɗi yafice a gidan bai dawoba sai dare a ɗaki ya sameta ta zauna tayi zugum zama yayi a gafenta cikin sanyin jiki jawota yayi jikinsa yafara bubbuga bayanta yaɗauki tsawon lokaci ahaka sannan yaɗagota hawaye yagani a fuskarta cikin rawar jiki ya sanya hannu ya share mata hawayen, Haba haba Sajida wai har meyayi zafi haka baki yarda dani bane?
Soyayyar da nake miki yasa nake biye miki a komai da kikeso wanda yawancinsu daga ƙarshe muke zuwa muyi danasani, farkon aurenmu babu yanda banyi dakeba akan ko yaro ɗaya mu haifa amma kikaƙi kikace karatu haka soyayyarki ta sanya na amince dukda raina bayaso,
bayan kingama karatu haka kikace aiki yayi miki yawa nanma na biye miki, har mahaifana lokuta da dana nakan bijirewa maganarsu saboda ke meyasa duk wannan abun bazaki iya fahintar sonda nake miki bazai bari naci amanarki ba?
Yanzu ni banaso wani abun yasake haɗani da mahaifana ta dalilinki inaso a yanzu komai dake tsakaninku ya dai-dai ta kinsani sanin kanki cewa ke kika fara saɓaw ada ƴan uwana su basu nuna miki wani haliba basu taɓa nuna miki wani ƙi ta dalilin baki haihuba abunda kike mus yasa suka canja miki kuma hakanma ban goyi bayan dangina ba ke nabi baya, kinsani kinsan dangina mutanen kirkine bzasu taɓa ƙinki da baki haihu ba, kuma laifin rashin haihuwarmu duka laifimmu ne mun biyewa son zuciyarmu,
Toh yanzu ma idan bakiyi hankali ba koda wannan tatafi wata zasu sake sawa na auro kinga nikuma bazan zama sai auri-sake ba,
Advertisement
zan zauna da wanda zasu auramin nan gaba har indai baki tsaya kin kwantar da hankalinki Anyi komai kamar yanda aka tsara ba, maganar tafiya kuma zamu tafi da ita idan hankalinki bai kwantaba ki biyomu amma bazan saɓa umarnin Alhaji ba,
Lumus tayi ajikinsa tana sauraron abunda yake faɗa komai tasan ta aikatashi shiyasa tayi shiru dan itama duk zafin zuciyarta bata iya juran ɓacin ransa nan danan take shiga damuwa ko tafara kuka dake tasan baya iya jure ganin hawayenta."
Jin yayi shiru da maganar yasa Alhaju yasake tun tuɓarsa yace Alhaji inaso zanyi clearing schedule ɗina na month ɗin gaba gabaki ɗaya sai mutafi zuwa wancan month ɗin,
Alhaji yace toh hakanma yayi Allah yakaimu."
Sawwama na gaban mirror ta fito daga wanka ɗaure da towel ta zubo gashin kanta abaya tajiyo shigowarsa amma bata juyoba tacigaba da abunda takeyi tabaya yazo ya rumguneta janye gashin kanta yayi gefe yayi mata kiss abaya murmushi tayi tace sannu da zuwa, ƙara rungumota yayi ya saka kansa a wuyanta yana kallonta ta cikin madubi yace albishir,.
Goro tafaɗi tana sakar masa murmushi Hajiya tace nakaiki tun jiya amma bansamu dana nazo nakaiki ba idan kuma taga driver ne yakaiki zatayi faɗa yau zamuje saiki yiwa Alhaji godiya ya biya mana zamu tafi saudi, juyowa tayi tana kallonsa dan son gasgakatar da abunda yake faɗa,
Ganin babu wasa a fuskarsa ya sanya ta raba jikinsa da nata ta isa izuwa gado ta zauna bin bayanta yayi da mamakinsa sai yaga batayi murna da hakanba
Bai yanke mata hukunci ba dan baisan dalilinta ba ya isa bakin gadon shima ya zauna,
Kamo hannunta yayi cikin kulawa yace"mai kuma yafaru? Maimakon kiyi murna sai naga akasin haka, sunkuyarda kanta tayi hawaye yanason zubowa tana ƙoƙarin maidashi tace "duk waɗannan abubuwan bamasu ɗaurewa bane kabari kawai nagama abunda ya kawoni natafi banajin daɗin wannan muguwar shaƙuwa dake shiga tsakaninmu,
Kamo hannunta yayi ya sakar mata murmushi sannan yace nikuma inaso, karkiyi judging komai yanzu bakisan yanda Allah zaiyu damu nan gababa, kedai yanzu ki shirya muje kiyiwa Alhaju godiya,
Gabaki ɗaya takasa gane yanda maganarsa ta dosa amma saboda batason sakawa kanda damuwa kawai saita share tayi masa godiya,
Yakaita tayiwa Alhaji godiya kuma yaji daɗi sosai."
