《ƘADDARAR RAYUWA》K page 100
Advertisement
*ƘADDARAR RAYUWA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa
#Follow me on
"
Marubuciyar
*BIBIYATA AKEYI*
* Y'AR FARI*
* YARIMA FAYAD* paid 200
page 100
Tana tashi daga kan dining din shima yatashi yabi bayanta umma wacce take kallonsu gabaki daya ta sauke ajiyar zuciya tausayi suke bata gabaki dayansu kowanne su rayuwarsa tazo cikeda kaddarori baga Sawwama Ba haka shima yarima kowanne su da kalar tasa kalubalen da ya fuskanta arayuwa sai dai tana fatan wannan wanda yawuce yazamana shine kalubale mafi wahala a cikin rayuwarsu dan bata fata nan gaba su fuskanci wata kaddarar makamanciyar wannan dukda dama ita rayuwa ba'a rasata da kalubale,
dan Adam akowenne lokaci akwai kalar kaddara da Allah kan jarabceshi da ita sai dai ayi fatan idan zatazo tazo da sauki, afili tace "Allah ya saukaka muku duk wata kaddara da zata biyo bayan wannan a cikin rayuwarku, Ummi dake zaune gefe ta na dama tace "Amin jiki a sanyaye,
Harta isa kan kujerarda ke falon ta zauna sannan yashigo ya sameta da sallama ta amsa batareda ta kalli kofar shigowa Ba,
Zama yayi a kujerarda take zauna dake ta zaman mutum biyu ce yayi shiru itama tayi shiru, Hafsa yakira sunanta wani iri taji yayinda taji muryarsa ya kira sunanta yanayin yanda Abubakar yake kiranta, hatta yanayin su komai nasu daya sai dai wasu yan bambamce-bambamce da baza'a rasaba, kuma shi yafi Abubakar yarinta sosai shekarun dake tsakaninsu da rata,
Kasa dagowa tayi ta kalleshi amma gabaki daya nutsuwar ta na tattare dashi, hatta da saukar numfashinsa tana iya jiyowa,
Tayi kasa da kanta ta zubawa hannunta dake kan cinyarta idanuwa kamar mai son gano wani abun ganin yanda take kallo yasa a hankali ya kai hannunsa kan cinyar tata yanda nata hannun yake ya rike cikin sigar lallashi yake shafa hanun nata da babbar ya tsar sa,
Dauke idanuwanta tayi daga nan hannnun nata saita kalli gefe shikuma so yayi ta kalleshi amma hakan ya gagara,
Mai yasa bazakici abinciba? Ya jefo mata tambaya,
naci tabashi takaicecciyar amsa,
Numfashi kawai ya furzar ganin batada niyyar cewa komai ya sanya ya mike yace "bari nayi wanka bai jira cewar ta ba ya shige ciki can jimawa yafito sanye da jallabiya amma wata Ba wacce yake sanye da itaba,
tafara jiyo kamshin turarensa daganan kuma taji fitowarsa,
Sallama yayi mata yanata kallon fuskarta amma taki dagowa haka yayi mata sallama yafice yana fita itama tatashi ta gabatarda sallah."
Waziri zaune gaban Hajiya babba yagama zayyane mata abunda yagani da idanuwansa kallon maras hankali tayi masa kokuma wanda yafara zaucewa
bata kulashi ba amma yanayinta ya nuna tana cikin matsanancin bacin rai,
Fuskarta harta canja izuwa jaa dama daga haka ake gane bacin randa take ciki,
Ganin haka ya sanya waziri ya shafawa kansa lafiya bai sake cewa komaiba, dan babu yanda zaiyine yasanya yakawo mata wannan zance amma da bazai iya tunkararta ba yasan irin tsanar da tayiwa Yareema, wacce hakan yasan ta gwammaci taganshi yana azabtuwa da jinya akan ace ta kasheshi, (karshen kiyayya kenan)
Waziri nazaune awajan har wajan awa guda
sannan aka fara kiraye kirayen sallar la'asar, sai alokacin
Hajiya babba tayi magana da fadin "tashi kaje inaso bayan an idarda Sallah kadawo inaso ka shaidamin cewa abunda kagani bahaka bane domin hakan bazai taba yiwuwa ba, bana fatan ganin wannan rana, tayi shiru sannan ta nisa tace"
Wannan shirmen magana da kayi kawai ka cancanci hukunci mai tsanani, bana tunanin zan iya yafe maka ko ragar maka a wannan zancenda kayi yau,
Waziri cikin kidima yamike ya fice sai fiffike idanuwa yake yi domin yasan halin Hajiya babba tsaf zata iya hucewa akansa,
Advertisement
Yana fita Hajiya babba ta rakashi da harara yakamata tazo ta sauke waziri akan wannan aikin ta daura wani daban domin kwana biyu yana bata matsala tsufa ta fara cinmasa toh amma idan ta saukeshi kan wannan aiki waye zata daura mai amana wanda yafishi?
