《ƘADDARAR RAYUWA》K page 87
Advertisement
*ƘADDARAR RAYUWA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa
#Follow me on
"
Marubuciyar
*BIBIYATA AKEYI*
* Y'AR FARI*
* YARIMA FAYAD* paid 200
Page 87
Rayuwa mai cikeda kunshi da kadaici ta sake dawowa Sawwama kamardai lokacinda tarabu da Sadam zamu iya cewa garama wancan lokacin danshi rabuwace kuma tana sanya ran cewa ko badade ko bajima wata rana zata sake ganinsa Amma Abubakar fa? Yatafi fa yatafi gabaki daya shikenan bazata sake ganinsa ba, yatafi yabarta da farin cikin daya sayar da ita alokacin da suke tare dakuma bakin cikin rabuwa dashi, akoda yaushe taga fuskar muhammad fuskar mahaifinsa take gani domin kamarsu daya sak babu wani ahunda yabaro na mahaifinsa,
Hajiya ganin damuwar Sawwama gabaki daya taki karewa ya sanya ta yanke shawarar tayi takaba agaban Mama ko zata dan samu sauki,
Dady da mummy sunzo mata ta'aziyya amma dady sam baiyi tunanin karban yaranba tunda marikinsu ya rigada ya rasu ko maganarsu baiyiba har suka mata ta'aziyya suka tafi,
Itadai mummy batace komaiba amma a zatonta zasu taho da yaranne sai taga dady baiyi zancensuba."
Sadam yafito daga wani eatery dake kusada wajan aikinsa dan samun abunda zai sanyawa cikinsa ko breaskfast baiyiba saboda sassafe yake barin gidan,
Kansa na sama yafito dauke da breaskfast a hannunsa yana sauri ga dukkan alamu yanaso yakoma wajan aiki,
Batareda ya lurada yaji ya bigi mutum da sauri yaja baya yakai kallonsa ga wanda ya bige, a fili da furta hafsa! Da mamakin ganinta dayayi awajan dan baiyi zatoba,
Tsayawa tayi ta kalleshi sannan ta tabe baki tace "Sadam kaine?
kace bazamu sake haduwa ba sai gashi yau Allah ya hadamu, murmushi sadam yayi yace "ikon Allah kenan,
Sake tabe baki tayi sannan tace "ina tunani abaya ka manta da cewa Allah zai iya ikonsa musake haduwa koh?
Sadam ya sunkuyarda kai yana murmushi itakuma ta wulla masa harara,
Cikin sauri yace "Yanzu dai bani phone number dinki zannemeki zuwa jimawa idanna tashi wajan aiki yanzu haka idanna tsaya zan iya latti,
Harde hannuwanta tayi tace "banbayarwa kaje abunka,
Sadam yace "toh shikenan sai anjima,
Hade rai tayi,
tayi saurin shan gabansa oh dannace katafi sai katafin? Har yanzu baka canjaba kunyatardani baya baka wahala idan mace tace maka zatafi kawai saika sanya kai katafi? Dan rarrashi haka bazaka iyaba?
Murmushi sadam yayi yace "yanzu bani adreshinki zanzo mu gaisa,
Babu musu tabashi adreshin sannan tace "kazomin da twins idan zakazo,
Advertisement
Yake yayi wanda yafi kuka ciwo kawai yawuce batarea yasake cewa komaiba,
Kwana uku kenan hafsa tana sanya ran ganin Sadam amma baizona,
Shikuwa Sadam harma ya manta da sun haduda hafsa."
Yau yakasance weekend babu aiki sannan yagaji da fita yawuni bazai iya zama agida yaji dramar abida ba,
Yanata tunano wanda yasani sai yaje can, Hafsa ce tafado masa rai, kai ina yace bazan iya zuwa wajanta karma tayi tunanin wani abun ya kaini ta sanyawa ranta auranta zanyi bakuma zan iyaba,
Haka ya share baije wajan nataba Sati biyu Allah yasake hadasu a same eatery da suka hadu,
Hafsa tayi bambammi kan cewa yace zaizo baizoba koya tunanin har yanzu zatace saiyayi soyayya da itane?
