《ƘADDARAR RAYUWA》K page 103
Advertisement
*ƘADDARAR RAYUWA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa
#Follow me on
"
Marubuciyar
*BIBIYATA AKEYI*
* Y'AR FARI*
* YARIMA FAYAD* paid 200
Page 103
Already sun san address nasu Sadam kafin su isa sun rigada sunyi booking motarsa zatazo ta daukesu ta yanar gizo sun rigada sun tura address din batareda bata lokaci ba suna sauka suka motar ta daukesu tafiyar minti hamsin ce tsakanin filin jirgin da gidansu Sadam Har kofar gidan motar ta ajiyesu suka karasa suka danna bell,
Shiru na wani lokaci suka sake dannawa, bude kofar akayi Hameeda ce Sawwama tatsaya kallonta kawai yarinyar ta girma sosai ga tsayi yanzu tana 7years kenan amma girmanta kamar wacce takai 10yrs, Hameeda ta ihu tace "Ammie da mugun mamaki Sawwama ta juya tana kallon Yareema bata taba tunanin Hameeda zata ganeta ba, Tabudi baki zatayi magana Hameeda ta daka tsalle ta dale ta da murna itama Sawwaman ta kankameta,
Hamdan ne yabiyo bayanta yana dubawa yaga mahaifiyarshi da murna ya karaso yana fadin Ammie, Sawwama cikeda fara'a tace "na'am hamdan amminka ce, cikin nutsuwa ya taho ya rumgumeta Hafsa wacce take tsaya bayansu dan tun kwala ihun Hameeda suka fito tace "kubar Ammintaku tasamu karasowa ciki, hamdanne ya saketa ya riko hannunta Hameeda kam kamar za'a kwace mahaifiyartata taki sakinta,
Yareema kallonsu yakeyi cikeda sha'awa uwar da yaran sai duka suka bashi tausayi,
Suka shige ciki gabaki dayansu suka zauna kan kujera daya daga Itada Yareema Hameeda ta dale cinyarta shikam dama muhammad na makale da Yareema,
Hamdan ne yace Hameeda bazaki sauka ma Ammie a cinya ba kina bata wahala ya kalli Sawwama yace "Ammie ki tureta Sawwama tayi murmushi ta riko fuskarsa tace zo kaima ka zauna kaji bazakuyimin nauyi ba,
Kamar wanda yake jira yazo ya shige jikinta,
Saida Hafsa tayi magana kafin tadago ta dubeta ita harta ma manta da zamanta a wajan, cikeda fara'a Sawwwama ta gaisheta ta amsa itama fuska a sake,
Sai can Sadam ya fito dake shi bacci ma yakeyi tunda bai fita aiki ba baiyi expecting zuwannasu da wuri haka ba,
Saida gabansu su duka yafadi, da suka hada ido karfin guiwa tasamu ta sakar masa murmushi saida yayi ajiyar zuciya sannan shima ya sakar mata murmushi,
Sawwama ta girma ta zama cikekkiyar mace Sawwamat daya sani ya aura a shekara GOMA SHA SHIDA itace tazama haka idanba ace matsayinda take dashi wajansa ya sanya bazai iya mantataba toda tabbas bazai iya gane Sawwama ba,
Daga ganinta zaka tabbatar tana rayuwa cikin jin dadi mai cikeda kulawa da tarayraya, yanzu Sawwama matar manya ce tabbas domin idan wanda baisan Sawwama ba yanda ta juyo ta rikide baza'a taba cewa tunda can ba cikin dukiya aka haifeta ba,
Ya karaso ya zauna gefen kujerar Yareema yabashi Hannu sukayi musabaha,
Bayan sun gaisa ta kalleshi tasakawa zuciyarta dakiya tace "Yaya sadam ina wuni?
Lafiya Alhamdulillahi yafadi alokacin yake kamo hannun muhammad wanda hankalinsa yake kan yan uwansa da suke jikin Amminsa,
Muhammad yaje jikinsa yanata yimasa wasa,
Advertisement
Jin hayaniyarda tayi yawa ya sanya Abida fitowa dan ganin wanda sukaso dafarko bata gane Sawwama ba saida ta isa wajan gabanta yafadi ganin Sawwama tsabar idanuwanta ya rufe bata lurada wanda yake gefen Sawwama ba ta yatsine fuska tafara zantuka, tace "toh wajanwa kikazo kuma? Bayan naji labarin kinyi aure? Aurenne ya mutu kokuma mijinne yasake mutuwa?
Sawwama tayi murmushi mai cikeda takaici tace wajan Wajan Yarana nazo,
Tabe baki tayi tace "koh wajan uban yaranba,
Siririn tsaki Sawwama taja tace "ko wajan ubansu nazo ai ban fadi ba,
Ranta yafara baci tadubi Sadam tace "Yaya sadam har yanzu wannan bata daina halinta ba?
