《ƘADDARAR RAYUWA》K page 92
Advertisement
*ƘADDARAR RAYUWA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa
#Follow me on
"
Marubuciyar
*BIBIYATA AKEYI*
* Y'AR FARI*
* YARIMA FAYAD* paid 200
Page 92
Kwanansu hudu agarin amma gabaki daya garin ya isheta damuwarta kawai taganta agida Hajiya kanta ta fahimci hakan shiyasa ta yanke shawarar kwana biyar kawai zasuyi su koma hakan yana nufin saura kwana daya kenan,
Hajiya Sam batason ganinta cikin yananyin damuwa har irin haka,
Ta lura idan suna zaune ita shiru kawai takeyi tana tunani idan aka sakota cikin zance sai tayi murmushin yake kawai,
Yareema kuma gabaki daya ya hanata sakatt kuma baya taba yiwa kowa magana sai ita baya sakewa da kowa sai ita idan tabar wajan ya ringa musu tijara kenan bata samun lokacin kanta sai dai idan yayi bacci,
Har su umma hakuri kawai suke bata domin sun san ta takura dayawa amma babu yanda zasuyi,
Aranar Hajiya ta snaar musu cewa washe gari zasu koma nan kuma sai hankalinsu ya karkato kan lamarin toh idan suka tafi wani hali yareema zai kasance aciki?
Karfa akoka gidan jiya, su kansu shaidane baya taba yarda ya zauna waje idan bata a wajan kuma har lokacin bai saki jiki da kowa ba sai ita, yaya zasuyi kenen menen mafita?
Izuwa yanzu basu hango mafitar ba amma da ace zau kara koda wasu yan kwanakine tabbas za'a samu mafita,
Hajiya zaune gaban mai martaba kanta yana kasa bayan sun gama gaisawa sannan tace "Abba dama nazo na sanarda kai ne cewa gobe idan Allah yakaimu zamu koma gida,
Mai martaba saida yaji gabansa yafadi a tunaninsa zau dan kwana biyu,
Shiru yayi sai can yace "Bazaku dan kara wasu kwanaki ba? Tunda kinga yanda lamarin ya kasance kada kutafi kuma abu yazo ya baci azo akoka gidan jiya azuwa yanzu bamuda wata mafita amma nasan idan kuka kara kwanaki tabbaas zan nemo mafita,
Ajiyar zuciya Hajiya ta sauke sannan tace "Abba nima naaso nakara kwanakin tunda dama bada niyyar kwanakin danazoba kenan naso nafi haka amma Abba hafsatu tana takure matuka tana cikin damuwa ganinta a wannan yanayin baiyimin dadiba Abba kar garin son zuciyarmu ita kuma mu tauyeta tunda mijinta ya rasu na yi alkawarin bata farin ciki dai-dai gwargwado yana daya daga cikin dalilin dayasa nazo da ita nan,
Kar yazamnaa ni banbata farin cikiba kuma na sakata a damuwa batajin dadin zaman nan idan muka koma can duk wani abunda ake ciki sai a yanke, tayi magana yanda mai martaba ya fahinceta sosai,
Advertisement
Dan haka baija wani zance ba,
Mai martaba ya nisa sannan yace "hakane maganarki kinyi tunani mai kyau shikenan yanzu kuje in sha Allah zamusan abunyi,
Hajiya tayi masa godiya sukayi sallama da fadin gobe zatazo yimasa Sallama,
Sawwama jin zasu tafi washe gari taji dadi sosai sai take ganin kamar gobenma bazata yiba,
Washe gari jirgin 12:am suka biyo suka dawo gida sai asannan sawwama taji sanyi aranta,
A gidan Hajiya suka wuni zubur sai yamma likis kafinnan tasaka driver yakaita da muhamnad da tsarabarda suka zo da ita,
Babu wanda tabawa labarin abubda yafaru agidan tacigaba da rayuwarta kamar yanda tasaba, amma sai dai wani abu guda daya shine tausayin Yareema takeji aranta ko menene ya sameshi ya kwanta ciwo haka tsawon lokaci?
