《ƘADDARAR RAYUWA》K page 97
Advertisement
*ƘADDARAR RAYUWA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa
#Follow me on
"
Marubuciyar
*BIBIYATA AKEYI*
* Y'AR FARI*
* YARIMA FAYAD* paid 200
Page 97
Tun acikin toilet din bayan ta taimaka masa ya tsarkake jikinsa ta fuskanci sauyin yanayi a tattare dashi,
Wani irin kallo yake mata wanda takasa gane na menene sai lumshe ido yakeyi kamar wanda yakejin bacci,
Numfashinsa yana fita da sauri da sauri ganin haka ya sanya ya janyoshi kawai suka fice daga bandakin,
Suna fitowa daga toilet din sai taga jikinsa gabaki daya ya mace kamar wanda ciwon yake shirin tashi gabaki daya ya canja yanayi ya isa gadon batareda yasake kallon yanda takeba ya kwanta a gefensa na dama, dasauri ta bude wadrope din taciro sabuwar jallabiya da sabon boxer kamar yanda tagani suke kowanne cikin ledarsa gabaki daya wadrope din abjnda yake cike kenan dam kuma dukansu sabi fill, taga dai wanda yana cirewa fita dasu akeyi, ahaka dai ta taimaka masa ya sanya amma a yanda ta sanshi a kwana biyunnan zata iya cewa yanzu kamar wanda aka sauyashi kamar wani daban bashiba,
Da sauri yakoma yasake kwanciya a gefensa na dama ta dauko ruwan addu'a tabashi ya sha ya sake komawa ya kwanta ha lumshe idanuwansa,
ganin haka ya sanya itama ta kwanta gefensa shikuwa yana kwanciya kamar wanda baccin yake jira ya daukeshi, ba ita tafarka ba sai asubahi a yanda ya kwanta ko kwakkwaran motsi baiyiba saida ta mirginashi ta canja masa wajan kwanciya sannan ta tashi tashiga toilet tafito daureda alwala taga yakoma kamar yanda ya kwanta a barin damarsa,
tabarshi a hakan ta gabatarda Sallah dake anrigada anshiga ta dade zaune akan Sallaya bayan addu'oi tayita karatun alqur'ani saida taji bacci na neman daukarta a zaune sannan tatashi ta dauko ruwan addu'an da mai martaba ya aiko ta tasheshi amma kamar baya jinta ko matsawa baiyiba nunfashinsa dai yana sauka a hankali ganin haka ya sanya kawai ya shafe masa jikinsa dashi sannan ta kwanta a gefen gadon,
yau kam bata kai kamar jiyaba dawuri tatashi tashiga tayi wanka sannan tafito ta canja kayanta tafita bataga kowa a falonsu Umma ba dan haka tawuce izuwa kitchen wanann matar ta jiya tagani wacce Umma tace mata itace wacce takeyin komai na kitchen din,
Da mamaki take kallon Sawwama domin batasan abunda yakawota kitchen dinba batama taba kallonta ba ko batasan bakowa ke shiga kitchen dinbane?
Sawwama ta kalli matar taga ita take kallo ta juyarda kanta gefe batareda ta kalletaba ta bude baki zata gaidata sai taji matar ita tafara gaisheta nauyin amsawa taji sai kawai ta maida mata da gaisuwar itama matar bata amsaba dan tasan cewa batada damar amsa wannan gaisuwa ko ba'a fada mataba tasan cewa itadin watace shigar jikinta zai nuna hakan,
Jin bata amsaba ya sanya Sawwama bata sake tankawaba tajuya tafara abunda ya kawota saboda taji Umma jiya tace ayimasa faten dankali da kifi sanna asaka alayyahu akai hakan ya tabbatar mata da yanaso ne,
Advertisement
Saida ta tanadi duk wani abunda takeda bukata sannan tafara aikin itadai matar kallonta kawai takeyi bataso ta hanata kuma taje tayi laifi tunda batasan ko wacece ba,
Sawwama bata matsa a wajanba saida tagama komai ya jure sannan tabar kitchen din,
Iya wanda zauyi amfani dashi ta deba da ajiye sauran akan dining dinsu Umma,
Har lokacin yana bacci hakan yasa ta debi nata taci sannan ta rufe masa nasa ta zauna takira mama Sun dade suna hira samnan ta kira haleema saida suka dauki tsawon awa suna waya bayan sun gama takira hajiya suka gaisa,
Baba kam tasan yana kasuwa hakan yasa batama kirashi ba,
Har wajan shabiyu bai tashiba tana zaune tana danna waya taji Sallamar Umma amsa Sallanar tayi sannan tace tashigo ta karaso ciki ta gaidata ta amsa tana tambayarta mai jiki tace "Alhamdulillhi
Umma ta zauna tana kallonsa da mamakin irin kwanciyar dayayi,
kwana biyu har wani dan cika yayi,
Saida tanemi waje ta zauna sannna ta maida hankalinta kan Sawwama wacce tayi kasada kanta tace "ya tashi kuwa? Ko har yanzu bai farkaba?