Yaya kake iya zama da ita?
Zata sanya maka ciwon zuciya,
Sadam ya sunkuyarda kai kawai yarasa mai zaice shikma baisan wace irin mace bace Abida,
Gidan ubanwa zai kaini da kike gaya masa wannan maganganun?
Afusace Sawwama ta sauke Hameeda dake gefentata cafko hannun Abida tayi hanyar waje,
Babu wanda yayi kokarin yin magana bare asamu mai dakatarda ita,
Ita kanta Hafsa kallon ikon Allah kawai takeyi ashe karamin kishi Abida keyi da abida, bata taba kallon tasantsan kishi a fuskarta ba irinna yau dataga Sawwama,
Suna kaiwa waje Sawwama ta banko kofa ta rufe babu mai iya jiyosu ko ganin abunda sukeyi,
Sawwama tasaki hannun Abida data biyota kamar rakuma, cikeda bacin rai tafara magana tace "Ashe har yanzu kina wannan halin dabbancin naki?
Wai sai yaushe zakiyi hankali? So kike kisa sakawa Yaya sadam ciwon zuciya?
Abida zata kuntuma mata Ashar tayi saurin dakatarda ita tace "A'a yanzu ba daa bane ki iya harshenki, koda wasa, yakamata ace yanzu kiyi hankali kisan cewa na girme miki a tsara,
Ba wannan ba abunda na jawoki na fada miki kashesi jan kunne dakuma shawara yakamata ace yanzu kinyi hankali kinbar wannan kauyancin,
Da mamaki Abida take kallon Sawwama, Sawwaamarda abaya ko yatsa aka sanya mata bazata ciza ba yau itace take kashedi,
Kuma niba wajan mijinki nazo dukda banace banzo danna ganshi ba saboda inada aurena inada iyalina acan gefe kuma inajin dadin rayuwata, toh Amma babu yanda na iya har indai bazaki canja hali ba bazan iya kallon Yaya sadam cikin matsala ba zan iya kashe auren nazo na aureshi, tunda dama bawai nadaina sonsa bane yananan acikin zuciyata ko kadan bai raguba sai dai kawai soyayyar ta rikide daga da aure zuwa ta yan uwantaka,
Yanzu mijina nake matukar so ammahar indai bazaki canja hali ba banda wani zabin daya wuce na dawo cikinku mu zauna, ke shaidace akan irin sonda nake yiwa Yaya Sadam tunda har zai iya rikidewa yakoma kan wani daban, yanayi zai iya dawo dashi muhallinsa na baya, indawo na rungumi yarana, su girma gaban uwarsu da ubansu amma faruwar hakan ya danganta daga sauyawarki,
(Sawwama tafadi wannan kalamanne kawai saboda tanaso ta samarwa sadam zaman lafiya a gidansa Bawai zan zata iya rabuwa da Yareema ba, eh tabbas dagaske ne soyayyar Sadam bata ragu azuciyarta ba saina tausayinsa daya karu kan soyayyar amma ahalin yanzu ba soyayyar aure takeyi masa ba, Sadam shine jigon duk wani abunda tazama a rayuwarta shine wanda ya daura rayuwarta akan hanya, hakkine akanta itam tayi iyawarta dannema masa zaman lafiya acikin gidansa)
Advertisement
Jikin Abida har bari yakeyi jin kalaman Sawwama gani takeyi kamarma yanzu tazo kashe aurenne ta dawowa Sadam,
Calm down Hajiya Abida bawai kashe auren nawa zanyiba idan kika zauna zaman lafiya dashi nima zan zauna lafiya agidana har Abada in sha Allahu,
Ga mamakin Sawwama sai taji Abida tace "kinyi alkawari? Koda yake ba abun mamaki bane idan akayi la'akari da yanda ta tsorata,
Uhm eh nayi alkawari cewar Sawwama amma zan ringa waya da yarana danjin halinda ake ciki, shikenan nima nayi alkawarin bazan sake tada masahankalinba, kin kyautawa kanki Sawwama tace hadeda shigewa gaba tafara tafiya kai tsaye tabude kofar takoma dake ba'ayi locking dinta ba,
Abida tabiyo bayanta suum-summ zata wuce daki sai tajiyo muryar Sawwama tana fadin kizo kugaisa da mijina dasauri Abida ta juyo suka gaisa tawuce daki,
Kowa yanaso yaji Abunda yasa Abida sanyi haka amma babu wanda ya iya tambaya."
Kudi sosai Yareema ya kashewa twins ya saya musu abubuwan tsaraba kala-kala,
Kwana biyu sukayi agidan amma Abida bata shiga harkarsuba sam abun har mamaki yake bawa Sadam da Hafsa sanin rashin mutumci irinna Abida,
Zamanda sukayi Sadam Ya fahimci cewa Yareema na matukar son Sawwama da abunda ta haifa gabaki daya, yanayin yanda yake tarayrayarta sai yakeji inama da awajansa tasamu irin wannan kulawa haka amma yanzuma bai baci ba zai bawa matansa dai-dai gwargwado danya dauki darasin yanda ake lailaya mace kamar kwai."