Akwai wanda zata yarda dashi kamar yanda ta yarda da waziri kuwa? Numfashi tasauke mai nauyi sannan tamike tashige ciki zuciyarta cunkushe da damuwa."
——————-
Sawwama na zauna shiru babu abunda takeyi hakan yasa ta lalubo wayarta ta matsa lambar Mama , bugu biyu mama tadauki kiran Sawwama tayi sallama mama daga can wajanta ta amsa,
Ta gaisheta ta amsa tayi iya kokarin ta wajan ganin ta danne duk wata damuwa da take ciki kar mama tagane, amma saida ta fahimci wani abun sai dai bata tambayeta damuwarta ba saboda tasan zamanda zatayi yanzu zamane da sai tayi hakuri, hakuri na gaske,
Amma duk da hakan bazatayi kasa a guiwa wajan kwantar mata da hankali ba,
Takira sunanta a sanyaye tace "Hafsa, Na'am mama Sawwama ta amsa cikeda son boye damuwarta, mama cikin lallashi da kulawa tace "kiyi hakuri wannan karon zakiyi hakuri ba irinna baya a, sai kinyi hakuri matuka, domin al'amura ne su ma bambamta, Wannan da wancan zaman basuyi kaman cece niya da juna ba, wancan zaman kinsamu soyayyar mijinki amma baki samu ta danginsa Ba wannan kuma mijinne gashi batareda Kinsanma cewa zai soki ko A'a zaisan ki wata rana ko kuwa bazai sanki ba har abada,
mudai muna masa fatan samun gamsheshhiyar lafiya mai daurewa,
Sawwama bata katse mama ba saida ta kai aya sannan ta shaida mata samun lafiyar Yareema Sannan. Ta daura mata da wasu abubuwanda duka faru akai, amma koda wasa bata kawo zancen fyadenta acikiba dan wannan SIRRIN ta binneshi a cikin ranta har Abada bata fatan ranarda zata budi baki ta sanarwa wani ko wata ,
Duk da tasan iyayenta zasu fahimci zancen amma tasan dole bazasuyi dadi ba,
Mama
tayi murna sosai dukda tasha mamakin wannan lamari tsoro ya shigeta tasan akwai marassa tsoron Allah dayawa a duniya wanda basu dauka akwai Hisabi bayan mutuwa ba,
Kuma ta tsorata da wannan masarauta dan haka tayita mata nasiha sai asan nan taji nauyin dake kirjinta ya sauka sai dan nan tasake sukayita hira aka bawa kannenta dasu Hameeda da Handam dama tana kewarsu dan haka sun dade suna hira sannan sukayi sallama saita kira haleema nanma sun dade bayan sunyi sallama sai takira hajiya itama tabawa muhammad yanata yimata maganar su ta yar a haka taji sanyi sai ana kiran magrib sannan sukayi Sallama,
Dake akan sallayar take da alwalarta ta tashi tayi Sallah sai da akayi isha'i sannan Umma taturo kiranta sukaci abinci wannan karon tadan sake taci ba kamar datsu ba kuma dukda kasancewar baya wajan tunda yafita sallar la'asar bai dawoba sai wajan 9:00pm yashigo lokacin Sawwama harta yiwa su Umma sallama tashige ciki,
Sai taji gabaki daya tafi sakewa idan bayanan bata taba jin nauyin Wani abu kamar yanda takejin nauyinsa ba ko fuskarsa bata iya kallo,
Tana shiga ciki ta wuce toilet kai tsaye ta cire kayan jikinta ruwa mai zafi sosai ta zuba cikin bahon wanka dake toilet dama akwai turaruka na wanka wanda tasamu a toilet din da wanda tazo dasu duka ta zubasu nan danan toilet din ya dauki kamshi, tashiga ciki ta kwanta fuskarta kawai tabari a waje ta lumshe idanuwanta zafin ruwan yana ratsata tanajin wani dadi cikin jikinta, tunanin Al'amuran duniya tashiga ba tadade a ciki batasan ta dade ba tana duniyar tunani saida ruwan yafara hucewa Sannan tatashi ba tayi wankan sabulu ba saboda kamshin yarigada yagama ratsa jikinta, tafito daga cikin ruwan tanufi wajan towel, gabaki daya towels dinda suke cikin toilet din ankwashesu sai yan kananu wanda bazasu rufe mata jiki yanda takeso ba ala dole tayi amfani dasu dan babu yanda ta iya domin bazata iya maida kayanda tacire ba,
Advertisement
Haka tadaura tafito yanda hankalinta yake kwance ma babu kowa a dakin dan haka ta daura tafice tana fita ta taka zuwa bakin gado ta zauna ta zantsame jikinta da wani towel din tatashi saita ta janyo lotion dake kusada ita akan dressing mirror ta fara murzawa jikinta a hankali cikin salo,