Sadam yace " no hafsa bahaka nake nufiba kawao aikine yayimin yawa bansamu danar zuwaba,
Hmm kokuma kace matar so ta hanaka ba? Ina tunanin bazaka iya zuwa wajena kabarta a weekend ba,
Murmushi mai ciwo Sadam yayi yace "Hafsa kibari zanzo zamuyi magana,
Nasan bazuwa zakayiba ka fadamin address dinka ni zanzo, girgiza kai yayi yace "dagaske nake miki wannan Karon zanzo,
Hafsa bata tafiba saida takarbi lambar wayan Sadam, kiransa takeyi akai-akai amma bata wani samun kansa,
A weekend ya shirya yatafi zuwa address dibda tabashi wani dan matsakaicin gidane mai kyawun gaske,
Sadam yasamu tarba sosai har mamanta da babanta saida suka shigo suka gaisa,
Bayan sun fita ya kasance saura ita dashi a palourn,
Hafsa tace "nace maka idan zakazo kazomin da twins har yanzumma rowarsu zakayimun?
Sadam yace "twins basa tare dani shiyasa banzo miki dasuba,
Kace idan kazo zamuyi magana inajinka yanzu zaka aureni matsayin matarka ko har yanzu bakada ra'ayin aurena?
Nasan kanason matanka kuma nima zan kiyaye bazan yi wani abunda zaai sanya musamu matsala dakai ta dalilinsuba,
Sadam yace "kiyi hakuri amma aure tsakaninmu bazai yiwuba ko yanzu haka nazone kawai dan karkiga kaman ina miki wulakanci,
Nunfashi hafsa ta furzar tace "har yanzu baka canjaba kananan dason matarka,
Ko kasan dalilinka ya sanya nadawo nan kasar da zama?
Awancan lokacin nashiga wani hali daka nuna bazaka aureniba dama kuma mahaifina anan yakeda zama ina wajan kaninsa acan, yasamu ambassdor nanan kasar amma koda yadawo ban biyoshiba saboda nafison can, nafi sabawa acan natashi, amma dana rasaka saina yanke shawraar barin kasar ko zan samu sauki sai gashi Allah ya hadani dakai anan shin baka tunanin akwai abunda Allah ya tsara akanmu?
Sadam yace "bawannan dalilin ya sanya bazan aurekiba Sawwama yanzu bama tareda ita, aurenmu yarabu badan wani laifi dana mata ko ita tayimun ba,
Advertisement
Atakaice yabata labarin abunda yafaru yace "kinji dalilin daya sanya bazan iya auranki ba saboda abune mawuyaci nasake haihuwa idanna aureki na cutar dake ko Sawwama abunda yasa bazan taba iya maidataba kenan,
Kuka sosai Hafsa takeyi na tausayinsa dakyar ta iya budan baki tace "bantaba tunanin abunda yafaru dakaiba kenan saboda nahana su najeeb fadamin duk wani abunda ya shafeka,
Nace musu komai naka bana bukatarsa dan abunda kayimin wajan bikinsa,
Banyi tunanin abunda yafaru dakaiba kenan,
Yanzu kun rabuda maman twins?
Kai kawai ya jijjiga mata tacigaba da fadin amma baka tunanin idan kayi mata haka bakayi mata adalciba?
baka tunanin cewa ka sake mata wani rashin adalcin akan wanda aka mataba?