Menene alakarta dashi wacce ita bata saniba? A iya tunaninta tayi amma batasan wani abunda yataba hadata dashiba.
Nisawa tayi sannan afili tace "Allah yabaka lafiya dan har cikin ranta tana tausayinsa."
Yareema yasake shiga wani hali a hankali-hankali ciwon yake dawowa yanaso yakoma kamar na baya mai martaba Umma da sauran hankalinsu ya tashi ganin abunda yake shirin sake faruwa,
Mai martaba ya rigada yagama yanke hukunci cikin zuciyarshi dai dai har izuwa yanzu bai fadawa kowa Bayan yazo ya duba jikin yareema yafito falo yasamu su Umma suna zazzaune suna kallonsa gabaki daya suka mike shikuma ya zauna akan kujera sannan suka zauna a kasa,
Yadubesu zuciya cikeda Damuwa yace "Ga dukkan alamu abunda banaso shine yake shirun sake faruwa jikin yareema yanaso yasake dawowa kamar nabaya,
Bamuda tabbacin abunda yake faruwa gameda wancan yarinyar (Sawwama) amma inada yakinin cewa akwai wani abun dake kulle tasakanin wannan ciwon dakuma ita yarinyar bamu saniba ko Allah ya rubuta cewa warakarsa na tareda ita shiyasa tsawon lokaci mukayita neman magani Allah baiyiba amma gashi a mintuna kadan da haduwarsu sai Allah ya nuna mana ikonsa, yanzu gashi tatafi abu yanaso yadawo,
Shiru yayi sannan yacigaba da magana "narigada na yanke hukunci cikin raina amma yazama dole na shawarceku matsayinku na mahaifansa zan tafi dakaina har can garin na nema masa auran wannan yarinya domin hakan shine kawai mafita,
Umma wacce itama ayanzu tasan batada wata mafita data wuce wannan dari bisa dari tabawa mai martaba goyon baya,
Amma sai dai ita yarinyar basusan ko cewa zata aminceba, amma zasu fara tunkarar Hajiya da maganar kafin akaita gaba,
Mai martaba yace "idan Allah yakaimu gobe zan tashi natafi can kuma inaso har naje nadawo babu wanda zai san abunda yakaini,
Advertisement
Da mamaki suke kallonsa da sukaji abunda yafada wai gobe zaije can, mai martaba da kansa zaije akan wannan maganar shida bama mutumbe mai son tafiya ba, barinma da akace yareema ya kwanta rashin lafiya sam baya nisa da gida saboda tsoron abunda zaije yazo,
Umma cikin ladabi kanta yana kasa tace amma Mai martaba daka tura wani basai kaje da kanka ba koda wasu daga cikin amintattunka katura za'aje kuma zasuyi abunda yakamata,
Mai martaba cikeda damuwa yace "wannan lamari yanada muhimmanci sosai a wajena bai kamata ace nayi wasa dashiba bayan ku nan dana sanar daku babu wanda zai san abunda zai kaini, kuma na gargadeku karkowa yasani,
Umma tace "in sha Allahu babu wanda zai sani, mai martaba yace "Allah yayarda akowani lokaci yana fada musu su boye samun lafiya da ciwon Yareema bawai dan yana tunanin zasu fada ba sai dan kawai yanaso yasake jaddadawa."