Yareema dake zaune da adaya daga cikin kujerun dakin wanda tun shigowarta bada dadewa ba shima yashigo Dan tana barin falo su umma yashiga Umma tace yanzu kuwa tatashi bai tsaya a shima yayi musu saida safe yashigo ciki, yana shigowa yayi arba da kamshin turaren wanka ta daya cika dakin, kamashin ya kashe masa jiki yasanya yakasa motsawa daga kujerarda ya zauna bayan shigowarsa domin ya saukar Masada kasala, dama shi duk duniya babu abunda yake daga masa hankali irin kamshi, nandanan saiya rikice, yana zaune kusan 40minute yaji fitowarta yana bude idanuwansa suka sauka akan kyakkyawar surarta yakasa dauke idanuwansa harta zauna ta fara shafaman sai yakeji kamar wanda take murza man da gayya Kamar wacce takeyi da nufin ta daga masa hankali a hankali yake hadiyar yawu itakuwa Sawwama batamasan yana dakinba tacigaba da shafa manta alokacin daya sauke towel din kasa zuwa cikinta tana shafa man saida ya runtse idanuwansa,
Alokacinda ya bude su harta gama shafawa ta tashi izuwa ma'ajiyar kayanta inner wears ta dauko tafara sakawa caji ta tsaya domin tun fitowarta daga wanka taji dakin yadauki kamshin turarensa gabaki daya bata kawo komai aranta ba dayake dakin ya rigada ya amshi kamshi ya rike koda yaushe yana akwai kamshin sai yanzu tunaninta yabata cewa sai idan yana dakinnne kamshin yake yi kamar haka dasauri takai kallonta kan kujerunda suke dakin aikuwa idanuwansu ya sarkafe cikin na juna,
Tsawon sakonni sai kuma tayi saurin kauda kanta gefe takare kirjinta da tafukan hannuwanta, murmushi kawai yayi yamike tashige toilet ta sauke ajiyar zuciya,
sauri-sauri tagama shiri tadauki abun ruhuwa ta isa kan babbar kujerarda take dakin ta kwanta layi luff kamar mai bacci,
Yafito yaganta ahaka batareda yace komaiba yagama shirinsa na bacci yarage wutan dakin tadawo yar kadan harya kwanta sai kuma yatashi zaune ya fuskanci kujerarda take zaune yace "dawo nan ki kwanta yayi magana kai tsaye domin yasan ba bacci takeyi ba,
Taso ta share amma. Kwar jininsa dakuma nauyinsa da takeji yasa bazata iyaba,
A hankali tatashi tadawo kan gadon can karshen gadon ta kwanta baice mata komaiba shima baice komaiba,
kamshin dake fita daga jikinsa nan danan yafara rikitashi,
Tana jiyo sautin numfashinsa yanda yake fiddashi da karfi sannan da sauri ga dukkan alamu bayajin dadi daga bayama sai taji yafara juyi akan gadon daga baya bacci ya dauketa batasan yanda ya kaya ba,
ba ita tafarka ba sai tsakar dare taganshi kan sallaya yana Sallah batayi motsi yanda zaisan tatashi ba haka tacigaba da kwanciya can taga ya mike yafita jimawa kadan yadawo da lemon tsami da ruwa mai zafi a kofi ya matse lemon cikin kofin yafara sha ahankali harya shanye sai can ya dawo ya kwanta duk tana ganinsa amma dayake dakin akwai karancin haske shi bai lurada cewa idonta biyu ba,
Kwanciya yayi tana jiyoshi yana addu'oi bayan yagama taga ya nufeta rufe idanuwanta tayi dasauri sai taji ya shafa mata addu'ar sannan yakoma ya kwanta,
Da asubahi kafin yafita masallaci ya tasheta sannan yafice bashi yadawo ba sai da gari yayi haske Sosai itama ya sameta akan sallaya kujera ya nema ya zauna kusa da ita bayan tagama zikirotinta kanta yana kasa ta gaisheshi ya amsa cikin sakin fuska yana kallon fuskarta yanaso ta kalleshi amma taki gefe take kallo,
Mikewa yayi ya isa gado ya kwanta sannan itama tabi bayansa ta kwanta agefen gadon,
Basu suka tashi ba sai karfe goma ita tafara tashi tafara yin wanka shikam dake bai samu bacci jiya da dare ba shiyasa harta fito tagama shiri ta ta zauna sannan yatashi,
Umma ce ta aiko kiransu su ita tafara fita shi saida yayi wanka sannan yabiyosu yauma kamar jiya kasancewarsa awajan ya sanya bata sake taci abincin ba sosai ya lurada hakan bama shi kadaiba Umma ma ta lura idan yana wajen ne bata sakewa."