Bakasan ko cewa zata iya zama dakai ahakaba da baka yanke mata wannan hukuncinba, zaka ka jefata cikin wani hali,
Sadam yayi murmushi yace "nasan wacece Sawwama bazata taba guduna ba komenene yasameni, kowani hali nake ciki zata zauna dani ta rumgumeni hannu bibbiyu,
Amma nikuma bazan iya zamada ita ayanda nakeba ba lallai idan mummy zata zauna da ita lafiya ba na rigada na sanyata a bacin ciki abaya ayanzu bana fata tasake shiga wani bacin cikin koba ta dalilinaba,
Zan barta tayi rayuwarta amma soyayyarta bazata tana gushewa acikin zuciyata ba, soyayyar da zanyi mata kenan na barta tasamu farin ciki,
Kuma yanzu haka tayi auranta harta haihu a yanda nakejin labari ta samu farin ciki kamar yanda nake mata fata, tasamu kulawa da komai wanda ni banbata kamarsa ba,
Hafsa tace "bana tunanin ita awajanta zatace haka dan ga dukkan alamu itama tana sonka sosai, farin cikin daka bata kuma bazai taba barin zuciyarta ba,
Babu abunda mace zata nema wanda baka bataba ayanda mutane suke fadin sonda kake mata abu daya takasa samu shine soyayyar mahaifiyarka abunda ya tarwatsa muku farin cikinku kenan,
Murmushi Sadam yayi yace "kinga kuwa nakasa kenan ba? Tunda ban iya samar mata da soyayyar yan uwanaba shikuma wancan ya samar matada hakan,
Wannan ba laifinka bane Sadam babu yanda ka iya da wannan, yafi karfinka,
Ita yanzu abida tana ina?
Tana gida yanzu haka nabarta,
zafafe tace "itama karabu da ita karka zauna da ita babu wani amfanin da zatayi maka arayuwa ninan na isheka duk wani farin cikin daka rasa ni zan dawo maka dashi,
Wata dariya Sadam yayi yace "Hafsa wai bakya jine?
Nace miki bazan aurekiba kinemi wani can ki haifa wanda zaku tara iyalai dashi,
Cikin fada tace "wallhy baka isaba saika aureni waya cemaka tara yara shine kawai farin cikin rayuwa?
Kaganni kadauki darasi akaina Ummina daka gani wannan ba itace ta haifeniba,
Mahaifiyata wajan haihuwata tarasu abbana ya aureta ta raineni haryau Allah bai bata haihuwa ba kuma tana ryuwarta cikin farin ciki, ko kawayena bantaba fadawa kowa cewa ba itace ta haifeniba saboda soyayyar danake mata,
Shi kansa mahafina daga kaina bai sake samun haihuwaba kuma yayi hakuri ya zauna cikin farin ciki, mahaifina da mahaifiyata farin cikin da suke ciki wasu masu yaranma basa ciki, bare kai Allah yanaka har guda biyu muyi aurenmu mu rumgumi yaranmu zamu kasance cikin farin ciki."
Mikewa Sadam yayi yace "banaso nayita jan magana dake Hafsa mubar wannan maganar ni yanzu barina tafi saimun sake haduwa, baijira abunda zatace ba yafice,
Hafsa bata tsaidashi ba yatafi abunsa, yana fita umminta ta shigo da niyyar jin yanda sukayi,
Ganin yanayinta ya sanya ta tabbatar abun baitafi dai-daiba,
Zama tayi tace "hafsa yaya kukayi dashi?
Hafsa tace "yace bazai aureniba,
Umminta tace "Hafsa izuwa yanzu ki hakura da wannan yaron tunda yanuna baya sonki ko kina tunanin ni zanji dadi na turaki yanda ba'a sonki?
Ummi shifa bawai sonane bayayiba ayanzu bazai aureni bane dan wani dalilinsa na daban,
Mahaifiyarta tace "komadai menene dalilinsa baida hujjarda zai ringa wahalardake akan kinasonsa kawai.
Nifa bashi yake wahalardaniba kuma dalilinsa mai karfine amma ni wannan dalilin bai isa yasaka nabarshiba,
Menene dalilinsa toh?
Hafsa ta fadawa mahaifiyarta,
Cikin tausayawa tace amma ke har zuciyarki kika amince zaki aureshi ki zauna dashi ahaka?