Ya lura Sawwama tacire duk wani abu aranta ta dauki Kaddararta ta rumgmi gagarumin sauyin da ubangiji yayi mata,
Suna Hira da Yareema,
Sadam yake ce masa lallai Sawwama tayi sa'ar miji Allah yayi mata sauyi yadubizyciyarta,
Murmushi Yareema yayi sannan yace "nikuma gani nakeyi kamar nine mai sa'ar ba itaba domin ban taba cin karo da mace mai kyawawan dabi'u kamarta ba, murmushi mai ciwo Sadam yayi yace "kuma bana tunanin har Abada zakaji wannan karon,
Sawwama nada kyakkyawar zuciya Cewar Yareema kuma bata manta halaccida bakinta tacemin bazata taba mantawa dakaiba domin kai shigone arayuwarta, a hankali a zamana da ita saida nafahimci wanenen kai,
Nasan cewa KADDARAR RAYUWA ce tazo mukj ahaka amma soyayyar da kuke yiwa junanku banaji akwai abunda zai rabata, tacemin har Abada bazata daina sonka da ganin girmankaba sai dai soyayyar da take maka yanzu tasha bambam data baya,
Eh ai dole zata sha sun bambamta cewar Sadam soyayayrda takemin abaya yanzu tadawo kanka domin ka kwaceta,
Dariya dukansu suka saka,
Haka idan suka zaune sukeyi sun ringa hirarraki kenan,
Kwanansu 5 suka shirya tafiya, Hameeda tayi kuka ba kadanba saida su dukansu sukaji babu dadi babanta yayiwa Yareema Alkawarin ana hutu zai kawosu sannan da zarar Hameeda tagama primary zai basu ita gabaki daya danya lura tana matukar son mahaifiyarta,
Godiya sosai sukayi masa har ita kanta uwar taji dadin hakan sosai,
Haka suka tafi cikeda kewar juna har suka tafi Abida bata sake tada musu rikici ba."
—————-
Tun daga wannan lokacin duk hutu sai Sadam ya kawowa Sawwama twins sunyi hutu a wajanta daga karshe ma yabata Hameeda gabaki daya."
Sun shiga na shekara biyar da aure amma Sawwama shiru,
Ranar ta shirya tsaff tasamu Yareema adakinsa sai dai tana taraddadin yanda zai dauki zancenda taje masa dashi,
Zama tayi gefensa saida yagama karanta shafin da yake sannan ya rufe alqur'anin yajiyo ya dubeta, murmushi ta sakar masa shima ya maida mata, matsonan ki fadamin meke tafe dake dannaga bakinann kamar akwai magana,
Wani murmushin tasake saki sannan tamatso ta kwanta jikinsa tayi kasa da murya tace "ina waccar shekarar da mukaje saudi yace "ehem inaji mai yafaru acan?
Mun hadu da wata sunanta nabila mun gaisa ta ganmu tare dakai shine take cemin itace tsohuwar matarka bayan mundawo sai nake tambayar ruma tabani labarinta tanada kirki sosai ta kula dakai,
Se akayi yaya? Ya tambaya da mamakin abunda Zai biyo baya,
Uhmm dama nace ko zaka aureta idan andace sai kaga Allah yabamu yara ta wajanta, tunda kaga auranda tayi bayan naka bata zaunaba,
Da mamaki yake kallonta yace "Anya! Anya kina sona kuww? Kowace mace na gudun kishiya ke kinaso?
Ni nace miki nadamu da yarane? Wanda nake dasu sun isheni, balle me menene na kara aure? Tunda naga aike kin haihu idanma da matsala ko wajena ne, kinga bbu wani amfani kara auren har indai akan hakanne,
Turo baki Sawwama tayi tace "ina sonka mana kaima kasani wannan sai dai kafada kuma kishiya nifa duk aurenda nayi na zauna da ita,
Shafa gashin girarta yayi yace "toh ni agidana karki zauna da ita sai gidana yafita daban kamar yanda nima nafita daban,
Uhmm kawai tace zata mike ya dawo daita yace ai baki idaba dawo nan, indawo inyi mene bayan kaki jin shawarata,
Bari kiga mai zakiyi yafada yana rumgumota,
Kokarin kwacewa takeyi yace "tsaya mana toh kiga nima na gwada sa'ata shammatarsa tayi ta fauce kasancewar tasan yaran basa gida yau zasusha soyayyarsu yanda ransu yake so,
Tana sauka daga gadon tafara tafiya a hankali shima yabi bayanta yana fadinta tsaya ya gwada sa'asarsa ganin yana shirin cimmata ya sanya ta kara sauri taku uku ya kara ya cafkota rumgumeta yayi da karfi saida tasaki nishi, yace ""ni kike kaiwa kasuwa koh? Waina kara aure toh naki sayuwa kici gaba da zamada abunki haka babu maiso,
Tana kokarin kwacewa tace "kabari kagani idan nayi tallah daka wawa za'ayi dan kowa naso,
Tsayawa yayi yana mamaki wai dagaske Sawwama aure takeso yakara?