Jiya Da dare kuwa bayan an idarda sallar isha'i lokacin Hajiya babba nata jiran waziri shikuma waziri tun kafin magrib yawuce gida saboda Yanaji kamar jininsa yahau yana zuwa gida kuwa ya yanki jiki
yafadi sai asibiti akayi dashi likita yayi yan dube-dube sannan ya tabbatar musu da jininsa yahau sosai kuma Yanzu haka yasamu mutuwar barin jiki ko magana baya iyawa harcensa ya zazzaro yacika bakin,
Tsatsar tashin hankali ne ya sanya waziri yasamu mutuwar barin jiki samun lafiyar Yareema, ga Hajiya Babba baisan wani irin hukunci zatayi masa ba, yanzu haka baimasan yanda yakeba,
Hajiya Babba kuwa kowa labarin halinnda ake ciki afada yake kawo mata itama tashiga tashin hankali zance dai ya tabbata abunda take tsoro,
Itama saida jininta yayi samada dari biyu,
Mai martaba yayi iya bincikensa wajan ganin yagano mai hannu a lamarin Yareema amma abun yaci tura, shidai akwai wanda yake zargi amma haka kawai bazai fito tashi daya yace su bane bayan bayi da wata kwararriyar shaida da zata nuna cewa sune dan haka yayi hakuri ya fawwalawa Allah komai domin yasan koma wanene yakeda. Hannu Allah zai hukuntashi idan bai hukuntashi a gidan duniya ba tabbas zai samu sakamako abunda ya aikata a lahira.
Hajiya suwaiba haka taji wannan labari kamar saukar aradu wai Yareema yasamu lafiya, daganan tashiga firgice saboda tana tsoron kada agane wacce tayi masa a hukuntata ko yaranta,
Hajiya Babba tarasa ta ina zata fara kamo bakin zaran gashi labarin rashin lafiyar waziri ya risketa, taji tsoro sosai domin tunaninta abunne ya dawo kansa sai kuma taji sanyi data tuno cewa waziri keda Al hakin girbe duk wani abunda suka shuka ko wace shirka shi take sakawa yayi shiyasa da abun yatashi tafado kansa abunda bata saniba shine shi Allah ba'a masa wayo ko dabara ta iya kasa cewa daurin talala yakeyi mata,
kuma duk wata hanya da zatabi dan ganin tasake samun nasara akan Yareema tayi amma Allah ya rufesu su kansi wanda take aika suyi mata shirkan dayawa daga cikinsu sun juya mata baya ganin abunda yafaru da waziri."
Amma har izuwa yanzu cikin ranta bata risina ba dama take jira,
har yau tanada burin taji tayaya yareema yasamu lafiya amma bata samu ba domin babu wanda yasan cewa yareema yaada aure agabaki daya masarautar sai yan tsirarru amintattun mai martaba, wanda suma bai shaida musuba har saida Yareema yasamu lafiya,
satin yareema uku da samun lafiya amma har yannzu Sawwama taki sakin jiki dashi hakan kuwa ba karamin damunsa yakeyi ba,
gashi Allah ya jarabceshi da sonta mai tsanani acikin zuciyarsa,
kullum dare sai taga yasha lemun tsami da ruwan dumi tun bata fahimta ba harta fahimci abunda yakeyi dashi, tausayisa takeji matuka amma nauyinsa da karjinsa ya sanya takasa sabawa dashi,
ranar tana zaune yazo yakarbi passport dinta itadai baice mata ga abunda zaiyi dashiba haka itama bata tambayeshi ba."