Jijjiga kai tayi dasauri umminta tayi tace "shikenan zanyi magana da abbanki yanda mukayi dashi zakiji har indai kinada tabbacin zaki samu farin cikin da kikeso awajansa wannan ba komai bane,
Murna sosai hafsa tayi bayan mahaifinta yadawo umminta ta sanar dashi ya sanya ta kira masa hafsan bayan sun zauna yace "hafsa naji abunda umminki tafadamin ahaka kina sonsa? Dasauri ta gyada kai mahaifinta yace shikenan kije Allah yayi miki albarka ki kirawonshi zamuyi magana, hafsa tayi murna sosai takira sadam tace masa yazo inji abbanta bataeda yayi tunanin cewa mahaifin zaiyi masa maganar auren yarinyar bane dan atunaninsa babu mahaifinda zaiso yarsa wacce bata taba aurena ta aureshi."
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
💞
Advertisement
- In Serial114 Chapters
Rebirth in a Magical World
What would you do if you were reborn inside the Harry Potter Universe. Follow Alexander Fawley's adventures as he is reborn in the Harry Potter world. In this tale, he will have new unique adventure to call his own, And he will discover that the Harry Potter Universe is much greater than he had imagined. P.S This is my first story, so please leave reviews, to let me know how I am doing, so I can get better. Also J.K. Rowling owns Harry Potter, I simply play in her world. On a side note, I am curently re-editing the first half of the story. So, you might see grammer mistakes. I am working on fixing the problems, if you can push through to the chapter thirty-five ish the grammer improves alot becuase White Wind has been editing my mistakes.
8 374 - In Serial12 Chapters
Fire and Blood
There are a lot of stories about people reborn into a fantasy world but most such individuals seem to be young, inexperienced and forced to start from the bottom up. But who attempts to summon a nobody, expending vast magical power to do so? What if there is an effort to summon a champion of the celestial host and strip them of their free will, binding them by their True Names only to be foiled as they vacate themselves to follow possession by another? What if the one summoned from something approximating our own world is a veteran in her thirties who now finds herself in a form alien, powerful, but far from invulnerable? It involves a whole lot of fire.
8 141 - In Serial12 Chapters
Spread of Chaos
Leon has a problem. He's been kidnapped from his world to be the champion of a god no one likes. When his deal with the god Chaos falls through he's stripped of the best part of being a champion. Now without the active support of his god, he has to turn his last remaining trump card into the mother of all cheats, spread the name of Chaos, and look good doing it, if he's to make it back home.
8 255 - In Serial8 Chapters
Wanderlust
After having been given a prophecy at the Imperial Palace in New Tokyo, Sumire decides she's going to do some soul searching on an adventure to fulfill it. Nobody knows where it'll lead to, least of all the people involved. Wanderlust is a fantasy, action / adventure through California after a nearly apocalyptical event shatters the United States into the Divided Territories of America. The new wild west has started filled with guns, mist, swords, armor, and of course magic spellslingers. It has multiple points of view, mainly following two women in a story of connection, revenge, and focuses heavily on character development. I hope you enjoy. - - - A note on tags: as of writing there is currently no sexual content, but that will change later as the story progresses.
8 90 - In Serial23 Chapters
Creatures of Avetoro
Grace Bennet is an ornithologist from Maryland who, with 3 other researchers, were given the chance to go to the island of Avetoro for researching the unique Caribbean birds, but only she and another left. Now, two years later, she is drafted onto a team to investigate the disappearances. However, the team was slaughtered and left only Grace and Adam Butch, a mercenary, alive on an island of dinosaurs. Possibly the last ones alive, they need to get off or die as well.
8 179 - In Serial10 Chapters
Goblin Combe
This story follows Jack Chaque-Travail, an Illusionist determined to usher in the next generation of Druids to make sure he doesn't have to watch the earth die around him. Druids used to be awakened high on mountain tops, or in deep caves, but now there are so few left they must be shipped into a summer camp to at least eke out what little potential they have. 'Come with WildWise™ and get away from the buzz of the city and towards the buzz of the sacred bee!' as quoted from their website. As years have gone by, and ozone has deteriorated, Druid training is less summoning treants and more kumbaya-ing. If there is no connection to nature, there are no more Druids, and that means horrible things for everyone left behind. Join Jack as he grifts his way through being a childrens educator, cheating and tricking them into being valuable members of society.
8 93