Sawwama tace "tun jiya dai daya kwanta da dare bai tashiba na tasheshi yasha wannan ruwan da aka aiko amma har yanzu bai tashiba,
Umma ta jijjiga kai tace toh kwanciyar fa tun jiya haka ya kwanta?
Sawwama ta dago ta dubeta dan bata gane yanayin tambayarba,
Umma data fahimci haka sai tace "ina nufin a hannun damansa ya kwanta?
Eh a hannun ta kwanta koda na mirginashi sake dawowa yayi,
Umma da nisa zuciya cikeda damuwa danma yanzu damuwartata ta ragu cikin karyayyiyar murya tace "kuma naga jiya baiyi baccinba Allah dai yasa bawani sabon abun bane kuma,
Sawwama ta amsa da amin,
Suna zaune ahaka Ummi tashigo ta samesu sa'i-sa'i suke taba hira amma ita bata sanya musu baki saboda akwai rashin sabo,
Saida akayi azahar sannan su Umma suka fita don gabatarda Sallah itakuma aciki tashige toilet tayi alwala ta gabatarda nata sallan ta zauna akan sallaya tanata addu'oi,
Umma ce tasake dawowa ta sanarda ita mai martaba zai shigo dama da hijabinta jikinta sauya wajan zama kawai tayi, Umma ce tayi masa iso yashigo da sallama Sawwama ta amsa murya kasa-kasa yashigo kai tsaye yayi kan Yareema saida yayi masa addu'oi yaduba jikinnsa sannan ya juyo ya zauna a sopa dake dakin Sawwama ta gaidashi kanta yana kasa ya amsa yana tambayarta jikin yareema tace "dasauki,
Sun dauki tsawon lokaci ahaka mai martaba yakara mata yan nasihu sannan yace "aduk lokacinda kuke zaune kada bakinki yagaji da tofa masa addu'oi kuna zaune kiyita fadin
"*HASBIYALLHU LA'ILAHA ILLAH HUWA ALAIHI TAWALKALTU AHUWA RABBUL ARSHIL AZEEM*
*A'UZU BIKALIMATILLAHI TAMMAH MIN KULLI SHAIDANIN WAHAMMA WANIN KULLI AININ LAMMA*
Ki lazimci karanta *A'UZU BIKALIMATILLAHI TAMMAT MIN SHARRIN MA KHALAQA*
*LA'ILAHA ILLAH ANTA SUBUHANAKA INNI KUNTU NIMAL THALIMIN*
In sha Allahu Allah zai dubemu sannan sai yaye mana damuwarmu,
Sawwama kanta yana kasa tace "in sha Allahu yacigaba da bata addu'oi na tsari dana kariya,
Ya dan dade a wajan Sannan yayi sallama yatafi,
Advertisement
Yana tafiya Sawwama tahau yin addu'oin tana shafa masa dama tunda can ita bakinta bamai zama shiru bane idan tana zaune toh akwai abunda takeyi acikin ranta kamarsu *Istigfari, Su Hasbunallhu wani'imal wakeel, La haula wala kuwwata illah billah*
Har akayi la'asar Yareema yana wannan baccin yanzu kuma abun yafara bata tsoro dan bata tana kallon baccin nasa hakaba,
Tayita kokari ko zai tashi amma ko motsi bayayi idan taga haka zai takoma ta zauna tacigaba dayi masa addu'a."