Da dare Hajiya na zaune wayarta tafara ruri tana dubawa taga mahaifinta da sauri takai hannunta taja ta amsa kiran cikin ladabi ta gaidashi ya amsa cikin hikima mai martaba ya zayyana mata abunda yake shirin faruwa da kuma wanda yafaru m bayan tafiyarsu,
Hajiya tayi shiru sai can tace "Abba ni aganina hukuncin daka yanke bayida laifi hakan yayi yareema danane ni kaina mai bashi aurene ya aura ko aysha akace a aura masa a yanzu banida jaa zan bashi zuciyata daya kuma hankalina kwance amma dubada condition dinsa a yanzu bana tunanin Hafsa zata amincewa auren kokuma zatayi farin ciki da auran Abba rokon danakeso nayi maka guda dayane in sha Allahu gobe zan kirata muyi magana kafin kazo amma har indai bata amince ba inaso kayimin wannan alfarmar kada a tilastatta ko abi ta wajan mahaifanta yanda zasu sanyata ta amince, inaso tayi farin ciki tayi aurenta zai sanyata farin ciki tasamu nutsuwa fiyeda yanda tasamu wajan Abubakar lokacin yana raye,
Shiru mai martaba yayi jim kadan sai kuma yace "toh shikenan Allah yakaimu goben nayi miki wannan alkawarin babu wanda zai tilastata, amma kifara magana da ita tukunna kafin na iso jirgin rana zamubi bayan azahar in sha Allahu zamu iso,
Hajiya tace Allah ya kawoku lafiya sannan sukayi Sallama."
Wa she gari ta sassafe Hajiya tafara aikan abubuwan da za'ayi na bukatar wanda za'a tarbi baki dasu,
Wanda zatayi ordernsu kuma tun adaren jiya tarigada tayi karfe tara takira Sawwama tace tanason ganinta batareda wani tunani ba Sawwama tadauki muhammad dake su Hamdan suna makaranta tataho,
Ganin ayyukan da akeyi ya sanya tmdaga zuwanta itama tashiga aikin cikin kankanin lokaci suka gama tangamrmen falon Alhaji na tarban baki aka sake gyarawa dukda koda yaushe acikin gyara yake aka jere abubuwan acan lemu kuma da na kanti da wanda suka hada da kawunansu aka sanyasu a cikin firiji,
Sai bayan angama aikin Sawwama tasamu zama Hajiya kam bata samu zamaba domin tasa anata gyaggyara ko'ina dan mai martaba wannan karonne zuwansa na biyu gidanta da rasuwar Abubakar sai wannan ko auran yaranta yazo daga zaran an gama daurin aure daga can yake wucewa,
Shi kansa alhaji ya kansile duk wasu schedules dinsa na ranar ya gayyaci wasu daga cikin abokanansa kawai suna jiran zuwan mai martaba."
Hajiya babba tana zaune rohoto ya isota cewa mai martaba zaiyi tafiya da garinda zaije amma sai dai basusan abunda zai kaishi ba Hajiya Babba tashiga taraddadi sosai domin mai martaba baya tafiye-tafiye shi sam idan yabar gari kuwa toh zaije Kasar saudia ce, sai kuma wani Babban lamari dan haka gabaki daya hankalinta baikawo mata cewa wai zaije nemawa Yareema aure bane amma duk da hakan ta sanya ayi mata binciken abunda zai kaishi garin."
Saida sukayi sallar azahar sannan Hajiya tasake wanke ya shirya cikin Lace tazauna a dakinta sannan ta nemi ganin Sawwama,
Sawwama tamikr tabar muhammad wajan Aysha dan tasan maganace mai muhimmanci tunda a uwar daki za'ayita,
A zaune tasamu hajiya akan Sofa dake cikin dakinnata saida gabanta yafadi dan wata iriyar kama da Hajiya tayi mata da Abubakar, gabaki daya shima kamanninta ya dauko,
Dakyar ta iya saita kanta dan hawaye ke son gangarowa a idonta ta maidasu sannan ta isa da Sallama Hajiya ta amsa tana sakar mata da murmushi zama tayi kasa nan kan carfet kanta yana kasa tace "Hajiya gani,
Hajiya tadade tana kallonta ahaka takasa furta komai jin shiru yasa Sawwama tadago taga ita Hajiyan ke kallo saita maida kanta ta sunkuyar Hafsatu! Hajiya ta kira sunanta a hankali ta amsa da fadin "Na'am,
Iska Hajiya ta furzar Sannan tace."