Acikin month ɗin suka fara shirye-shiryen tafiya
tun awaya ta sanarwa mama kafin taje ta sanar msu Mama akan cewa zasuje Saudi kuma daganna zasu wuce wata ƙasar,
Mahaifanta sunyi murna sosai dan sunce zuwa saudi komadai menene a auren ai alkhairi ne,
Saudi suka fara zuwa dayake yazo ɗaya da lokacin aikin hajji,
sukayi aikin hajji wtaansu ɗaya acan suka wuce wata ƙasar,
Tarairaya da kulawa sosai Sawwama take gani a wajansa, zuciyarta takan yabi irin kulawa da tarairaya dayake mata, wata zuciyar sauta haneta tace karta fara ta faɗa domin gaba zatasha wahala kuma duk abubuwan dayake bawai dan yana sonta yakeyi mata na sai dan neman cikar burinsu shida matarsa, Amma ahaka idan kukaga irin kulawarda yake nuna mata saiku rantse auren soyayya sukayi,
Shikansa yanajin daɗin zamansu da Sawwama sosai domin ta kuwa ta iya zamada mutane iya zamansu bazai iya faɗin wani halinta da takeyi wanda bayaso ba, komai nata a nutse tajeyinsa Sam batada hayaniya gashi tanayi masa biyayya akan duk wani abunda yakeso,
Satinsu biyu acan Sawwama tatashi da zazaaɓi ya matsa sutafi asibiti tace dasauƙi basai sunje ba, ƙwana biyu da samun lafiyarta still wani ciwon yasake dawowa wannan lokacin kam dolenta saida tayarda sukaje asibiti, likita sun shaida masa tana ɗauke da ƙaramin cikin na wata ɗaya, Alhamdulillahi kawai yake faɗi yana godiya ma ubangiji,
Ita kam Sawwama tarasa wani irin hali take ciki shin murna zatayi? Kokuma baƙin cikin takusa rabuwa da mijinta?
Shi kansa saida ya fahimci halinda take ciki sai tabashi tausayi yasan koda ace bata sonsa sai taji wani iri idan tayi tunanin cewa da zarar da haihu zata rabu dashi saboda shi kansa yanzu bazai iya cewa baya sonta ba bare ita mai sanyayyar zuciya,
Kwantar matada hankali yayitayi harya samu ta ɗan sake tadawo kamar yanda suke."
Tunda Aka tabbatarda cikinne kuma sai jinya laulayi kala-kala, shidai yanan yana kulawa da ita kamar ƙwai saida cikinta yakai 4month kafinnan ya sanarwa su hajiya lokacin harya ɗan fara fitowa laulayin kuma yayi sauƙi sosai."
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
💞
Advertisement
- In Serial118 Chapters
Song of the Void
A great race faces extinction and tries to leave a legacy for the future. Young races building on the ruins of the old. What happens when one of the old ones wakes up and finds the universe changed? Will she try to find new meaning? Will she try to help the younger races or will she punish the grave-robbers for their sacrilege? Or will the eternal servant of her people try and finally find some happiness of her own?
8 388 - In Serial6 Chapters
Eyes of heaven and hell
Imagine a world where your eyes decide your place in the world. Ken Itami, a boy living in the powerless island carrying the power of heaven and hell in his eyes has to seek out those who destroyed his family. Read Ken Itami's story where he finds allies and makes enemies. How will Ken take up an entire government?
8 103 - In Serial6 Chapters
The unyielding lost girl
A girl suddenly wakes up in the middle of nowhere, with no recollection of her past, of her own identity, and no purpose. Her body seems to have been unconscious for quite a while.Moving is more troublesome than expected. Everything that she possesses is her wit, her sensations, and her intuition. Follow the adventures of ???, discover her name, and unravel the truths and rules of the world around her.
8 126 - In Serial29 Chapters
Universal Tampering Considered Harmful
Not so far in the future, in our very own galaxy... nothing much has changed. No robot apocalypse, no flying cars. Orion and his group of hackers and thieves live a simple life: do jobs that are fun, don't get caught. It would be quite easy if there wasn't that one friend that disappeared five years ago. The friend that worked on some top secret research on brain activity for the government. The friend that they've been looking for, without avail. As Orion and his friends finally pick up on a trail, they quickly find themselves involved in something much larger than one missing person. WARNING: This work contains explicit violence, mentions of abuse, and other potentially disturbing content. Reader discretion is advised.
8 219 - In Serial12 Chapters
Jealousy | Pico x Boyfriend |
Boyfriend decides to sign up for a rap competition. He bumps into his ex seeing that jealousy would form between one of them. you're free to make animations, edits or literally anything you desire with this fan fiction!
8 149 - In Serial18 Chapters
Blood Oath (Book 2 of Alfireán age)
In a world of dragons, magic and technology, a world that has been drastically changed from what we know, the weakest man alive must rise to overcome the greatest evil and discover a thousand years of mystery and secrets.Alfonso Vivyander Brockovich the third, one of the seven High Lords of Alfirea, has officially been declared dead and his life for ever changed. Now he and his friends travel to Glandledale to find the one they believe can help slow down Vackzilian's onslaught. However they are not the only one searching for her.
8 198