———————————-
Cikin week din Sadam ya shirya dawowa kasarsa akaro nafarko bayan wasu shekaru,
Hafsa ganin dagaske tafiya zasuyi su barta ya sanya itama tace binsu kawai zataje,
Abida kuwa cike takeda zumidi dan rabonta da gida itama tun tahowarsu da Sadam banda aurensa da Hafsa ma da wayartama kwacewa yayi,
Kowaccensu na ciki na ciken kawai amma ita Abida dake bata iya boye abunda yake cikinta sai ta fiddoshi haka yasa bata iya boye damuwarta dake ciki na dawoda Sawwama dayace zaiyiba tasan irin sonda yake yiwa Sawwama bata nanma bata isheshi kallona bare kuma ace yanzu tadawo,
Tanada yakini cewa idan yanzu Sawwama tadawo toh zaiyi mata soyayya ne fiyeda yanda yayi mata abaya zai riketa gam kuma ba mummy ba koma wacecce bazai yarda tasake rabashi da itaba,
Ita dai wannan lamari sam baiyi mata ba tafiso ace yakaro wasu matan da ya maido Sawwama,
Sun gama shiri tsaff lokaci suke jira suyi airport domin tashin yamma zasuyi,
Yana zaune adakin Abida amma hankalinsa yana can gida gani yakeyi kamar lokaci bazaizoba yakoma yaje aiwatarda abunda yakaishi, yasake duba agogo akaro na ba dadi mtsww yaja tsaki ya furzar da wata iska yana karkada kafa,
Abida da fitowarta daga wanka kenan ta tsaya tana kallonsa cikeda takaici,
Kasa karasawa gaban mirror tayi ta nufoshi saida tayi magana kafin yasan da isowarta, yana kallonta daureda towel yace "me kikeyi anan da bazakije ki shirya ba?karki bata mana lokaci, tabe baki tayi tace "saura awa biyu harda rabi kafin jirginmu yatashi idanma kayi hakuri lokaci zaizo amma cikin kwanakinnan duk wanda yaganka sai yaga wani zumudinda kake ciki ita kanta waccar uwar kwainanayen bata isheka kallo ba,
Zaunawa tayi gefensa ta canja murya tace "Sadam dan Allah kafasa zance dawoda Sawwaman gara ga auro wash matan daban,
Wai na mamajo kika maida nine abida? Kullum zancenki na auro wasu matan daban ance miki ra'ayin kainane tara mata kema sanin kan,,,, daga masa hannu tayi cikeda takaici tace kafada yafi sai arba'in dan haka banada bukatar ji, kai kanka kasan idanma yanzu kana kokarin kamanta adalci a tsakaninmu tana zuwa zaka daina ka canja gabaki daya saboda kasmau abunda kakeso dama abunda kake fada shine katara mata ata dalilin rashinta, kaga kuwa kdan tazo mundawo hoto,
Sadam yayi shiru yakasa bata amsa dan yasan a wannan karon kam dole saiya danni kansa ayanda yake jin daukin Sawwama idakuma ba hakaba toh za'ayi babu dadi tsakanin matansa,
Mikewa tayi ta isa mirror ta shafa mai sannan ta shirya ko kallonsa batayiba yaja trolley dinta tayi gaba,
Bude dakin hafsa tana zauna akan bed ta alamu tagama shiryawa jiransu kawai takeyi, yana kallonta itama ya fahimci tana cikin damuwa,
Sake murfin kofar yayi ya karasa ciki ya zauna gefe ta cikin sigar lallashi yace "amaryata ne yake damunki haka?