Bayan kwana uku kawai yace tashirya zasuyi tafiya tashirya da murnarta domin itama tagaji da zaman waje daya,
garinsu suka fara wucewa suka sauka gidan Hajiya dake bayan ya warke yajiya tazo tadubashi basu kwanabaa suka koma,
daga nan yakaita gidansu yace kwana 2zasuyi saisu wuce."
———————
Sassafe yana tashi yayi wanka cikin farareem kaya, kayanda Sawwama takesoo kenan takance idan yasaka fararen kaya suna masa kyau,
shikansa yana kallon kansa yanajin dadi baya jimawa yake sake murmushi,
yariga duka matanatashi saida zai fita sannan ya tashesu ya sanar dasu duka cikinsu babu wacce zata bishi dan haka yasa kai yafice Abida kanma da tsaki tabishi hafsa tazauna tayi tagumi irin wannan rawar kai tayi yawa itadai tasan zasuji ajikinsu idan Sawwama tadawo,
agidan su Mummy yayi breakfast domin yaje kena suna shirin farawa yazauna sukayi dashi iyayen nasa sunyi murmar ganinsa sosai,
suna gamawa yace dady su tafi dady yace "mubari dai zuwa 12:00pm sadam yanz yayi safiya dayawa, Sadam yace "dady yana fita kasuwane gara mutarddashi yanzu, tabe baki mummy tayi rawa kan Sadam akoda yaushe na dabanne idan akan wannan yarinyarce har gobe batason Sawwama aranta tsanarta tana nan kuma ita ba'a son ranta sadam zai dawo da itaba kawai dai babu yandata iyane kuma tun wancan lokacin tayi alkawarin bazaisake nuna yanason abu tanuna bataso ba sai dai Sawwamarce bataso amma dukda haka bazata hanashiba, dan azalzalarda Sadam ke yiwa Dady dole saida ya shirya suka fita Sadam sai yaga sunnufi wata anguwa daban ba wacce yasani ba shiru yayi yana tunanin ko dady zai biya yadauki wani abokinsane, bayan anbude musu gate sun shiga Dady yafitowa yacewa Sadam yafito."
kuyi hakuri kwana biyu kunjini shiru wallhy exam nakeyi har yanzu haka bawai nagama bane kuma final exam ne kawai nasamu nayine saboda kar shirun yayi yawa dayawanku kuma bakusan cewa ina exam dinba,
in sha Allahu idanna gama zakujini akai-akai bazan tsaya a har sai mun kammale littafin tunda yazo karshema."
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
Advertisement
- In Serial131 Chapters
Wandering The Multiverse! Saving The God?
“Ah, when did things get mixed up this much. Damn that Deaf God couldn't even send me to the right world. Why was I even reincarnated in a world that I have no understanding of?! I asked him to reincarnate me on a TV show which I actually knew about and was a fan of! Damn, now how will I live in this world? All I do is wander in Multiverse. Mostly Anime Worlds I heard, but I never watched. Now I have to visit all of those worlds, with my intelligent system, named The Crow. He guides me and helps me, but there is more to it. When I was getting stronger, all of the sudden I targeted by a group called Templars. As I later found out they also traveled from other world and come to the same world to learn strong techniques, so their God, can be more efficient in the next Annual Universal God Tournament. I was at beginning of my journey and oblivious to the worlds I visit. My intelligent system was keeping me in dark. Do I also get stronger for the God reincarnated me? Am I chosen?" This is mostly an anime fan-fiction novel. The MC is oblivious to the Anime Worlds he jumps into. The story jumps from one world to other. Some of the popular novel worlds also part of the story. The MC first went to the Naruto World but is presently in the One Piece world. But, he will be back! Next Anime World will be Hunter x Hunter !!
8 92 - In Serial12 Chapters
Morlock
What happens when in modern society, magic is discovered? What happens when the gift of magic is centered around a small percentage of the population? What happens when a kid who despises magic and magicians discovers his talent in magic? This is the story of a youth learning how to make peace with his gift, his past, and his future. As a new author any and all help is appreciated. If you see any mistakes, please notify me about them. Constructive criticism is appreciated. If you think my story sucks, tell me why it sucks. Hope you enjoy my first fiction.