Shidai baitaba kallon matarda takeso dan karan kanta ayi mata kishiya ba sai ita, shikuma dai ara'ayinsa baida niyyar auren mata samada daya kuma har yanzu hakan yakeji aransa,
Tana kokarin kwacewa ya dauketa cakk bai ajiyeta ko'inba sai cikin dakin nishi ya tsaya yanayi tana dariya yace "Allah kin kara nauyi sosai,
Uhmm ai gara na kara kar nayita cin abinci ba'asan yanda yake tafiya ba."
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
Advertisement
- In Serial20 Chapters
The Casual
Notice: On hiatus. *profanity tag added just in case a bit of swearing is required, but I'll try to keep it as profanity-lite as possible* RealWorldIII came with the motto "Bringing the imagination back into the gaming" with an innovative skill combination system that promises to create unique (see: not-actually-unique) characters tailored to each player's preferences (see: we-swear-it's-not-random) Alex is a random guy with the motto "Well... whatever" with a history of being at the top of the gaming scene (see: he was a kid back then) that after twenty years of working for daily necessities finds himself facing a tough dilemma: do I go back to being a corporate slave, or do I gain money by playing a game no questions asked? (see: not really a dilemma) The only question is, can an actual "casual", even if ex-pro, survive constantly playing a game? or will he end banging his head on the wall? The story will unfold mainly in-game, with little if any real life events happening.
8 202 - In Serial38 Chapters
Apocalypse on Endless Earths: Apocalypse How? A LITRPG Adventure
Declan Mason is just an average guy who is about to pop the question to the woman he loves more than anything when his whole world gets turned upside down. No, that's not right, it gets crushed, pulped, eviscerated, and apocalypsed to hell before he even realizes what is happening. He suddenly finds himself working for an Extradimensional Entity that has tasked him with committing genocide on a daily basis. As Declan's new job, it seems, consists solely of him eliminating alternate versions of his Earth. Not content to just destroy, he vows to save the woman he loves one planet at a time. Soon, he's up to his armpits in doppelgangers of his dearie, and he starts to get a clue as to why he has to destroy each world. Just to complicate matters the Horseman, the person who held his station prior to Declan taking over, has decided it is up to him to stop the Entity's murder spree and has placed Declan in his cross-hairs. Apocalypse on Endless Earth's is seriously silly and actively adventurous. Can one man learn to destroy numerous worlds in new and creative ways while simultaneously saving copies of the woman he loves? Find out!
8 240 - In Serial11 Chapters
Family business
Blood is thicker than water. The famous one-liner to bond families together, but is it really true? Lo and behold as family dramas occur under the watchful eyes of an old and obscure profession. Jack Crucintum is always interested in entertaining guests.
8 162 - In Serial106 Chapters
Hodgepodge
Hodgepodge is a collection of stories set in a realm where planes fly, immortals walk, people summon weird animals, a rabbit uses a traveling shovel of death, a man and his dog try to change the future, and the underworld decides to send someone to calm things down to stop the flow of the dead. Please enjoy.
8 498 - In Serial36 Chapters
The Summoned Queen[Revamp]
Synopsis Suno Temeria's heritage was of the royal family of the Temerian Empire. With the Temerian Empire annexed by the Kingdom of Toria, Suno, now ex-royalty, is currently the target of hate and disgust in the academy he is attending.However, this did not stop him from being a genius at magic, giving him more options than what he has at the moment. So with his extensive knowledge, he came up with a plan to get a companion to talk to and to help him along the way. He decided to use a summoning spell to do this and what came out of the portal was....“I am the Queen of Toria, Sora Lune what might thee want from me?”"Eh!?!"_______________________________________________________________________________________________This is my first time posting a fiction so please be gentle when you give your reviews on my story and depending on my mood I will have a chapter out. Summary/Synopsis by LordofVoids
8 80 - In Serial42 Chapters
Gallanor (On hiatus)
In the year 2036 the theory of ejection was proposed. Ejection is the process of transferring a persons entire being from one universe to the next closest one. Once done this theoretical process cannot be reverted. Darren Tower the first person to ever eject finds himself in Gallanor a inhabitable world in the Universe adjacent to his own. Unaware that his arrival will set in motion a chain of events that will shake this world and his own to their cores.
8 137