Hmmm nikam aina kusa sauka a wannan matsayin tunda ga wata amaryar zakayi, yayi murmushi dan yasan kishi ke dawainiya da ita yace "Au na manta ashefa yanzu itace zata kasnace amarya toh nacanja uwargida, tabe baki tayi tatashi cikeda damuwa zatayi waje hannunsa ya sanya yakamo hannuta ahankali ya jawota tadawo baya akan cinyarsa ya daurata, ya sanya bakinsa a dai-dai wuyanta ta lumshe idanuwa, a hankali yafara magana "Hafsa karkiyi kishi da Sawwamaty idan kikayinin haka bazanji dadi ba,
Sawwama tanada kwayun hali zakiji dadin zama da ita, nisawa tayi cikeda damuwa tace "amma fa sonda kake mata yayi yawa kaduba kaga kwanakinan kowa yaganka sai yasan kana cikin nishadi,
Kimin afuwa sannan kimin uzuri akan Sawwama nafara sanin menen so kaddara tazo ta rabani da iga bawai dan nadaina sonta ba na hakura da ita yanzu Allah yabani damarda zan maidata dole nayi farin ciki,
Sawwama nada kyawun hali sosai itace macenda nasan menene so akanta mun dauki tsawon lokaci muna tare da zancen aure amma haka Allah ya rubuta abida zan fara aura koda na sanarda ita bata kullaceniba bare ta kullaci abida,
Kinga batada hayaniya sam tanada halaye masu kyau zakiji dadin zamada ita har indai baki bata mastsalaba inada tabbacin bazaki samu matsala a wajanta ba,
Jikinta yayi sanyi sosai har kunya taji toh meyema abun kishi da Sawwama bayan wajan mijinta zata dawo?
Amma ai dole tayi kishi tunda tana sonsa kuma tanada masaniya akan sonda yake yiwa Sawwama,
Nisawa tayi ta turo baki tace "amma fa karka manya kayimin alakawarin zaka bani twins na rikesu,
Sadam yayi shiru kamar mai nazarin wani abun sannan yabude baki yace "eh toh nayi alkawari zan bakisu amma yanzu tunda mahaufiyarsu zata dawo saina shawarceta tukunna dukda nasan bazama tahana ba sai abaki hamdan saboda saboda zakubi jituwa dashi dan yana bawa mahaifiyarsa ciwon kai saboda ita batason hauaniya, Hakeeda kuma kamar yanda na fada miki batada maraba da mahaifiyarta hattada kamanninsu da halayensu,
Uhmm kawai tace sannan ta mike tana fadin "muje time, a falo sumu Abida tacika tayi famm danma yayi mata dokaciya akan kada takara shigo musu daki idan suna ciki komai zatayi tajira har sai sun fito, kuma ranta yana bace sam batajin yin laben shiyasa bata labe danjin abunda ya zaunarda suba, suna fitowa fuuu tafice tayi waje."
taxi suka kira ta daukesu har zuwa airport, suna isa bata sukabi duk wani matakin daya kamata bada dadewaba jirginsi ya daga."
Saukar cikin dare sukayi Amma dukda haka Sadam bai yarda sun sauka gidan Mummy ba gidansa suka sauka ahakan aka tattare abunda za'a tattare suka kwanta har Allah-Allah yakeyi hari ya waye yaje yaga Sawwama da yaransa."
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
💞
Advertisement
- In Serial9 Chapters
Another Day, Another Quest
Lifetimes ago, a young woman named Vin was summoned from another world to defeat a Demon Lord and the Great Calamity that birthed him. After successfully saving that world by subduing the Demon Lord, she lived out her life there as a celebrated Hero. At her death, the Pantheon, a collection of all of the patron deities of all the many worlds, offered her a place among them. She accepted and thus, she created her own world to watch and protect, and named it Xael. Xael, a world of magic and swords, flourished for centuries, but now... Now, there are signs of a Great Calamity approaching, much like the one that caused her to be pulled her away from her father and sisters so many years before. Unwilling to see her world fall, Goddess Yvinne decides to do the one thing that she can to save her creation, and even herself. Summon a Hero from another world. However, the Summoning did not work quite correctly, and the "Hero" she got? Well...let's just say he's not exactly what she hoped for. This is a story of a nobody becoming somebody, and a goddess remembering what it was like to be a human.