Nayi test jiya shiyasa jiya da shekaran jiya kuka jini shiru na tsaya na dan taba karatu, Allah ya taimakemu baki daya ya biya mana bukatunmu na Alkahiri nagode sosai da Hakurin da kukeyi da yanayin typing dina in sha Allahu komai yakusa zuwa karshe nahuta kuma ku huta. Sai dai comment dinku yayi kasa sosai😩😩 dan Allah kudaure kuna comment dayawa ko zan samu naji karfi nagama tashi daya."
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
💞
Advertisement
- End806 Chapters
Coiling Dragon
Empires rise and fall on the Yulan Continent. Saints, immortal beings of unimaginable power, battle using spells and swords, leaving swathes of destruction in their wake. Magical beasts rule the mountains, where the brave – or the foolish – go to test their strength. Even the mighty can fall, feasted on by those stronger. The strong live like royalty; the weak strive to survive another day. This is the world which Linley is born into. Raised in the small town of Wushan, Linley is a scion of the Baruch clan, the clan of the once-legendary Dragonblood Warriors. Their fame once shook the world, but the clan is now so decrepit that even the heirlooms of the clan have been sold off. Tasked with reclaiming the lost glory of his clan, Linley will go through countless trials and tribulations, making powerful friends but also deadly enemies. Come witness a new legend in the making.
8.18 820 - In Serial15 Chapters
The Fourth Faction
The protagonist died, and regained consciousness in an unknown location. He kept some memories, and quickly realise he was reincarnated in an alien life form... A life form which wasn't unfamiliar. A life form full of potential. The protagonist also realise that there will be a lot of trouble in the future with the other races... Another "reincarnation in another world" story, but it's not a fantasy world. WARNING: Mature content of all kind once in a while, and more in later chapters
8 118 - In Serial15 Chapters
Escape the Room Game #1 - The Bedroom
This is an interactive story game where you, the reader, must solve puzzles in order to escape a number of rooms and ultimately escape the confinement you are in. The game incorporates a life points system to make the game a bit harder. Each player starts out with 5 life points. Each time you meet a bad ending, you lose a life point. Reach 0 life points and you lose the game. Once you solve the puzzle(s) in the room, you must pm me your answer (DO NOT WRITE YOUR ANSWER IN THE COMMENTS!). Depending on the answer, I will give you a link to either a bad ending or a good ending. The game has started so please enjoy. If you have any questions, don't hesitate to ask in the comments.
8 138 - In Serial19 Chapters
Primal Cosmic Sage: A Marvel Fanfic
A flashy death led to his reincarnation into the multiverse of one of the most dangerous and exciting works of fiction. An unintended stopover at the bleed dimension associated with the DC multiverse ultimately led to the demise of his Guardian System. Outraged and swearing revenge at the perpetrators of this grievance, witness Acheran's journey from a cannon fodder existence in the Marvel World to become one of the most powerful Cosmic beings in the wider Omniverse as the Primal Cosmic Sage.
8 69 - In Serial14 Chapters
Falling for you
Alli Stubbins is Tommy Stubbins older sister who is pretty much a sassy, stubborn girl who only believes that you only have a one true love once in your life which she thought she had. While one day she, Tommy, her uncle and cousin who Alli finds annoying may I say as they're trying to turn Tommy into a hunter but she understand that he wants to help animals just like Alli did but stopped for a while. What happens when Tommy accidentally shoots a squirrel and they follow a parrot to a house that Dr. Dolittle lives in. What happens when they both fall for each other but don't realize it but Tommy and the animals do.
8 226 - In Serial20 Chapters
My Thoughts In The Form Of Poetry!
Well here are few poetries I have written. They are basically an interpretation of my thoughts.I hope you guys enjoy and try to relate!
8 219