8 113 - In Serial86 Chapters
Sylph Resurgence
Our protagonist Kai has his mother taken away from him at a young age, an act apparently committed by demons. Now, 7 years on, Kai embarks on a new adventure as he begins the new school year at the esteemed Zion Academy in the kingdom of Nirvania, where adventures await him in a world embroiled in tensions which is full of surprises and mysteries at the same time. A month has passed since Night Wing's incursion on the capital of Nirvania, Nirvana. However, that isn't the end of Nirvania's problems, with war against its warmongering neighbour, Miran looking ever more likely than before. To make matters worse, tensions have been stoked between the Sylph Kingdom and Nirvania by the Chaos Legion, the true enemies hiding in the darkness, opening the possibility to a war on 2 fronts. Kai may only be a 2nd Year student at Zion Academy, but the raging storms of this chaotic era spare no one, especially given his close ties to Adeline, the Sylph Princess. Can Kai circumvent the tides of chaos and live to see the end of what is likely to be a 3rd Holy War? Will Nirvania stand strong against its foes, or crumble and be washed away by the sands of time? 2 years had passed since the conclusion of the 3rd Holy War, which was achieved by the combined efforts of the Nirvanian Army, the 10 Saints and Kai's team, which have been affectionately known thereafter as the Rising 8; a group of rapidly rising youths revered as national heroes for their contributions in putting an end to the 3rd Holy War. Moreover, relations between all 4 Kingdoms on the Central Continent, namely Nirvania, Miran, Cameron and the Sylph Kingdom, have reached unprecedented heights, ushering an age of peace. However, danger lies ever closer, with the Chaos Legion staying low over the past 2 years, awaiting the perfect opportunity to rear its ugly head. Even though Kai had trained hard over the past 2 years to master both his demonic and Sylph ancestry, when the battle has evolved from between mortals to that of the seemingly immortal Chaos Generals, can Kai and his fellow Nirvanians rise above the odds with their allies and vanquish the chaos?
8 151 - In Serial42 Chapters
The Life of a Goddess and a Fox in the Cultivation World
In the Wanderer's Realms, where many beings fight to gain more powers and lifespan by breaking through to higher Ranks, a mysterious man sent two unknown Seals in two of the three main Realms. One was found by a masked woman who seemed to hide a tragic past, while the other was directly absorbed in the body of newborn with an Immortal Fox Bloodline. Two beings that should have never met each other, two seals that seemed to attract one another. What will they experience? Adventures, fights, love, pain? Only by reading this novel will you know the answers to those questions. Greetings dear readers! I am Calm Wanderer and I present to you my first novel in the universe I created, the Wanderer's Realms. This story is mostly about the story of Bai Yue and Guang Yang. It will follow how their relationship evolve and how Guang Yang matures from an innocent child to a powerful cultivator. I will do my best to avoid 1 dimensional characters and also to avoid plot holes. The first few chapters will present more and more information on the important characters and set up the universe I decided to write in: The Wanderer's Realms. If you have any questions or advice, feel free to comment. I'll do my best to answer you as quickly as possible. Release rate: For now I'm planning to release 1 chapter on Friday. The average length of the chapters are 3000 words each. Quite lengthy compare to a lot of other novels.
8 184 - In Serial29 Chapters
Trollhunters and Avengers
After the Battle of New York, the Avengers find themselves investigating strange portals appearing in a small town in California. When they drop by, they'll find that the weirdness of Earth is not confined to Loki,HYDRA or aliens from beyond the stars... A crossover with Trollhunters, by Guillermo del Toro. Trollhunters is owned by Dreamworks and the MCU by the Disney Corporation. All characters are the property of their IP holder and no challenge is implied.
8 175 - In Serial9 Chapters
Beyond The Sky
This is not a battle between good and bad, in a realm that defies those things, good or bad were counted on which intention to keep. Ansel Cakara and Maven Kalila once had an encounter between two gods who fight against each other for the greater good. Maven, who was traumatized by the encounter, wrote her experience in a web novel. Ansel noticed it, and then they met and discuss the event. When they discuss those things, something happened. They were transported to another world, where those gods reign. Unfortunately, not only Ansel and Maven were transported, their friends too. Thabit promised if they fight for the greater good, they could be taken back to their world. The problem lies whether which greater good that they have to choose.
8 55