8 194 - In Serial8 Chapters
The Defier of Everything
Kate Lance, the MC of this story is just a human without any speciality or any ability in this world of supernatural. His fate was to suffer endless suffering, his destiny was to live a normal human life but it all changed after a major incident which shook his entire life. He lived a happy life along with his family in the village of Denzu, he had happy and 'normal family'(this is what he used to think about before). He had also a best friend named Keli whom he knew since quite a while. But all this changed when he was betrayed by his best friend and thrown into the endless abyss of the forbidden area of his village. But now after 5 years of time he returned back to his world with his memories in fragments and also it was a span of 5 years for that world only!!! He now wishes to defy everything and destroy his own destiny to end his eternal suffering and create a path for his own. To achieve his goals he is ready to defy everything and everyone, even the supreme laws of life, death and time are not able to affect his destiny and he has become a fate less. Now what had happened in his time of 5 years in the abyss? Was it actually a time period of 5 years?? What has he become after all this time and why has he become a Defier? To know more about this continue to read the novel "Defier of Everything".
8 50 - In Serial12 Chapters
The First King of Beasts
On a normal evening, a voice appeared out of no where to give an announcement all over the world, this same evening was also when Dustin was run over by a car while running way from thugs. Dustin however woke up unharmed, and learned that the world was about to go into ruins basically, and that some humans would be taken away in a few days as 'earth's warriors'. As it would turn out, on the D-day, Dustin is one of those that were taken. But, this might turn out to be an opportunity rather than a curse, as some night before this day, something interesting happened. [System activated][Starting assimilation... Complete][System online][Congratulations player for being the first to awaken. Rewards will be given] .. To continue reading future chapters: https://www.webnovel.com/book/the-first-king-of-beasts_22850494105573905
8 247 - In Serial591 Chapters
Retribution Engine/Sturmblitz Kunst [Ultraviolent Martial Arts Progression Fantasy]
"The War of Fog is over. Every major city is under occupation. Now we prepare to take back our home." - Unknown Soldier The continent's great heroes have slaughtered one another for the ideals of their countries, but the world keeps moving. The industrious nation of Ikesia lays still smoldering from the nigh-apocalyptic War of Fog, yet it stubbornly forges onward, shielded from further invasion by the impenetrable Blackwall. Its leader - the Sage of Fog - has disappeared, yet his influence is still felt everywhere, his plans and contingencies still in motion - even the Blackwall is said to be his last, desperate creation. New heroes have begun rising from the war of fog, and there is more need for them than ever. A towering foreigner has emerged from the desolate Exclusion Zone. She strides into the war-torn country without the intent to pick sides, but is soon forced to do so when the machinations of malevolent occupiers collide with her own ego. Disclaimer: Retribution Engine and its sequel, Sturmblitz Kunst, are original works and are no way associated with, to, or sourced from existing copyrighted material. The story, all names, characters, and incidents portrayed in this production are fictitious. Copyright: This fiction and all associated works, artwork, fanfiction, derivative fiction, world building, assets, and anything that could conceivably be considered sourced from or created as a result of this fiction are the sole intellectual property of the author, herein known as Akaso. This work and all above terms are © Akaso 2022.
8 118 - In Serial4 Chapters
LOST
Alyson Stewart, rich English girl, gets stranded on a desert island after the ship her family was on sinks. What will happen to her and her brother? Will they survive?
8 100 - In Serial7 Chapters
seven deadly sins...or eight deadly sins. wolf sin of shyness(complete)
Serena Luna is a wolf shape-shifter. She was a mysterious eighth member of the deadly sins. When the sins were framed for the murder of the Grand Master she disappeared into the mist. Ten years later she walks into a tavern called the Boar hat. She instantly recognizes captain Meliodas. when he sees her wolf ears and tail he realizes that it's her. He introduces her to Elizabeth and hawk. They head out find the rest of the sins. Including Serena's long time crush who gave her the nickname Wolfie. His name is Ban, the fox sin of greed.All original characters from seven deadly sins belong to their rightful owner.
8 139

